Showing 111001 words to 114000 words out of 139085 words
Chapter 38 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
ka na so ma za ka iya tafiya da matar ka gida yanzun."
Sai lokacin murmushi ya bayyana a fuskar shi yace "Mama da gaske zan iya tafiya da ita? Kai Alhamdulillah Allah na gode ma ka."
Dariya Mama ta yi ta na kallo ya shiga ciki, dama k'ofar ba rufe ta ke ba kamar yanda tafi barinta mafi yawan lokuta, ya na tura k'ofar ya shiga ya yi daidai da Khadija ta idar da sallah ta mik'e tare da cire hijabin ta, riga ce jikinta ruwan madara mai k'ananan hannuwa wacce ta kama ta, sai bak'in siket da ya bud'e sosai bai kama jikin ta ba, saida gabanta ya fad'i ganin mutum kawai a d'akin, amma kuma saita kasa motsawa saboda tasan yau ta ta kam ta k'are dan idon shi na kan cikin ta, Usman da tunda ya d'ora idon shi akan cikin ta yaji k'wak'walwar shi ta fara tuna ma sa da wasu abubuwan, mamaki ne fal a fuskar shi har ya fara matsowa kusan ta, ta na ganin haka ta fara ja da baya a hankali shi ma ya na bin ta, daf da ban d'aki ta juya da sauri za ta shige ciki da azama ya rik'o hannun ta.
Janyo hannun ta ya yi har saida ya zaunar da ita bakin gadon ya tsaya gabanta sank'am kamar zai fad'a mata ya na kallo, kan ta k'asa ta kasa had'a ido da shi kafin yace "Ya mu ka yi da ke?"
D'agowa ta yi tace "Akan me fa?"
Had'e rai ya yi yace "Kar ki raina min wayo mana, Khadija me ye hujjar ki na b'oye min ki na da ciki? Akan me za ki min haka?"
Mik'ewa ta yi tace "Kaga malam dan Allah kar ka d'aga min hankali, ni babu wani ciki da na ke da, ko kai ka ga na yi ma ka kama da masu ciki ne?"
Wani bala'in haushi ne ya taso mi shi amma sai ya share yace "Tashi wuce muje gida sai mu yi maganar acan."
"Wane gidan kuma?" Ta fad'a ta na kallon shi, kai tsaye yace "Gidan ki mana."
Wani murmushi ta yi tace "Ni ai duk filaye ne gare ni har yanzu ban gina gida ko d'aya ba."
Cile da k'aguwa yace "Haba uwar yarima, gidan mu fa na ke nufi, ki tashi mu tafi mana."
Cikin nuna rashin damuwa tace "Au! Ai wannan gidan ka ne ba nawa ba, idan da nawa ne ma ai da ba ka yi abin da ka yi ba har na baro ma ka gidan."
A hankali ya durk'usa kan gwiwoyinshi ya rik'o hannayen ta yana murzawa yace "Khadija fad'a min me na mi ki in ba ki hak'uri? Ke kinsan ba zan iya cutar da ke ba, tunda mu ke da ke ba mu tab'a samun sab'anin da yasa mu ka raba shinfid'a ba bare gida, dan Allah ki fad'a min sai na baki hak'uri yanzu kuma mu koma gida tare, sanin kan ki ne ba zan iya bacci ba alhalin ke ki na nan."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Ka na nufin ka ce ba ka san ma me ka min ba?"
Kamar zaiyi kuka yace "Wallahi na manta Khadija, komai ya dawo min kamar sabo a rayuwa ta." Tab'e baki ta yi tace "To kaga ka tashi dai yanzu ka koma gidan ka kafin amaryar ka ta fara neman ka."
Tsaki yaja yace "Ina mi ki magana mai mahimmanci ke ki na magana akan wata, dallah malama ki tashi ki wuce mu tafi gida."
Waro ido ta yi irin mamakin nan tace "Eyee! Lallai ma mutumin nan, to ba zan je ba ina nan gidan mu."
Ba alamar wasa yace "Haka ki ka ce?" Ita ma ba tsoro tace "Eh, haka na fad'a."
Yatsunshi ya sa biyu ya kama agarar (jijiyar da ke bayan k'afa kusa da diga-digi) ya dinga murzawa da zafi, da sauri ta janye k'afar ta sai kuwa ya rik'e k'afar ya na fad'in "Ba dai kinfi son na mi ki hukunci a gidan ba? To ai sai mu zuba ni da ke, na ga wanda ya isa ya k'wace a hannu na yau."
K'ok'arin k'watar k'afar ta ta shiga yi amma ya hanata dama, idon ta ne suka cika fal da ruwa ta na so ta bashi hak'uri amma ta k'i magana, shi kam ko a jikin shi har cije leb'e yake ya na fad'in "Uhum! Da dad'i ko? To yaya yanzu za ki fad'a min dalilin ki na k'in fad'a min ki na da ciki?"
Jin zafi ya kai mata ya sa ta bud'a baki da k'arfi tace "Mamaaaaa, ki zo ki taimake ni."
Bushewa ya yi da dariya yace "Kuma a zaton ki za ta zo? Kar ki wahalar dani a banza ki fad'a min abin da na ke son sani."
Jin bala'in na k'aruwa ya sa Khadija fashewa da kuka irin na sangartattun yaran nan ta na fad'in "Dan Allah ka yi hak'uri zan fad'a ma ka, wallahi zafi ke akwai, dan Allah ka daina zan fad'a."
D'an tsagaitawa ya yi yace "To ina jinki." Saida ta fara goge hawaye tace "To d'anyi baya mana ka matse ni sosai."
Kallon da ya mata ya sa ta d'an matsa baya amma sai ya sake binta ba tare da ya mik'e tsaye ba, shiru ta yi shi kuma ya sake kamo k'afar ta yace "Ke fa na ke saurare, muguwa kawai, da meye nufin ki to? Ban cancanci zama uban d'an ba ko kuma ke kad'ai ke da shi? Allah sai kin fad'a min dalilin ki ko na rabu da ke."
Tangale kanta ta yi da hannayen ta ta rufe fuska ta na tunani, a hankali taji ya d'an d'ago ya zauna bakin gadon ya rumgumota jikin shi, cikin taushin murya yace "Nana, ki fad'a min komai da ya faru mana, meye ake b'oye min haka da ba'a so na sani? Kowa na tambaya sai ya yi shiru ba ya son fad'a min komai."
D'agowa ta yi daga jikinshi tace "Kaje ka tambayi Hajia ko Baba su za su fad'a ma ka komai."
"Ban damu da sanin komai ba Khadija, na fi damuwa da sanin abin da ya sa ki ke zaune gida."
Tallabo fuskarta ya yi yasa idonta cikin na shi yace "Khadija me nai mi ki da zafi haka?"
Kamar za ta fashe da kuka tace "Mun samu sab'ani ne da kai akan amaryar ka, sab'anin da ya sa ka yi abin da ba ka tab'a yi ba a rayuwar ka, shine ni kuma na dawo gida gaba d'aya a lokacin ba ka buk'ata ta a gidan ka."
Da tsantsar mamaki yace "Sab'ani? Amma me na yi to?"
"Duka, duka na ka yi." Ta k'arashe da sunkuyar da kan ta k'asa tana hawaye, dafe kan shi ya yi yace "Duka? Ni da hannu na?"
Tsaye ya mik'e jiki a sanyaye ya sake sunkuyawa gabanta ya d'ago fuskarta yace "Ki yi hak'uri Khadija, wallahi Allah bansan na yi ba sai yanzu da ki ke fad'a min, ki gafarce ni dan Allah kar ki hukuntani da laifin da bansan na aikata ba, yanzu haka kunyar had'a ido na ke da ke da ahalin ki."
Ya na fad'a ya tashi ya fita ko juyowa baiyi ba, Mama ya samu a in da ya barta da alama kan ta ya d'au zafi, sunkuyawa ya yi yace "Mama, Khadija ta fad'a min abin da ya faru, Mama ina mai baku hak'uri da gaba d'aya zuciya ta, ku yafe min dan Allah, ba dagangan na yi ba, kuma banyi dan cin zarafin ku ba, hasalima abu ne da sam banyi tsammani ko tunanin faruwar shi ba."
Mik'ewa ya yi tare da cewa "Saida safe Mama." Ya fad'a ya na barin falon ba tare da jiran me za ta ce ba, Mama kam sai taji tausayin shi ya kamata sosai, watak'ila har ya yi anfani da maganin da Garba ya kawo cewar Mama a zuciyar ta, Khadija ma tausayin mijin ta ne ya sa ko fitowa ba ta yi ba ta kwanta daga nan kuma bacci ma ya d'auke ta.
Kai tsaye gida ya sake komawa ya samu malam zaune k'ofar gida sai Bilal gefen shi da wayar shi a hannu, zaune ya yi akan tabarmar ganin haka ya sa malam cewa "Fodio lafiya dai na gan ka haka?"
Idon shi cikin na malam yace "Ba lafiya Baba, Baba ka fad'a min dan Allah me ya faru da ni ne? Sannan me na aikata a lokacin da na rasa tunani na? Kawai ganin abubuwa na ke kamar sabi kuma kamar a almara."
Tank'washe k'afafu malam ya yi yace "Fodio, abubuwa sun faru da dama, idan da ka nutsu kai da kan ka za ka iya tuna komai, amma ka kasa kwantar da hankalin ka ma bare har ka samu nutsuwar."
Cike da damuwa yace "Baba ina maganar nutsuwa ga wanda ya na kallo rayuwar shi ke barazanar fita daga gangar jikin shi, a yanzu haka fa Khadija na gidan iyauen ta zaune da kuma ciki na a jikin ta, Baba ban ma san tsawon lokacin da ta d'auka acan d'in ba."
Murmushi sosai malam ya yi yace "Watan ta uku yanzu."
"Wata uku?" Ya fad'a da k'arfi da zaro ido kafin ya d'ora da "Baba da sakin ta na yi fa da yanzu ta kammala idda kenan? Kutumar bala'i, Allah ya ceceni."
Dariya malam ya yi kafin yace "Ai kam dai, dan ni dai ka ganni nan ba zan tashi zuwa yi ma ka biko ba da girman ka da komai."
"Yanzu dai malam ku fad'a min abin da ke faruwa da ni, ina so na sani."
Gyara zama malam ya sake yi bayan dogon tunani da ya yi kafin yace "Abin da ya faru da kai ba zamu dangana shi da kowa ba, dan har yanzu ba mu san mai wannan alhakin ba, dan haka kai ma ba na so ka d'auki laifin ka d'ora kan wani ko wata, ka barwa Allah kawai shine zai ma ka sakayya." Jinjina kai Usman ya yi alamar gamsuwa kafin malam ya ci gaba da bashi labarin iya abin da ya sani kawai daga barin Khadija gida zuwa yau d'in nan, sosai al'amarin ya girgiza Usman tare da bashi mamaki, to shi kam waye abokin gabar shi da har zai mi shi haka? Kasa tunawa ya yi sai kuma zuciyar shi tafi ta'allak'a mi shi komai da Haseenah, dan a ganin shi ita ce za ta iya sawa ya manta da Khadija dan ta bar gidan ita ta zauna, to amma kuma malam yace kar ya d'orawa kowa laifi, ya barwa Allah zai ma sa sakayya dan haka ya ja baki ya yi shiru, amma kuma abin da ya ji yanzun ya sa ya tuna da abubuwa dayawa da su ka faru, sai dai ba duka ba, saida safe ya mi shi dan lokacin har bacci ya d'auki Bilal daga nan, ganin zai shiga mota ya sa malam cewa "To matar ta ka fa wa ka barwa ita anan? Ko nan za ta kwana ne?"
Zaune ya yi cikin motar ya kira ta a waya yace ta fito, ba wani jimawa ta fito cikin takun k'asaita da izza dan dama zaman gidan ya isheta, kafe fuskata ya yi da ido har ta k'araso, tabbas ba munin fuska ba ko munin halitta, sai dai wani abun al'ajabi wani irin haushin ta ne yake ji na taso mi shi, wanda ko farko duk da ba wani son ta yake sosai ba amma dai ba ya mata irin wannan k'iyayyar, zagayawa ta yi ta shiga suka d'auki hanya ba tare da sunwa juna magana ba, jin shirun ya yi yawa kuma ya d'auki hanyar gida ya sa tace "Kasan fa ba mu da abin da za mu ci a gida, ka siya mana kafin mu wuce ko."
Cikin isa da gadara ya juyo ya kalle ta, a hankali kuma ya d'auke kan shi daga kallon ta cikin mak'oshi yace "Uhum."
Saida ya tsaya ya siya mata iya cikin ta kafin suka wuce gida, suna shiga ya nufi k'ofar na shi falon, da sauri tace "Beby, ina kuma za ka je?"
Juyowa ya yi yace "...
*Gidan uban da ki ka aike shi mana.*ππ
04/03/2020 Γ 19:43 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*35*
"Zan d'an shiga ciki na kwanta ne saboda na gaji, ki ci abincin kawai dama ni na k'oshi."
Sake juyawa ya yi zai wuce tace "Amma yau d'akin ka za ka kwana ne?"
"Eh." Ya fad'a a hassale tare da juyowa ya na kallon ta ya ci gaba da cewa "Kuma ke ma ina so ki kwanta d'akin ki dan ba na son takura."
Da mamaki tace "Takura kuma? Ni ce ma zan zama takura a gare ka? Babban mutum wai lafiyar ka k'alau."
Ajiyar zuciya ya sauke irin ta takura masa d'in nan kafin yace "Lafiya k'alau, na yau kawai na ke so ki bar ni na kwanta ni kad'ai, ki yi hak'uri." Ya fad'a ya na wucewa ciki ya barta nan, mamaki ne ya kama ta sosai da tunanin ko lafiyar shi? Ita dai a saninta lafiya lau suka je gida, amma daga lokacin da ya shiga d'akin malam ba ta ma san da tafiyar shi ba sai da taji kamar su na waya da Hajia duk da dai ba ta da tabbacin da shi su ka yi wayar, ita ma d'akin ta ta nufa ta cire kaya ta yi wanka kafin ta ci abinci ta kwanta, sam ba ta samu wata damuwa ba wajen baccin ta, dan kuwa ba jimawa baccin ya d'auke ta.
A wajen Usman kuma kasa bacci ya yi ya na tunanin abin duniya, da farko dai da kunya ce ke neman sa shi yin k'asa a gwiwa, amma kuma saiya duba ya ga ai ba a sanin shi bane komai ya faru, sannan bai saki matar shi ba bugu da k'ari ta na d'auke da cikin shi, da haka kuma sai ya ji ya ma k'agu gari ya waye ko ya sake komawa wajen Dije, ba kuma zai gushe ba har sai ta dawo gare shi, saboda fatan dacewa ya sa ya d'auro alwala ya shiga fad'awa Allah kukan shi tare da neman taimakon ubangiji.
*Washe gari* da safe d'aurin aure, sammako sosai Usman ya yi ya hallara d'aurin auren bayan yace wa Haseenah ta yi k'ok'ari taje da wuri ita ma, haka ya fita kamar shine angon cikin babbar riga da 'yar ciki farare, ya na isa a k'ofar gida ya tsaya saboda mutanen da ya samu a wajen, nan su ka shiga gaisawa da mutane har lokacin da motar Naseer ta kutso cikin taron jama'ar, mazauni aka samarwa da motar kafin Mama ta bud'e ta fito daga ciki, Usman na ganinta ya tafi da azama dan kwasar gaisuwa sai ya ga Khadija ta fito a matsayin dreban da ta tuk'o motar, tsaye ya yi ya kasa k'arasawa saboda haushi, tabbas yasan ta na fita da gyale sai dai yau ne ya fara jin haushin haka, domin kuwa ta na fitowa gyalen ma a kafad'ar ta yake, duk da doguwar rigar shadda ce jikinta wacce ta fito da d'an cikin ta na wata biyar, amma dai baiji dad'i ba duk da ya ga sai gyara gyalen take, har saida su ka zo daf da shi kafin ya sunkuya ya gaishe da Mama ta amsa cikin sakin fuska, wucewa Mama ta yi shi kuma ya mayar da kallon sa kan Khadija da ita ma shi take kallo yace "Ke ba ka iya gaisuwa ba ne ko me?"
Cikin tsiwa tace "Um ban iya ba, ko ka koya min ne?"
Gyara tsayuwa ya yi ya na k'ara sab'a rigar shi a kafad'a yace "Uwar yarima wai yaushe ki ka raina ni ne haka?"
Ta na kallon idon shi tace "Tun ranar da ka fara wulak'anta ni saboda ka yi amarya."
Wani kallo ya mata kafin ya d'an saci kallon mutanen da ke wajen yace "Yanzu ko albarkacin mutanen nan ba zan ci ba na ga murmushin nan na ki mai saka ni bacci."
'Yar siririyar dariya ta yi tace "Toh fa Alhaji mai babbar riga, kai da za ka je d'aurin aure kuma me ya had'a ka da bacci? To ka farka idan mafarki ka ke, kai da sake ganin murmushin Nana Khadija kuma sai dai ko a lahira, a lokacin da aka min umarni da na shiga aljanna, to zan iya juyowa na kalle ka dan na ma ka bye bye, to fa zai iya yiwuwa a lokacin ne za ka ga murmushin."
Shi maganar ta dariya ma ta bashi, da sauri ya rik'o hannunta ya matso daf da ita yace "Ki na so ki ce ni kuma zan zauna har sai kin riga ni shiga? Ko kuma nufin ki ni ba ma zan shiga ba?, ai k'afar ki k'afa ta insha Allahu, in kuma ba haka ba to sai dai ki same ni a ciki kewaye da sabbin mata na."
Fizge hannunta ta yi tace "Ka na dukan nawa ne kuma ka ke tunanin za ka shiga aljanna."
Wucewa ta yi ta bar shi nan tsaye ya na ta dariya shi kad'ai, Murtala ne ya k'araso wajen shi yace "Mijin Khadija lafiya ka ke dariya kai kad'ai?"
Hararan shi ya yi yace "Ni kad'ai ka gani a wurin? Ba ka ga wacce na gani ba."
"Na gani kam, ince dai kun sasanta za ta koma?" Kallon shi ya yi sosai yace "Da alama fa sai ka tayani bata hak'uri, ran 'yar aljanna ya b'ace sosai."
Zaro ido Murtala ya yi yace"Wa? Ni! Sam ba dani ba, kai dai da ka mata laifi ka bata hak'uri amma banda ni."
"Au! Yanzu ka na nufin ba za ka tayani ba kenan? To nagode, ai na d'auka zan iya yin zaune gida ma kai kaje har sai ka dawo min da ita, ashe ba haka bane."
"A'a ni ba haka na ke nufi ba, kasan dai maganar