Showing 87001 words to 90000 words out of 139085 words
Chapter 30 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
_ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*28*
Saida ya fara ganin Haseenah ya tabbatar komai lafiya kafin ya nufo wajen Khadija da nufin bala'i, ya na shigowa falon sai ya yi sanyi ganin mutanen dake d'akin, a hankali yake takawa ya na kallon Bilal dake k'afafun Mama ta na bashi magani, Khadija ma da mamaki take kallon shi kamar ba ta tab'a ganin shi ba, da sauri ya k'arasa ya zauna gefen Khadija ya na fad'in "Yarima, bashi da lafiya ne? Me ya same shi?"
Shiru Khadija ta yi sai Mama ce tace "Bashi da lafiya ai tun jiya, amma da sauk'i sosai."
Hannu ya zura ya kamo shi kamar d'an shekara biyar haka ya rumgume shi a k'afafun shi ya na shafa shi yace "Yarima ba ka da lafiya? Ya jikin na ka da sauk'i ko?"
Da kai kawai ya ma sa alamar eh, rumgume shi ya yi a jikin shi ya kalli Khadija yace "Amma ya akayi ba ki kira ni kin fad'a min ba?"
Cikin hushi tace "Saboda kai ne silar shigarshi wannan halin, kuma ma naga me za ki yi mana idan na fad'a ma ka? Tunda ba damuwa ka yi damu..." Da sauri Mama ta kalle ta tace "Khadija."
Kallon Mama ta yi ta na kumburo baki, Mama ce ta d'ora da "Subhanallah, Khadija haka ki ka koma magana da mijin ki? Ki na hauka ne?"
Shiru ta yi sai Usman da ke murmushi ya kalle ta yace "Me ya sa ki ka yi tunanin haka? Taya zan zama sila baya bana nan."
Shiru kawai ta yi saboda Mama ta mata magana, mik'ewa Mama ta yi ta d'auki gyalenta ta yafa ta d'auki jaka ta kalli su Naseer dake gefe kamar sun zo neman aure tace "To sai ku tashi mu tafi ko, ko kuma nan za ku tabbata?"
Mik'ewa su ka yi a tare da d'ai d'ai suka bawa Usman hannu su ka yi sallama kafin su ka fita, ta na ganin fitar su ta kalle shi tace "Dama na bar Bilal gida ne saboda umarnin ka, amma ka sani ba zan sake wannan kuskuren ba wallahi, tunda dai na gama lura matarka ba imani ne da ita ba, sannan daga yau wallahi ba zan sake d'agawa kowa k'afa ba, duk wanda yace zai min kan kara to tabbas sai nai masa na itace."
Mik'ewa ta yi saida ta zo gaban shi ta karb'i Bilal ta d'ora a kafad'a saboda k'arfin halin kafin ta nuna shi da yatsa tace "Da nace kowa ina nufin kowa ma, ba sauk'i a al'amarin."
Za ta juya ne taji sallamar su Hajia da sauren yaranta mata biye da ita, tsaye ta yi ta na kallon su har su ka k'araso su ka zauna, Hajia ce ta kalli Bilal da ke kafad'ar ta tace "Kai namijin duniya ya jikin na ka?"
Wani irin mamaki ne ya bayyana a fuskar Khadija ta sunkuya ta aje Bilal ta kalle ta da kyau tace "Hajia, ya jikin shi fa ki ke tambaya? Hakan na nufin dama kinsan ba ya da lafiya amma shine bai samu kimar da za ku zo ku duba shi ba tunda ku ka shigo gidan nan, tunda rana fa na ke iya jiyo hayaniyar ku a gidan nan, amma sai yanzu za ku zo ku tambaye ni lafiyar shi, hum, to ba ni ku ka wa ba, kan ku kuka wa."
Juyowa ta yi ta d'auki Bilal za ta wuce d'aki Aziza tace "Aunty Khadija ga kayan shi in ji Haseenah."
Juyowa ta yi fuska a had'e tace "Bilal na da kayan da a shekara baya saka su, ku mayar mata ta mayarwa da bokan nata tace ba ma so."
"Khadija, wai baki da hankali ne? Ke kad'ai ki ka fi kowa baki anan da za ki zaunar da mu ki na fad'a mana magana, so ko ke kice dole ke ce akawa laifi kenan bayan duk abin da ki ka aikata, me ki ka d'auke ni ne da har za ki tsaya ki na fad'awa 'yan uwa na magana kuma daga ciki har da mahaifiya ta, ko kinsan da hushin ki na dawo garin nan? Amma shine za ki nuna ke ce ma akawa laifi, to ya isheki haka, maza wuce ciki zan zo na same ki."
Yanda ya ke maganar ne ya sa ta yi dariya tace "To ka had'iye ni mana kaga shikenan sai ka huta."
Ta na fad'a ba ta tsaya sauraren shi ba ta shige ciki da Bilal a hannu, tana shigewa Hajia tace "Haka kuma abin nata ya zama? Lallai mutum bashi da kama, yanzu waye zai iya cewa Khadija za ta yi abin da ta yi."
Rabi'a ce tace "Hum, dama ai sai anyi yunwa halin kowa ke fitowa."
"Gaskiya ne, yau na tabbatar da hakan." Cewar Hajia, Usman ne ya kalle su yace "Hajia ku yi hak'uri dan Allah, kar ku damu da abin da ya faru."
"Ya kar a damu, ba ka ji maganganun da ta fad'a mana bane, nan gaba mu ka san me za ta fad'a ko ta yi mana, za ta iya cewa ma Bilal d'an ta ne ita kad'ai."
Mik'ewa su ka yi su na fad'in "Sai anjiman ku."
Tafiya su ka yi Aziza ta koma wajen Haseenah, shi kuma d'akin Khadija ya koma, ya na zuwa ta kwantar da Bilal yace "Ya kamata kisan ina d'aga mi ki k'afa ne saboda abubuwa dayawa, amma naga sam kin kasa fahimta sai ma son wuce gona da iri, Khadija wannan fa mahaifiya ta da ki ka tsaya ki ka fad'a mata magana son ran ki, me ki ke ji da shi? Rashin kunya ko fitsara?"
Tsaye ta mik'e tace "Kalle ni da kyau kaga da me ya kamata ka kira ni."
Da yatsa ya nuna ta yace "Na zo ne dan na fad'a mi ki wani abu, wannan ya zama na k'arshe da hannun ki zai sake tab'a jikin Haseenah, in kuma ba haka ba wallahi zan d'auki matakin da ba lallai ya mi ki dad'i ba, kinji na fad'a mi ki."
"Haseenah? Haseenah fa ka ce? To in har kaga hannu na bai tab'a jikin ta ba ka tabbatar ba ta min rashin kunya ba, wallahi ko yanzu tace za ta min abinda ba zan d'auka ba ni kuma can ci uwar ta a gidan nan kuma a gaban ka."
Daf da ita ya matso cikin d'aga murya yace "Saboda ki nuna min kin rainani? Ban isa na fad'a mi ki kiji ba kenan?"
Kafin ta yi magana ya sake k'ure ta da fad'in "Bak'in ciki ki ke da ta samu ciki za ta haifa min wasu yaran? Shi ya sa ki ka yi k'ok'arin zubar mata da ciki, wallahi Allah ne ya ceceki cikin nan bai zube ba, da sai na sa kinyi aman duk wani abu da ke cikin ki kema."
Rasa abin fad'a ta yi saboda kukan da ke son taho mata, rab'awa ta yi da nufin shiga ban d'aki ya rik'o hannun ta ya nufi k'ofar fita da ita yace "Muke ki bata hak'uri, 'yan uwan ta ma na nan suna tsammanin jin hukunci daga gare ni, ba zan barki haka ba, amma da farko ki ba su hak'uri."
Jin wani sabon rainin hankali ya sa Khadija fizgo hannun ta da k'arfi tace "In kuma ka ga haka ta faru to tabbas ba ta hanyar aure aka haife ni ba."
Juyowa ya yi ya na kallon ta ita kuma ta gyara tsayuwa tace "Wallahi na rantse da sarkin daya busa min numafshi ko za ka kashe ni ba zan bawa uban kowa hak'uri ba, Usman." Ta kira sunan shi cikin d'aga murya ta d'ora da "Karfa ka yi tunanin sanin da ka min da, wallahi yanzu walkice ni daidai na ke da k'ugun ko wace shegiyyy..."
Marin da ya zabga mata ne ya sa ta fad'i gefe har gilashin ta na fita daga idon ta, dafe kunci ta yi ta d'ago kai ta kalle shi, cikin fitar hayyaci ya shak'o wuyan rigar ta ya mik'ar da ita tsaye yace "Wuce muje na ce."
Ba tate da tayi yunk'urin k'watar kan ta ba tace "Ba zan je ba wallahi, banga laifin da na yi ba da zan bawa wani hak'uri."
Wani marin ya sake kifa mata da k'arfi da ya sa Bilal zabura ya tashi zaune, sake dafe kunci ta yi ta na kallon shi dishi-dishi, da hannu ya nuna mata k'ofa yace "Wuce muje."
"Ba zan je ba." Ta fad'a ta na k'ok'arin tashi tsaye, a karo na uku ya sake gwab'a mata wani marin ya na fad'in "Ai kuwa za ki mutu kamar yanda ki ka ce, tunda taurin kai ne da ke."
*Lovely sister kin tuna ko? Ki ci gaba da hak'uri komai zai wuce da ikon mai kowa mai komai.*
Bilal na ganin haka ya sauko daga kan gado ya rik'e hannun mahaifin shi ya na hawaye yace "Abba dan Allah ka daina, ka bar dukan ta."
Ture shi ya yi gefe d'aya ya na fad'in "Kai bar ni na nuna mata na fita taurin kai, zuciya ai ba ki fini ba." Ya k'arashe da kifa mata wani marin, a tak'aice saida Usman ya mata lafiyayyun mari har guda takwas a kumatu kamar ya samu jaka, da ta kasa tashi ne gashi ba ta iya jin komai ba ta ganin komai ya sa take zaune har yanzu k'asa, cikin hargagi ya ke fad'in "Wai ba za ki tashi ba?" Ya fad'a ya na zura k'afa ya na kai mata hanb'ara, Bilal ne ya rik'e shi ta baya ya na kuka sosai ya na fad'in ya k'yale mi shi Mummyn shi, Usman kam ido sun rufe rai ya b'ace bai ma san me yake yi ba sai harbinta ya ke da k'afa ya na had'awa da hannu ya na nausarta, da sauri Bilal ya zo ya rumgume ta ya juyo da kan shi ya kalli Usman yace "Abba na tsane ka, ba na son ka, ka fita ka ba mu wuri, Allah saiya sakawa Mummy na."
Cak ya tsaya da hannun shi sama daga d'agawar da ya yi zai dake ta, duk da ya ji kalmar tsanar har k'asan zuciyar shi amma saiya basar ya nuna ta da yatsa yace "Yanzu hankalin ki ya kwanta da ki ka ji d'ana ya na fad'in ya tsane ni? To ki zuba ruwa k'asa kisha dan farin ciki, ni ma kuma Allah ne zai saka min da har ki ka yi sanadiyar da d'ana ya furta min kalmar tsana, munafuka kawai shed'aniya, kuma ki sani wallahi in har ki ka ce wannan halin za ki ci gaba da nunawa a gidan nan kenan, to ki na tare da wahala wallahi."
Juyawa ya yi ya fita, d'auko gilashinta Bilal ya yi ya saka mata, mik'ewa ta yi ta shige ban d'aki ba dan tasan in da take saka k'afar ta ba, zaune ta yi bakin bahon wanka ta kunna ruwa suna zuba ta fashe da kuka, tabbas yau tabbatar da Usman baya hayyacin shi tunda har zai iya mata wannan dukan a gaban d'an su, mutumin da magana marar dad'i ba ta tab'a shiga tsakaninsu ba amma yau har da kiran ta munafuka, ta jima zaune ta ci kukan ta kafin ta mik'e ta wanke idon ta ta kashe ruwan ta fito, lokacin fuskar ta har ta kumbura kamar an hura balam-balam, jakunkunanta ta d'auko ta d'ura duk wani abun buk'atar ta a ciki Bilal na kallo, hijabi ta saka ta kalli Bilal tace "Bilal."
Cikin muryar kuka yaron ya amsa da "Na'am Mummy."
Cikin muryar da tasha kuka tace "Tafiya zanyi Bilal, ka zauna gidan mahaifin ka dan ba na jin zan iya dawowa gidan nan, amma ka sani ina tare da kai kaji ko."
Da sauri ya taso yace "A'a Mummy, ni dai dan Allah ki tafi da ni, wallahi ba zan zauna nan ba, yanzu Abba ba ya so na, aunty amarya ma ba so na take yi ba, ni dai wallahi binki zanyi."
"Bilal ba zan iya tafiya da kai ba, ba wai dan ba na so na tafi da kai d'in ba, sai dai nasan mahaifin ka ba zai bari ba, ka tuna ranar ma da zan tafi shi ya hana na tafi da kai? To ka yi hak'uri ka zauna kaji, idan ba ka jin dad'in zaman nan sai ka ce ya kai ka gidan su Hajia."
Cikin kula yace "Ni dai ba na so Mummy, idan kuma ki ka tafi ki ka bar ni wallahi guduwa zanyi daga gidan nan."
Cikin sanyin jiki tace "Shikenan je ka had'o kayan ka."
Ya na fita ta zauna bakin gado ta zuba tagumi ta na fitar da wasu hawaye masu zafin gaske, ba wani jimawa Bilal ya dawo da k'atuwar jakar shi shima ya sanyo duk wani abun buk'atar shi, kallon shi ta yi tace "Ka d'auko kayan makarantar ka?"
"Eh, suna ciki." Mik'ewa ta yi ta kashe duk wutar d'akin ta kile da makulli suka fita, a hankali cikin sand'a ta isa ga k'ofar da za ta shigo da mutum falonta da falonshi ta kulleta kafin suka fita ta d'aya k'ofar, nan ma rufewa ta yi kafin tace Bilal ya kira mai gadi k'ofar gida sannan ya tsayar mu su da adaidaita sahu, ba wahala kam mai gadi ya shigo har in da take ya tsaya yace "Mai adaidaitar na k'ofar gida Hajia."
"Yawwa karb'i nan." Ta fad'a da bashi jakunkunan tace "Ka fitar mana da su muna zuwa yanzun."
"To Hajia." Ya fad'a ya na d'aukar jakunkunan ya jasu Bilal ma ya ja tashi jakar, saida ta lek'o ta hangi motar Usman alamar ya na gidan, saida taga ficewar mai gadi kad'ai ta fito ita ma ta fita, har an yiwa kayan nasu wuri dan haka za ta shiga mai gadi yace "Hajia, lafiya dai ko? Ko tafiya za ku yi ne?"
Juyowa ta yi ta kalle shi tace "Ka yi hak'uri Baba mai gadi, duk da dai abin da ya faru yanzun sirrine na gida na, amma kai ba yau muke tare ba, tunda na dawo sabon gidan nan na tarar da kai, tun Bilal na jinjiri, matsala ce ta faru da tasa dole sai na bar gidan nan na wani lokaci, ku yi hak'uri, na bar ka lafiya."
Ta na gama fad'a ta shiga adaidaitar suka wuce, da kallo ya bisu ya na fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, ita kuma amaryar da abin da ta zo da shi kenan? Wannan wace irin jaraba ce, mata da mijin ta kullum cikin farin ciki, idan ka ji hayaniya to suna wasa ne kamar yanda su ka saba, amma yau gashi su na shirin rabuwa dalilin wata, kai Allah ya kyauta."
Usman na ciki shi da Haseenah bai san tsiyar da ake ba, ba jimawa kam adaidaita ya sada Khadija da gidan su, Mama na ganin su da kaya ta fara salati da sallalami, kai tsaye d'aki ta nufa ta aje kayan ta ta wuce d'akin ta, tashi Mama ta yi tabi bayan ta sai matan yan uwan ta ne su ka bisu da ido, matar Habeeb ce kad'ai ta iya cewa "Aifa lokacin ya yi."
Shiru sauran su ka yi dan suma kawunan nasu a rarrabe suke, kowa da b'angaren da yake saboda suma akwai uwayen gida akwai kuma amare.
Babu abin da Khadija ta b'oyewa maman ta duka ta fad'a mata, duk da taji ba dad'i sosai amma sai bata nuna mata ba, kallon maman ta tayi tace "Dan Allah Mama taimaka min da maganin ciwon kai."
Tashi kawai Mama ta yi ta d'auko ta kawo mata tasha ta kwanta, matar Mansur ta shigo d'akin dan su kwashi labari sai dai ta samu Khadija har ta fara baccin wahala da fuska har yanzu a sumtume, sam Mama ba ta fad'awa 'yan uwan ta ba ko a waya sai dare da suka dawo su ka tarar da wannan abin takaici, lokacin Khadija zazzab'i ya sake rufe ta, Naseer har da k'walla ya yi da ya kalle ta, yanda ya sunkuyar da kai ne ya sa Habeeb dafa shi, goge fuskar da ya yi ne ya tabbatar musu kuka yake, Bashir ne yace "Kai haba dai maza, kuka fa? Ai ba kai ya kamata ka yi kuka shi ya kamata ya zubar da hawaye."
Wasu hawayen ne suka sake taho mi shi yace "Yanzu domin Allah me ya sa Usman ya yi haka? Mufa mun bashi ita ne da tunanin zai kula da ita, me ya sa zai mana haka yanzu? Saboda kawai ana ganin ita marainiya ce mahaifin ta ya rasu."
Sun jima d'akin ta suna tattaunawa in da take kwance ta dunk'ule, saida dare ya yi suka tashi suka koma nasu dak'unan, saida tasha magani kafin ta sake kwantawa, sai dai ba ta yi bacci ba har aka kira sallah asuba, sallah ta yi ta sake komawa ta kwanta ta na istigfari tasbihi da hailala da hannun ta na dama.
Ko da Usman ya fahimci basa gidan haka kawai yaji bai wani damu ba, hakan ya sa ma da safe ko da ya je gida ya samu su Hajia da maganar ya kuma fad'a mu su kar suce za su je su dawo da ita, harda had'a su da Allah akan su barta harta shiga hankalin ta, Bilal kuma d'an shi ne ba ta isa ta raba shi da shi ba, amma malam yace sam ba da shi za ayi haka ba, a k'arshe ma tambayar su dalilin faruwar haka akayi, fad'an Hajia shine "Makulli Usman ya bawa Haseenah ta aje na mota da zai tafi, ita kuma ta tashi fita tace ta bata, shi kuma yace kar aba kowa idan za'a fita a fad'a mi shi zai aiko da wani ya kaisu duk in da za su je, shine ta turmushe yarinya da k'aramin ciki ta karb'i makullin, dalilin hka fa ya kusa sawa ta yi b'ari."
Duk da jin haka yace zaije ya dawo da ita gidan ta, kuma kamar yanda ya fad'a ya cika maganar shi, amma maganganu mabanbanta ya ci karo da su, musamman da suka fad'a mi shi har da duka, har d'akin Khadija aka