Showing 114001 words to 117000 words out of 139085 words

Chapter 39 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

nan ta manya ce ba iri na ba, kuma tsakanin ka da Khadija ma ai ba ta b'aci."


Ba jimawa da shigar Khadija mutane aka fito dan tafiya wajen d'aurin auren, daga ciki har da Mama dan dama d'aurin auren take son samu, nan aka shiga motoci aka wuce d'aurin auren, Khadija na zaune d'akin Hajia Nura ya shigo da sauri ya na kiran sunan Hajia, ya na ganin Khadija yace "Uwar gida yane, ke ba ki je d'aurin auren ba?"


Hararan shi ta yi tace "Wa? Allah ya sawak'e, me zanje na yi a d'aurin auren kishiya, ai ina daga nan ina aika mu ku da addu'a."


"Yawwa hakan ma ya yi ai, addu'ar ita mu ke buk'ata ai." Cewar Nura ya na kallon Hajia da ta fito daga d'aki, cikin k'aguwa yace "Hajia takalma na da na baki jiya na ke nema."


Ledar hannun Hajia ta mik'o mi shi tace "Dama nasan su za ka nema ka ke min wannan kiran."


Bud'ewa ya yi ya saka takalman kafin ya juya zai fita yace "Hajia ku fara tausar min k'irjin ta kafin na dawo."


Haka suka wuce wajen d'aurin aure gidan waliyin Choukra, kuma ba'a b'ata lokaci ba waken yin abin da ya kai kowa wurin, nan aka d'aura auren *Nura Ali* da amaryarshi *Choukra Sabi'u*, bayan taya juya murna da farin ciki ne abokan ango su ka nufi inda za su ci su sha, manyan mutane kuma suka dawo gidan su ango dan cin abinci suma.


Bayan tafiyar 'yan d'aurin aure ne ba jimawa kuma Haseenah ta zo ita ma kamar yanda Usman yace ta zo da wuri, a d'akin Hajia suke zaune nesa da juna amma babu mai kula wani, haka suke zaune Khadija na hira da mutanen da ba su je d'aurin auren ba, Hajia ce ta fito daga uwar d'aki ta kalli Khadija tace "Nana wai kinga Bilal kuwa?"


"A'a Hajia, ya na ina ne?"


"Ai tare da malam su ka shirya su ka fita, kin ganshi kamar shine angon sai rawar k'afa ya ke, saida na gargad'e shi dai kan karya kuskura ya kalli wasu mata."


Dariya kawai ta yi ba tace komai ba har mutane su ka fara shigowa aka fara hayaniya, nan su Hassana da sauran mutane suka fara raba abinci ana kaiwa mutane.


Bilal ne ya shigo tare da malam kai tsaye wajen mahaifiyar shi ya nufa ya zauna kan k'afafun ta, wanda hakan ya yi daidai da shigowar Usman da kwalbar lemu a hannun sai malam a biye da shi, kwantar da kan Bilal ta yi a k'irjin ta tana sumbatar shi tace "Yarima na yi kewar ka fa, kwana uku ka na nesa da ni."


Bilal kenan d'an gata sai kuwa ya sake wani cakume ta kamar zai sa nonon ta a baki yace "Mummy yunwa na ke ji fa."


Lek'a fuskar shi ta yi tace "Ban gane ba, ba ka ci abinci ba ne a waje?"


Cikin shagwab'a yace "Ban ci ba, to duka fa manya ne a wajen."


Murmushi ta yi tace "To yarima na k'arami ne? Yaro ana bikin kawun ka ace ka na rasa abin da za ka ci, to ba ka had'u da Abban ka bane?"


K'ara tusa kanshi ya yi cikin jikin ta yace "Um um."


D'ago kan ta tayi za ta yi magana sai ga Usman tsaye gaban ta ya na fad'in "Yarima yanzu da girman ka za ka hau k'afafu haka?"


Da sauri Bilal ya d'ago ya na ganin Abban shi ne ya yi tsaye ya mak'ale mi shi a wuya, rumgume shi ya yi shima yace "Me ya ke faruwa ne na ga ka na ta zuba shagwab'a haka?"


Khadija ce tace "Bai ci abincin bane, amma kuma kai ga hannun ka nan har da lemu ma ka ke korawa."


Kallon ta ya yi yace "To yanzu shan lemun nawa ya zama haramun ne ko me?"


"Ya zama mana, taya za ka jefa loma bakin ka ba ka san gudan jinin ka ya ci ko bai ci ba." Yanda ta had'e fuska ne ya sa ya ga ko ya fad'a mata shi ma bai ci abinci ba ba yarda za ta yi ba, dan haka ya juya da Bilal d'auke da shi yace "Yarima muje ka zab'i abin da ka ke so ka ci, rabu da mahaifiyar nan ta ka yau tunda safiya ta waye ta tashi da masifa, can ta k'arata da masifarta."


Shiru ta yi sai kallon k'eyar shi da take, shi kam jin ta yi shiru ya sa ya juyo dan ya san ta na nan ta na kumbura, wata irin harara ta dalla masa da tasa shi b'arkewa da dariya yace "Yi hak'uri Hajia, nasan me ye matsalar ki, ki ba ni hak'uri sannan ki lallab'a ni sai na mi ki magani."


Yanda ta motsa bakin ta ya sa ya fahimci me take nufi, dan haka ya mata gwalo yace "Idan kin kamani ki mayar da gabana gabas ki yankani."


Da haka ya fita su ka bar gidan, tun lokacin ba ta sake ganin Bilal ba har biki ya yi biki ana ta bayar da zafi, Haseenah na d'akin Aziza kwance sai narkewa ta ke, sai dai kuma abin ya d'an dameta na yanda kowa baya ma kula ta, sai wanda ya ganta ne dole ya ke iya gaisawa da ita, amma har Aziza sai ta shigo d'akin ta fita ko kallon in da take ba ta yi ba, haka yamma ta yi aka raba abinci, kasancewar a d'aki take ita kad'ai ya sa aka rabe abinci ba'a ma san da ita ba, babu wanda ya damu da hakan sai ma ran su Hassana da ke k'ara b'aci.


Da dare mutane duk sun tafi gidan amarya da ango, Khadija ce d'aki ke gaggauta shirya dan tafiya tare da masu jiranta a waje tunda ta zo da mota, sai Haseenah da tun sallah magriba ta tafiyar ta gida, Hajia na zaune kan katifa gyangyad'i na neman fizgar ta Khadija tace "Hajia bacci ne?"


Kallon ta tayi tace "To tukuna dai."


Saida ta gyara jakarta a kafad'a tace "To ni zan tafi, kuma ina ga daga can gida zan wuce, sai dai gobe idan Allah ya kaimu."


"To Allah ya yarda Khadija, Allah hutar da gajiya, angode sosai Allah ya saka da alkairi, saida safe." Duk ta na maganar ne saboda Khadija har ta kai bakin k'ofa ta na amsa mata, za ta bud'a labulen d'akin Usman ya sallamo, kaucewa ta yi da tunanin ya wuce amma saiya wani tsare ta da ido yace "Hajia ke kuma wannan kwalliyar fa? Duk ta zuwa kallon ango da amaryar ce?"


Kallon Hajia ta yi sai ta ga ita ma su take kallo dan haka ta share shi kawai, hannu ya sa aljihu ya ciro da hankici (hankiciep) ya kai a bakin ta zai goge mata jan baki, da sauri ta ja baya ta na rufe bakin tace "Ya za ka goge min? Yanzu fa na saka shi, kuma ina da bak'o ne a gida."


Wani kallo ya mata yace "Bak'o kuma? Wane irin bak'o?"


Ba alamar wasa tace "Bazawari nn..." Bugun da ya kai mata a baki ne ya sa ta saki k'ara ba ta shirya ba tare da rufe bakin ta durk'ushe kan gwiwanta, Hajia da ta zabura ne ta kalle shi tace "Alhaji meye haka? Me tai ma ka?"


Zaune ya yi akan kujerar da ke iya fuskantar Khadijar ya na hararan ta, cikin d'aga murya Hajia tace "Fin k'arfi ne ko me? Dallah malam ka bata hak'uri ko."


Rai b'ace ya kalli Hajia yace "Hajia ba ki ji me yarinyar nan ta ke fad'a ba ne, ina matsayin mijin ta za tace wani wai bak'o na jiran ta, har da cewa wai bazawarinta." K'wafa ya yi hakan ya sa Hajia kallon Khadija da har yanzu ba ta motsa ba tace "Yi hak'uri kinji Khadija tashi ki tafi abinki, ba zan iya tashi bane saboda k'afafu na amma da na rama mi ki dukan ki, ki yi hak'uri kinji."


D'agowa ta yi a hankali ta sauke ido a kan shi sun mata jawur, murmushi ta yi ta kalli Hajia tace "Saida safe."


Mik'ewa ta yi ta fice daga gidan, ta yi k'ok'ari ta sauke ma su jiran ta a waje gidan amarya amma ita ba ta tsaya ba ta wuce gida.




*A gurguje*




A kwana biyu zuwa lokacin da aka kammala sabgar bikin Nura Usman ya shiga taitayin shi, dan ko wayar shi Khadija ba ta d'auka bare ta saurare shi idan ya zo, hakan ya tab'a shi sosai dan ya damu, haka ma Haseenah ta fara damuwa sosai akan lamarin na shi, dan har yanzu ba su kwana d'aki d'aya ba, gari na wayewa kuma zai buga sammako yaje gida ya na lallab'ar malam ya je ya dawo da Khadija, sam ba ya da lokacin wata Haseenah yanzun, abinci ma idan ta dafa sai dai ta ci ita kad'ai amma ban da shi, ba ya son zuwa gidan saboda ba ya son ganin Haseenah da idon shi, ya na iya k'ok'arin shi sosai wajen b'oye k'iyayyar da yake mata, ya rasa dalilin da ya sa ya ke sake jin tsanar ta a kullum idan ya ganta, ba ya son jin muryar ta ko ganin giftawarta a gidan, duk da ba ya da kokwanto akan cikin da ke jikin ta cewa na shi ne amma dai ba ya jin ya na k'aunar abin da ke cikin ta kamar yanda ya ke k'aunar wanda ke cikin Khadija, a haka har aka kwashe *sati biyu* babu abin da ya sauya.


A sati biyun nan ne Usman ya yi tattaki har k'auyen su Baba Garba mai gadi ya je ya bashi hak'uri akan abin da ya farusannan ya nemi da ya dawo bakin aikin shi, ya hak'ura ya kuma nuna masa komai ya wuce shi dama bai rik'e ba saboda ya san ba laifin shi bane, amma dai ba zai iya komawa aiki ba saboda jiki da jini, amma idan ya amince akwai d'an shi da ke neman kangarewa zai iya had'a shi da shi saiya zauna a mazaunin shi, ya amince ya taho da yaron mai sunan *Rabe*, tabbas ya fara aiki yanda ya kamata sai dai burin Usman akan yaron ba wai ya zama mai kula da pliwoyin (flawers) gidan shi bane da k'ofa, ya na so a gama wannan zagon na karatu sannan ya d'ora shi ya ci gaba da karatun shi tunda ya na yi ya dakatar saboda shirme, duk da haka kuma Usman bai daina bibiyar Khadija ba, yanzu haka har ya gaji da sawa Bilal na rok'on ta akan ta dawo, Hajia da malam dama sun ce ba ruwan su, a k'arshe ya samu da k'yar ya lallab'a Murtala ya je ya mata magana, nuna masa ta yi ba komai za ta koma, amma ya na barin gidan tace ba yanzu sai ya sake shiga hankalin sa, jin shiru shiru ya sa saida ta kai ga Usman ya turo Nura da Kabir da kuma Mannir su ka je bata hak'uri, sai lokacin Mama tasan da irin tsiyar da Khadija ke tsulawa, dan sam babu wanda ya tab'a ce mata ya zo bata hak'uri dan ta koma, Usman kuma idan ya zo ta kan basu wuri ne dan su tattauna, kuma ba ta nuna mata wasu alamu na rashin jituwa, hakan ya sa ba ta san me ke faruwa ba, shi ma Usman ya so ya b'oye mata ne dan yasan za ta iya tirsasata akan ta dawo, duk da ya na matuk'ar so ta koma amma ya fi so ta koma dan ganin damar ta, kuma har yau ba ya ganin laifin ta akan hukuncin da take masa, dan kuwa babu abin da ta rage shi da shi a rayuwa amma ya mata kishiya, sannan ya rasa meya shiga kan shi da ya dinga cin mutuncin ta, dan wasu abubuwan sai yanzu ne idan ya na rarrashin ta take iya fad'a mi shi irin abin da ya mata, bugu da k'ari kuma bata gama hucewa ba ya zo ya bugar mata baki har saida ya kumbura, wanda kullum mitar hakan take masa, nan Mama tace su koma Khadija za ta dawo gidan ta ba jimawa, sun tafi da farin cikin samun nasara amma sam Khadija tace ba yanzu zata koma ba, da Mama ta fara fad'a kuma sai 'yan biyar suka tausheta suka ce tunda ba yarinya ba ce kawai a rabu da ita, hakan ya sa a ranar Usman ke ta zuba idon ganin Dije amma shiru, ko bacci baiyi ba a ranar ya na sak'awa ya na warwarewa, washe gari da dare ya je gidan da kan sa, a falo ya samu duk 'yan biyar d'in da wasu daga cikin yaransu, Mama na d'aki hakan ne ya sa ya zauna suka gaisa sosai, Naseer ne yace "Auta kam ta na ciki, amma kafin ka shiga ciki ka kawo kud'in ganin ta."


"To in dai hakane me zai hana ka fad'a min gaba d'aya farashin da zan biya, kaga sai ka d'auke ta da kan ka ka kai min ita gida na." Cewar Usman cikin raha, dariya su ka yi sai Habeeb ne yace "K'anwa ta fa tsada ne da ita, farashin ta baya fad'uwa."


Cikin zolaya yace "To kunga, duk cikin kun nan naga babu wanda zai iya taimaka min, dan haka ni zanje na yi yak'i na ni kad'ai, in har k'anwar ku bata koma gida na zuwa gobe ba to ku canza min suna."


Cike da cika baki ya mik'e zai nufi d'akin Khadija Naseer ya bushe da dariya yace "Wane sunan za mu saka ma ka to?"


Juyowa ya yi ya harare shi yace "Ka zab'a da kan ka mana."


Bashir ne ya yi saurin cewa " sai mu saka mi shi *Mani*."


Komai baice ba ya wuce d'akin, ko sallama baiyi ba yau dan al'amarin ba sauk'i, kuma cikin sa'a saiya samu Khadija tana ban d'aki, murmushi ya yi kafin ya cire hular kan shi ya aje gefe ya kwanta kan gadon ya yi d'a-id'ai, kusan minti biyu ya d'auka kafin Khadija ta fito daga ciki d'aure da k'irji, kasancewar cikin ta ya sa ya d'age sosai daga sama har ya kan iya hango cinyoyinta, ita kam gilashin ta ne take gogewa ta na k'ok'arin sakawa, ta na sawa ta ja ta tsaya da tsoro fal a idon ta, bud'ar bakin ta cewa ta yi "A'uzu billahi mina shaid'anir-rajim, innahu min Suleimana wa innahu bismillahir-rahamanir-rahim."


Ba tare da damuwa ba Usman yace "A kan ki, wato na ma zama shaid'an ko?"


Wata ajiyar zuciya ta sauke ta matso kusan shi tace "...




*Ina k'aunar ku.*
06/03/2020 Γ  12:54 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘




_SAMIRA HAROUNA_




*Litattafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


```Fatan alkairi masoya```




_Bismillahir rahamanir rahim_




*36*




"Malam lafiyar shigo min d'aki haka kawai, wa ma ya baka izinin shigowa nan?"


Kamar ba dashi take magana ba ma saiya share ta, ta jima tsaye ta na kallon shi ganin bai damu da tsiyar da take ba ya sa ta juya ta isa gaban madubi ta fara shafe shafe kamar yanda ta saba, lokaci lokaci takan juyo ta kalle shi amma abun mamaki shi kuma hankalin na ga waya ya na dannawa, saida ta gama ta nufi wajen kaya ta d'auko riga, ba tare da ta cire d'aurin k'irjin ba ta saka wando da rigar nono kafin ta saka doguwar rigar, juyowa ta yi ta kalle shi tace "To malam, idan ka gama da d'akin sai ka rufe min ko, ni zan fita."


Gyale ta d'auka ta fesa turare ta juya zata fice, da sauri ya duro daga kan gadon yace "Ina za ki je?"


Ta na kallon idon shi tace "Bak'o..." Sai kuma ta yi shiru saboda tuna ranar da ya kwamtse mata baki, rik'e k'ugu ta yi tace "Ka ban hanya mana zan wuce."


Rumgumo ta ya yi jikin shi ya dawo da ita ya zaunar akan gado, ture shi ta yi tace "Malam ka daina tab'a ni mana."


Sosai ya kalle ta yace "Khadija, har yanzu fa ni mijin ki ne, a labarin da ki ka bani ba ni ne na kore ki ba, amma Khadija ki na hukuntani abisa laifin da na ke tunanin ko da na aikata shi ne dadangan za ki yafe min, me ya sa haka Khadija? Kin daina so na ne yanzu? Ko kuma ba kya son ki tsufa a gida na ne yanzu kamar yanda ki ke fad'a min."


Mik'ewa ta yi tsaye tace "Ni dai kawai ka fitar min daga d'aki, so ka ke mutane su d'auka wani abun ne ke faruwa anan? Dan Allah ka tashi ka fita."


Yau fa ya yi niyyar ba zai bar gidan nan ba babu wani sakamako mai kyau, dan haka ya haye gadon ya gyara kwanciya ya kalle ta yace "Ba zan fita d'in ba, idan kuma ki na ganin za ki saka k'artin 'yan uwan ki ne su fitar da ni to bismillah."


Mamaki ne ya sa ta zaro ido tace "Abban Bilal, yan uwan nawa ne ma k'arti? To ai ko ba k'artin banza bane tunda su na ciyar da duka girman gidan nan dama wasu dake kewayen shi."


Hararan ta ya yi yace "Ni kuma na gaza ko? To ki jaraba kiran su ki gani mana idan za su iya."


Rumgume hannaye ta yi tace "Amma dai kasan tsaf zan iya saka su kefa min kai cikin kwalbatin unguwar nan ko?"


Wata irin dariya ya bushe da ita yace "To ki kira su mana, na fad'a mi ki ina tsoro ne."


Fitowa kam ta yi daga d'akin amma abun mamaki ba kowa a falon har telebijin ma an kashe, mayar da d'akin ta yi ta rufe ta dawo ta zauna kan kujerar da ke gaban madubi, kallon ta ya yi yace "Hajia ko za ki iya samo min kayan bacci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login