Showing 135001 words to 138000 words out of 139085 words

Chapter 46 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

dalilin da ya sa ya min haka sai kawai na ji andafa ni, juyowa na yi sai kuwa na ga takwarata, cike da farin ciki mu ka rumgume juna ta na fad'in "Takwarata me ki ke anan?"


Raba jikina na yi da nata na sake kallonta ta yi kyau sosai, murmushi na yi na ce "Na zo biki ne ni ma."


Tsaki naji Abbas yaja hakan ya sa mu ka kalle shi a tare, *Sameera* ce tace "Jarumi na lafiya ka ke tsaki?"


Da k'yar yake maganar saboda miskilanci yace "Kinsan ba na son hayaniya, wannan kuma ta tsaya min a kai ta na zuba kamar 'ya'yan kurna."


Tabbas raina ya b'ace yanda Abbas ya nuna ni kamar ya nuna kashi, tab'e baki na yi na ce "Da ace banga lokacin da ka ke wa takwarata 'yar murya ba da sai ka zare min ido, amma tunda har na ga komai to magana ta k'are, wannan shan kunun duk birga ce wallahi."


Kallon Sameera na yi na ce "Takwara idan kun koma gida lafiya ki gaishe min da su Bashir da su Abba da Mama." Da murmushi a fuskar ta tace "Za su ji aunty Meera."


Har zan wuce na ji Abbas yace "Ta na nan har yanzu yanda take kamar za ta fad'i ta na fama da bibiyar rayuwar mutane."


Wucewa na yi na barshi da takwarata tace mi shi "Ba fa na son haka uban yara, duk abin da za ka fad'a mata kamar ni ka ke fad'awa."


Wani kallo kawai ya bita da shi kamar zaiyi bacci, ni kam ina barin nan na shiga neman mutuniya ta, ai kam bansha wahalar ganin ta ba, da gudu na k'arasa na rumgumeta ta baya ina fad'in "Ohhh, my Hajiata."


D'ago kai ta yi ta kalle ni tace "Lah! aunty Meera, ke ce anan? Me ki ka zo yi wurin nan?"


Saida na taushe zuciya ta kafin na ce wani abu *Umar Faruk* (jarumin littafin *Jihadi*) ya fizgoni na yi baya ya na fad'in " Dallah malam sake ta, me ye haka kin wani zo sai kin karya ta."


Ba dan Umar ne ba da sai na mi shi rashin mutumci, amma saina k'yale na ce "To cinye ta zanyi da ka wani taso min haka?"


A tsaurare yace "Ki yi baya ki daina tab'a jikin matata shine kawai abin da na sani."


Rik'e hab'a na yi na ce "Ikon Allah, beby mijin beby, wato wai kai mai kishi ko? To Allah ya kyauta."


"Ya ma kyauta." Ya fad'a ya na kallo na, *Khairat* na kalla na ce "Hajiata ina *Zubaida* ne? kinsan fa fan's sunyi kewarta."


Murmushi ta yi tace "Ta na gida bata jin dad'i ne, kuma ga tsohon ciki da ke jikinta, shi ya sa ta zauna gida tunda tafiya ce mai nisa."


Juyawa na yi na kalli Umar ina dariya, shi kam sai ya had'e rai ya na harare na, saida na fara takawa na ce "Lallai Umar ba dama, wato har yanzu ka na nan ka na tsula tsiyarka, daga wannan ta sauke wannan za ta d'auka, humm."


Juyawa na yi zan wa Khairat magana amma sai Umar ya ciro takalman shi zai jefe ni, da gudu na bar wajen ina dariyar mugunta, kujera na samu na zauna ina sauke numfashi kamar saukar aradu daga gefena aka ce "Aunty Meera ya ki ke?"


Da murmushi na juyo dan na gane mai muryar, da farin ciki na d'aga mu su hannu na ce " *Falmata* (d'aya daga jaruman littafin *Itace k'addarar mu*), lafiya lau, ya ki ke kema?"


"Lafiya lau, me ki ke anan?" Saida na b'ata rai na ce "Abin da ki ke yi."


*Adam* ne yace "Daga tambayar arzik'i malama sai abu ya zama na tsiya."


Hararan shi na yi na ce "Kai ni rufe min baki dallah ban sa da kai ba."


"Ke ni ki ke fad'awa haka?" Ya fad'a a hassale, ni ma a hassalen na fad'a "Eh anyi d'in, me za ka yi?"


Tasowa ya yi ya nufo kaina amma ban gusa daga in da na ke ba, saida ya tsaya gaba na ya nuna ni da yatsa zaiyi magana na ga an rik'e hannunshi daga baya ance "Haba kai kuwa Adam, aunty Meera ce fa, ba ka gae ta bane?"


Sai lokacin na ga mai magana ashe *Marwan* (jarumin littafin *Kawu na ne*) ne, huci ya yi ya sauke hannun shi ya koma mazaunin shi, har ya zauna a kalli Falmata na ce "Fati wai ina d'an uwan ku mahaukaci?"


Cike da jimami tace "Ki bari kawai aunty Meera, har yanzu ya na can babu sauk'i, wallahi duk ya sauya ya zama mahaukacin gaske."


Tab'e baki na yi karo na farko da na ce "Allah ya yaye mi shi, *Fadjimata* kuma Allah ya mata rahama."


"Ameen." Ta fad'a ta na mayar da kallonta gaban ta, sai lokacin na kalli Marwan na ce "Marwan ina aunty na take?"


Da yatsa kawai ya min ishara zuwa bayana, ina juyawa na ga *Wafa'atu* bayana da tulelen cikinta masha Allah, da farin ciki na mik'e na rumgume ta na ce "Aunty Wafa'atu ashe Allah ya nufa."


Ita ma da farin ciki tace " allah ya nufa Meera, addu'ar ki data fan's d'in ki ta same mu har inda muke, gashi yanzu Allah ya sa nima ina d'auke da cikin wata bakwai."


"Kai to Allah ya raba lafiya aunty wafa'atu."


Da "Ameen." Suka amsa su dukan su, sai lokacin Wafa'atu tace min "Amma me ki ke yi anan? Ke ma Khadija ce ta gayyace ki."


Raina ne ya b'ace da tambayar sai kawai na yi gaba na bar su tsaye, ina cikin tafiya naji anyi magana cikin shagwab'a ance "Aunty Meera shine ko ganin mu ma ba kya yi."


Juyowa na yi sai kuwa naga *Raheenat* (jarumar littafin *K'angin rayuwa*) ce, saida na gama kallon mutanen da ke tare da ita, ita da *Sameera* suna manne da juna haka ma *Abdul hakeem* da *Sadiq* suna jone sai tattaunawa suke, matsawa na yi dan mu gaisa amma Abdul hakeem sai cewa ya yi "Ke me ya kawo ki nan?"


Baki bud'e na ce "Abdul hakeem yaushe ka zama haka kuma? A sani na dai ka na da taushin zuciya."


"Sanin baya ki ka min, ai yanzu abin ba sauk'i, dan haka b'ace min da gani kafin ran ki ya b'ace." Yanda ya ke maganar ya sa na tsora ta na juya zan tafi Sameera tace "Haba takwarata, yaushe ki ka zama mai tsoro ne haka har da wannan zai tsorata ki."


Abdul hakeem ne ya kalli Sadiq yace " aboki na ka sa matar nan taka ta yi shiru kafin na fitar mata da jini a baki."


Kallon Sadiq Sameera ta yi tace "To sa na yi shiru d'in, ina jira."


Wuk'i-wuk'i Sadiq ya yi da ido kafin ya kalli Abdul yace "Aboki na ka yi hak'uri, ba zan iya ma ka komai ba gaskiya, wannan matar da ka ke gani ina tsoron bala'in ta."


Wata dariya Sameera da Raheenah su ka yi harda tapa hannu, ni kam dariya na yi na yi kafin na ce "Wai ina yara na ne?"


"Suna gida." Cewar Raheenat, juyawa na yi na ce "Sai anjiman ku."


Kallon Sadiq na yi na ce "Ka gaishe min da bazawarar nan taka."


Waro ido ya yi ya kalle ni ya kalli Sameera, tasowa yayi zai min magana sai kawai takwara ta jawo rigarshi ya koma ya zauna tace "Dan Allah ya toni asirinka shine za ka bud'e mata ido."


Abdul ne ya kalle ni yace "Kedai anyi guba wallahi, to yanzu dad'in me ki ka ji?"


Kallonshi na yi na ce "Ka mantabi guba ce lokacik da ka ke sawa ina rubuta labarin soyayyarka da sabuwar budurwarka."


Kallon shi Raheenat ta yi ,dariya na yi na wuce gaba ina ganin bala'i ya b'arke tsakanin Sadiq da Sameera, Raheenah da Abdul dan fa ita ta yarda bazawara yake nema tunda a ganinta ina bibiyar rayuwar mutane, ta teburin da Adam ke zaune na wuce nan ma cewa na yi ya gaishe da budurwar shi, a tak'aice saida na bi duka ma'auratan d'aya bayan d'aya ina hura mu su wuta, kuma babu wacce ba ta yarda ba saboda ganin ba zan fad'a mu su abinda ba haka bane, kafin ka ce me wajen taron ya fara d'aukar gumi saboda muryoyin dake tashi sama, musamman Kaussar da Khairat da Sameera ta Abbbas, sosai suka rufe ido wai ana cin amanarsu, da dai abin ya k'i sauk'i sai gashi ina niyyar sulalewa na bar wurin na ji ance "Aunty Meera barka."


Ina juyowa da sauri naga teburin cike da jaruman littafin *Aure*, da farin ciki na k'arasa muka gaisa kafin na kalli matan na ce "Ina yaran?"


*Fatima* ce tace "Suna gida aunty Meera."


Sai *Rauda* da tace "Ai sun fara wayo yanzu." Kallon Laure nayi da kanta ke k'asa duk take jin ta a takure, murmushi nayi na ce "Lauratu sarauniyar kunya, to Allah ya mayar da ku gida lafiya, ni na yi gaba wajen nan ba zai zaunu gare ni ba."


"Me ya sa?" Cewar *Iro*, kallon shi na yi kafin na ce wani abu *Siryanu* yace "Akwai bala'in data had'a tunda kaji haka."


*Imam* ne yace "Ko kuma tsokana ba, kasan Meeran mu da tsokana fa, watak'ila akwai wanda ta harzuk'a."


Ban tsaya saurarensu ba na fece ba su ma san da tafiya ta ba sai gani sukayi bana wajen.


😂😂😂😂😂


Ina shirin hawa adaidaita sahu na ji an shak'o hijabina na dawo baya, wazan gani in ba Umar faruk ba da hijabi na a hannu, Saif da Marwan sune masu sanyin ciki sune suka ce ya sake min hijabi tunda ni ma fa ba kara zube ni ke ba ina da aure, saki na ya yi amma Abbas yace "Wallahi ko kije ki fad'a mu su k'arya ki ke ko kuma mu kwana anan mu da ke."


Ahmad ne yace "Ai ba maganar mu kwana anan bane, magana ce ta muje gidanta a matsayin samarinta ma su son ta."


😂 *Ahmad ko bala'i*


Jin haka ya sa na ce su yi hak'uri mu tafi na fad'a mu su gaskiya dan ina son *beby na* ni ma, haka suka tasoni a gaba na zo na fad'a mu su kawai dan raha ne, saida magana ta fara lafawa sai kawai muryar Usman naji yace "Abokai ku taimaka ku tafar min da matar nan dan Allah, dan nima ta d'an fara damu na, sam bata bari mutum ya yi sirri da matarsa."


Murgud'a masa baki na yi na ce " To babu in da zanje sai na k'arashe labarin har k'arshe sannan."


Cikin fad'a Usman yace "To zan gani idan gidanki ne ko nawa."


"Gidanka ne amma babu in da zata je har sai ta k'arasa abin da ta fara." Cewar Khadija, turo baki yayi kamar zaiyi kuka amma bai ce komai ba, nima cewa na yi "Zan tafi yanzu dai saboda na gaji, amma zanyi sammakon zuwa gobe da safe."


Dukansu hannu suka d'aga min suna min bye bye da cewa "Saida safe Meranmu."


Haka na bar wurin cike da kewar *jarumai na* ko ba komai ina jin dad'in zama tare da su, da haka suma su ka ci gaba da walimar su har aka yanka panke dare ya yi sosai kafin Usman ya samawa kowa makwanci mai rai da lafiya ya kwanta dan huta gajiya, haka duka ma'auratan suka kwanta suna soyayyarsu dan har yanzu akwai wanda basu san sun girma ba.


*Asuba ta gari*


Daga lokacin suka fara jego cike da gata da kulawa, a yanzu idan kaga zaman na gidan Usman saiya baka mamaki, duk da har yanzu suna jin kishi amma dai ba kamar baya ba, haka suke tasa Usman gaba su dinga masa k'iriniya shi kuma yana biye musu, rayuwar ta musu dad'i yanzu kuma sun fahimci zama lafiya yafi zama d'an sarki, a haka rayuwa da lokaci ke tafiya girma na k'ara zuwa musu, Haseenah k'iba take tayi abinta saboda kwanciyar hankali da hutu, amma Khadija har yanzu tana nan yanda take bata rage ba bata k'ara ba, a haka sherau su ka je sosai har shekara *goma sha biyar*.


A wannan shekarun abubuwa da dama sun faru masu dad'i da marasa dad'i, daga ciki akwai rasuwar su malam da Hajia, haka ma mamar Khadija ta rasu sakamakon rashin lafiya, haka mahaifin Haseenah ma ya rasu sai maman su wacce tsufa yasa ko yayanta bata ganewa, da haka kusan dukansu suka zama marayu suna kuma kula da junansu sosai, abun farin ciki kuma akwai haihuwa har biyar da Haseenah ta k'ara bayan Aisha, kuma dukansu mata ne sai auta shi kad'ai ne namiji wanda ya ci sunan *Ali* amma suna kiranshi *Khalifa*, kuma wacce yake biwa ita aka wa Khadija kara aka sawa sunan mahaifiyarta *Sadiya* ita ma suna kiranta da *Nawwal*, hakama hajia an mata takwara *Hawa'u* wacce akewa alkunya da *Noor*, sannan daga ciki akwai kammala karatu da bilal ya yi a k'asar *Canada*, amma har yanzu Khadija bata sake haihuwa ba daga Humaira, amma kaf yaran Haseenah ita ke kula da su kamar ita ta haifesu, a haka Bilal ya dawo ya zama cikakken saurayi son kowa k'in wanda rasa, matashin saurayi kyakyawa kuma miskilin yaro mai d'auke da shekaru *ashirin da bakwai*, hakan yasa Usman damka duk ragamar gidan hannu Bilal, a cewar shi aure zai mi shi nan da d'an lokaci kad'an, wannan damar da Bilal ya samu tasa yake juya komai na gidan har iyayen mata, shi ya sa yanzu kullum gidan cikin hayaniya suke saboda Bilal dai baisan yawan surutu, yau ma kamar kusan kullum Aisha da Humaira ne suka shirya dan auwa bikin k'awar su, masha Allah yan matan Khadija kenan, tabbas shak'uwa dake tsakaninsu tasa har suke kama sosai ta fuska da yanayi, sai dai Humaira tafi haske sosai da dogon hanci sannan tafi cikar hallita da kumari, kayan jikinsu ma iri d'aya ne haka suka nufi d'akin Bilal dake sama dan karb'o makullin mota su bawa drebansu ya kaisu, da sallama suka tura k'ofar Humaira ce gaba.


Kwance yake ruf da ciki babu riga a jikinshi sai dogon wando dake d'aure da d'amara (belt), saida suka tsaya kanshi Humaira tace "Yah Bilal makullin mota za ka bamu mun shirya."


Shiru kamar baiji ba, Aisha ce ta kama hannun Humaira tace "Kinga mu fita wallahi bana so ya tashi ya mana tsinannan duka."


Fizge hannunta tayi tace "Ke wallahi kin cika tsoro, kawai saiya doke mu daga wannan maganar."


Kallonshi tayi ta sake cewa "Ya Bilal magana muke fa."


A hankali ya juyo tare da tashi zaune yana kallonsu, saida ya gama kallonsu yace "Ku rufe k'ofar d'akin sai ku zo ku karb'i makullin."


Kallon juna su ka yi saboda sun san me ya ke nufi da abin da ya fad'a, zare ido su ka fara yi kafin ya sake daka musu tsawa yace "Na ce ku rufe k'ofar ko."


Haba wa ai da gufu suka fita suna rige-rige, Allah ne ya saukesu k'asa lafiya basu zama ko ina ba sai falon Usman, kamar an turosu haka suka fad'a d'akin, kowace wajen ta ta uwar ta nufa wacce tasan zata tsaya mata, Humaira wajen Haseenah Aisha wajen Khadija, wata cakuma da Aisha tawa Khadija yasa d'an kwalinta fad'uwa kan kujera hakan ya bayyanar da yar furfurar dake kan ta wacce ba'a ganinta sosai ma, Khadija ce tace "Kai Aisha ho, wannan ba sai ki karyani ba, lafiya me ya faru?"


Haseenah da sai wani k'ara rumgume Humaira take ne tace "Ai da gani ba tambaya kinsan su da wannan yariman mai gida."


Khadija ce tace "Wallahi al'amarin nan ya fara isata fa, gaba d'aya yaron nan ya hana min yarinya sakewa a gida."


"Ai ba laifinshi bane, laifin wanda ya bashi muk'amin ne a gidan." Cewar Usman daya fito daga d'akin shi tare da sauran yaran sunata gurgurar chocolat, hakan ma yayi daidai da shigowar Bilal ya sanyo farar riga wacce ta kamashi, tabbas ko kad'an Bilal baiyi kama da mahaifinshi ba saboda k'irar jikinshi ma ta k'akk'arfan maza ce kusan zaka iya cewa ma kawunshi ne yayi Habeeb, saidai kyawun mahaifiyarshi da yayi kawai da manyan idanunta, belt d'in dake hannunshi ya nad'e ya yo kan Aisha zai tsala mata ta sake shigewa jikin Khadija, Khadija ce tace "Allah ka daketa sai ranka ya b'ace, kaji marar kunya kai, kai baka ji ance ko mutuwa tana kunyar idon mahaifi ba."


Juyawa yayi ya kalli Humaira hakan yasa Haseenah cewa "Karma ka fara matsowa nan kaji na fad'a maka."


Usman ne yace "Yarima meya faru? Laifin me su ka yi?" Cikin b'acin rai yace "Abba nasha fad'awa yaran nan su daina shigar min d'aki idan ban musu izinin shiga ba,yanzu fa haka kawai suka suka fad'a min d'aki ina kwance ba riga a jiki na."


Khadija ce ta katse da cewa "To shine zaka dake su? Ba sai ka sake musu nasiha ba, kaji sai kace wani gudan babban mutum, yaushe ne aka daina saka maka kaya."


Usman ne yace "Koma yau ne aka daina saka mi shi ai dai an daina saka mi shi saboda ya wuce munzalin, dan haka dole ya hukuntasu tunda sun k'i su san daidai da ba daidai ba."


Kallonshi Khadija tayi ta motsa bakinta hakan yasa Usman yace "Naji ki kamani amma bayan na mik'awa yarima na wannan yaran nan na bayanku."


Wata dariya Haseenah ta yi tace "Kana ganin zaka iya k'watar su a hannun mu ne?"


Wani kallo ya mata yace "Kin manta da k'ashi d'aya ne gareni, bugu d'aya zan mu ku kuji ku a makara."


Dariya Khadija tayi tace "To ina zaka zauna kai kuma?"


"A duniya mana." Ya fad'a ya na zama kusa da su, Haseenah ce tace "Kenan ka fara soyayya a waje bamu sani ba."


Shafa kanshi yayi da ya kusan cika da furfura yace "Ai wasu kyawawan yan mata na samu suka mak'ale min wai ni suke so, kuma na yi alk'awarin aurensu, ai yarima ma zai zama waliyi na."


Dariya suka saka a tare sai Khadija da tace "Komawa baya kenan, to idan zaka je d'aurin auren dai ka shafa gawayi a kanka danka rufe wannan farin abun na kan ka."


Sake shafa kan yayi yace "Alamar arzik'i ne ai, kuma naga kema akwaita a kanki."


Cike da k'aguwa Bilal yace "wai yanzu na zo da matsalata amma ku manta kun shiga sabgar gabanku, Allah ya shirya min ku iyayena, banda kamarku a duniyar nan."


Harya juya zai fita ya tsaya ya nuna su Humaira da yatsa yace "Kuma wallahi babu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login