Showing 96001 words to 99000 words out of 139085 words
Chapter 33 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
kuma idan ya na son hawan k'afafu ga nata nan zai hau, da haka har 'yan biyar su ka zo suma suka d'ora nasu farin cikin ana addu'ar Allah ya sauketa lafiya.
*Mu ma dai munce ameen.*
Kamar kullum Usman ya je gaishe da iyayen sa, kuma kamar yanda ya saba riska yau ma malam baya nan, sai dai ya bar sak'on wannan ruwan addu'ar a bashi ya sha, saida ya shanye Hajia ta fito daga ban d'aki tace "Tashi kaje ka yi wanka ruwa na nan na had'a ma ka."
Kasa magana ya yi saboda mamaki da kuma rashin sanin abin da zai fad'a, saida ta maimaita da "Ko ba ka ji ba ina magana?"
Saida ya gyara zama ya kalli jikin shi da kyau yace "Amma Hajia na yi wanka fa, wane irin wanka ne zanyi yanzu kuma?"
"Ka tashi ka shiga lokaci tafiya yake." Marairaicewa ya sake yi yace "Amma Hajia wai dan..." Katse shi ta yi da "In za ka tashi ka tashi kafin ka b'ata min rai."
Tashi ya yi kamar zai k'urma ihu saboda haushi, ya rasa irin wannan sabon al'amari na iyayen shi, haka ya tub'e kayan da ya sanyo yanzun ya yi wanka da wannan hakukuwan na magani, haka ya sanyo kayan ya fito duk ruwan jikin shi sun tsaya a kayan, ya na fitowa Hajia kuma ta bashi damammiyar fura da maganin jiya a ciki, saida ta masa jan ido yasha dan cewa ya yi jiya baiyi bacci ba, hakan ya sa ta bud'e mi shi ido sosai sannan ya sha, wata 'yar kwalba ta d'auko bak'a mai d'auke da maganin *jibda* a ciki, da kan ta ta lak'ato a hannu ta shafa mi shi a wuya zuwa kai da hannuwan shi har zuwa damatsenshi, bashi ta yi tace ya d'iba ya shafa a cikin shi har zuwa k'irji, kamar zaiyi kuka ya kalle ta yace "Hajia wai duk wannan na miye haka? Wannan abun nan amai zai saka ni, sam warin shi babu dad'i."
Shiru kawai ta yi ba tace komai ba dole ya shafa yanda take so, mik'ewa ya yi yace "Hajia ko za ki bani magungunan sai ki nuna min yanda ake sha, ina ga kamar hakan zaifi ko?"
Kallon shi ta yi tace "Alhaji, kai ka haife ni ko ni na haife ka?"
Cike da ladabi ya rusuna yace "A'a Hajia ki yi hak'uri, ban fad'i haka dan b'ata ran ki ba."
"To ka wuce ka tafi in da za ka je kawai, sannan ba na so ka fad'a wa wani ko wata batun magungunan nan, ko da kuwa matan ka ne ban yarda ba, kaji ni ko?"
"Naji Hajia, amma wallahi da gaske na le idan ki ka bani zanyi aiki da su, Hajia ki duba kiga hakan zaifi a gani na, misali yanzu na wankan nan, idan da a waje na yake da haka ba za ta faru ba, amma idan ya na nan zai zamana kullum sai na yi wanka anan kenan, sannan idan na yi tafiya za'a dakatar da maganin kenan har sai na dawo, sannan Hajia..."
"Dakata dallah." Ta katse shi tare da d'aga hannu, shiru ta yi ta jima ta na tunanin abin da ya fad'a kafin ta gamsu ta d'auko duka magungunan ta bashi, saida ya karb'a ta nuna mi shi yanda zaiyi aiki da su kafin ta sake jadadda mi shi bata so ko matar shi ta sani, alk'awari ya mata babu wanda zaiji dan haka ta bashi ya tafi, aljihu ya saka su ya fita daga gidan ya shiga harkokin gaban shi, sai yamma ya dawo gida cin abinci, zai shiga wanka ne ya fito da komai na aljihun shi ya na ajewa akan gaban madubi, ya na aje ledar maganin Haseenah ta kalle shi tace "Oga wannan fa na miye haka?"
Ba tare da wani damuwa ba yace "Um, ba na fad'a mi ki zan karb'o wannan maganin ba a wajen Hajia? To ai sune na karb'o d'in, da k'yar ta bani su bayan na mata alk'awarin ba zan bari kowa ya sani ba."
Ya na fad'a ya shige wanka, zaune ta yi tana kallon magungunan har ya fito, cikin taushin murya tace "To yanzu ya za ka yi da su kenan? Za ka ci gaba da sha ne?"
Da k'arfi yace "Wa? Ni! Haba dai Hajia, kinga kawai d'auke su ma daga nan ki zuba su shara danni ko d'aya ba zanyi anfani da su ba."
Mik'ewa ta yi da wani mirmushin mugunta a fuskar ta ta kalle shi tace "Haka na ke son ji dama, dan ba na son namiji mai tsirfa kamar mace."
*Da dare* Usman da malam da kuma rakiyar Murtala da d'aya abokin nashi mijin Hajia Salamatu wato *Alhaji Salisu* suka je aka nemowa Nura auren sahibar shi *Choukra*, cikin girmamawa aka yi abin da za ayi aka gama kafin abin da zai biyo baya, ko da su ka dawo har gida suka fara aje malam in da ya umarci Usman da ya shigo su yi magana, suna shiga ya bashi ruwan addu'a yasha, ganin Nura a gidan ne ya sa yace ya je gida gobe da safe ya same shi kafin ya fita, da "To yah Fodio." Ya amsa kafin ya fito suka wuce.
*Washe gari* da safe Hajia Sadija ce ta yi sallama gidan surukan Khadija in da Mansur ke binta a baya, tarba ta musamman suka samun daga wajen Hajia da malam d'in kafin su ka nutsu, cikin dattako Mama tace "Nasan za ku yi mamakin gani na da sanyin safiyar nan, to ba wani abu bane dama face wani alkairi da ya tunkaro mu, shine na ce ba za mu yi farin cikin mu kad'ai ba, kuma da kuma Usman d'in ku na da hakk'in ku san me ke faruwa."
Malam ne yace "To gaskiya dai ba mu yi mamaki ba, abu d'aya da na ji shine fargaba, kuma bai wuce fargaban tunanin makomar auren yaran mu ba."
Murmushi ta yi tace "Malam kenan, kamar yanda na fad'a ne a farko alkairi ne ke tafe damu, kuma insha Allahu babu abin da zai shafi makomar auren yaran nan, yanzun ma k'addara ce kawai ta gifta a tsakanin su, amma komai zai daidaita da yardar Allah."
"Allah yasa haka Hajia." Cewar malam yayin da Hajia kuma tace "Allah ya yarda, ya kuma kawo mana k'arshen matsalar."
"Ameen ya Rabbi." Mama ce ta d'ora da "Dama dai ba wani abu bane Bilal ne za'a wa k'ane ko k'anwa idan Allah ya amince."
Da sauri duka suka kafe ta da ido kowa da mamaki, Mansur ma da kallo ya bita da mamaki, dan sam bai d'auka abin da zai kawosu ba kenan, amma ya zaiyi shiru ya yi ya na sauraren ikon Allah, Hajia ce tace "Wai Hajia ki na nufin Khadija juna biyu ne da ita?"
Dariya mama ta yi tace "K'warai kuwa."
Da tsantsar farin ciki tace "Kai Alhamdulillah, Allah abin godiya, Allah mun gode ma ka, gashi bayan shekaru goma sha uku za ka k'ara azurta baiwar ka da ni'imar ka wacce babu wanda ya isa ya bawa wani sai kai, baiwar da kud'i basa sayanta kuma alfarma bata bayar da ita."
Malam da hak'oran shi ke waje ya na faffad'an murmushi ne yace "Tabbas hakane, arzik'i ne da imanin ka ko kafircin ka bai isa ya baka shi ba, sai mai bayarwa ya ga damar baka."
"To wannan dai shine dama na ce bara mu zo mu fad'a mu ku, dan bai kamata ku kasa sani ba."
Malam ne yace "Gaskiya ne Hajia, kuma mun gode da wannan girmama mu da ku ke yi, Allah ya saka da alkairi."
"Ba komai wallahi." Mama ta fad'a ta na mik'ewa ta na gyara mayafin ta tana ci gaba da fad'in "Mu zamu wuce, dama zanje 'yar kasuwa ne na ce mu fara biyowa ta nan d'in."
Mansur mik'ewa ya yi suka mu su sallama, har k'ofar gida malam ya rakaso in da ya sake jadadda ba su hak'uri akan abubuwan da suka faru, sannan yace a gaishe mi shi da su sosai, da haka su ka wuce shi ma ya dawo gida suka k'ara jinjina al'amarin, suna haka Nura ya sallamo d'akin tare da Aziza cikin shiri, har k'asa suka gaishe da iyayen su kafin Nura yace "Zan aje Aziza makaranta ne daga nan na biyo gidan yah Fodio, jiya yace na je gida na same shi."
Malam ne yace "To shikenan Allah ya tsare, Allah ya mu ku albarka."
"Ameen Baba." Su ka amsa suna mik'ewa, Hajia ma d'orawa ta yi da "Allah ya tsare, sai kun dawo."
"Ameen Hajia." Cewar Aziza suna ficewa.
Mansur na d'aukar hanya ya kalli Mama yace "Hajia ta, dama abin da ki ka zo fad'a mu su? Wallahi ko kad'an banyi tunanin haka ba."
Ba tare da ta kalle shi ba tace "Kenan da ka sani da ba zaka kawo ni ba?"
Dariya ya yi yace "Wane ni, ni d'in banza na kasa kai ku in da ku ke so."
"Dan haka ka ja min bakin ka kayi shiru, in kuma ranka ya b'ace to rufe ni da duka." Ta fad'a ba alamar wasa, dariya ya sake yi shi dai yace "Allah ya huci ranku Hajia ta, ban fad'i haka dan b'ata ran ku ba wallahi, amma a gafarce ni."
Shiru ta yi basu sake magana ba har ya kawo ta yar kasuwa wajen *Nasruminallah* ta fita ta lek'o tace "Zan d'auki lokaci anan, saboda akwai atamfofin da zan duba, idan ka na da aikin ke ka wuce kaje in da za ka."
"To Hajia ta ame za ku koma kenan?" Kai tsaye tace "A adaidaita mana."
Waro ido ya yi yace "Ah haba dai, Hajia ki na da mu a cikin garin nan mu barku ku hau adaidaita sahu, haba dai wuce nan ai wallahi, Hajia ta shiga kusha zaman ki, zan jira ku har lokacin da ku ka gama."
Sai lokacin ta masa murmushi mai tsada cike da so da k'auna tace "Allah ya bar min kai."
Cikin jin dad'i shi ma yace "Ameen Hajia ta, ai wannan addu'ar kad'ai ma ta isa tasa na kwana wajen nan ina jiran ku."
Dariya kawai ta yi ta shiga shagon da ya kawo ta, shi kam gyara zama ya yi ya k'ara sautin wa'azin da ya ke saurara, ya na haka Bashir ya kira dan tambayar in da ya kai mu su uwa su, nan ya fad'a mi shi komai ai sai Bashir ya fara zazzaga fad'a wai akan me Hajia za ta mu su haka, ai sai su d'auka ko wani abu suke so a gurin su ko kuma su na son amayar da yar uwar su ne, Mansur kam da ya ji ya cika mi shi kunne kuma ya na gaba da shi babu rashin kunya tsakanin su sai raha, hakan ya sa yace "To yallab'ai Bashari ni zan kashe wayar sai ka kira wayar Hajiar ka fad'a mata haka."
"Wallahi zan wulak'ance idan ka sake kira ni da Bashari, fitsararre kawai, shine ma har za ka ce na kira Hajiar, wato so ka ke kaga ta yi hushi da ni ko? To ba zan kira ba."
Cikin dariya Mansur yace "Dan haka ni ma sai ka shafa min lafiya da surutun nan naka." Ya na fad'a ya kashe wayar ya na ci gaba da dariya, dan ya san in ya koma gida sai su sake wata badak'alar akan kashe mi shi waya da ya yi, shi kam Bashir jefar da wayar ya yi ya na ci gaba da mita, Aisha dai na saurarn shi dan yau ya na d'akin ta har ya shirya ya fita su ka gaosa da Khadija bai daina mita ba.
Nura na aje Aziza ya wuce gidan dan dama babu nisa sosai daga nan, saida sula gaisa sosai da mai gadi kafin ya wuce ciki, Haseenah na madafa ta na soya dankali saboda wuyar da take ji, Usman kuma na d'aki ya na bacvi dan lokacin tashin shi baiyi ba, har saida Nura ya tsaya k'ofar shiga falon Usman ya tsaya ya d'an fara bubbugawa, Haseenah dake kallon shi tana ta fad'a wai miya kawo shi da safiyar nan, sai lokacin ta lek'o ba tare da tunanin rigar baccin da ke jikin ta ba tace "Sannu ko?"
Juyawa Nura ya yi ya sauke idon shi a kan ta, d'auke idon shi ya yi lokaci d'aya sai dai ya na shakku ko ita ce amaryar ma ko ba ita bace, dan shi dai dama ba wani saninta sosai ya gama yi ba har yanzu, musamman kuma yanzu da yake ta taso daga bacci ne duk a hargitse take, hakan ya sa ya ga ta masa wani irin muni kamar tsohuwar akuya,π Nura bala'i, a tak'aice shi ma yace "Sannu, mai gidan fa?"
Cikin yamutsa fuska tace "Alhaji ya na bacci, kuma lokacin tashin shi baiyi ba, sai dai ko za ka dawo wani lokaci."
Wani kallo ya mata sama da k'asa yace "Da alama ba ki gane wane ne ni ba, amma ko Khadija dake gaba da ke na zo gidan nan tana taso min in har ina son ganin shi, amma bara ki gani."
Wayar shi ya ciro daga aljihu ya danna lambar Usman ya doka masa kira, murmushi ta yi tace "Ni Hassenah suna na, ita kuma Khadija sunan ta, kaga dole hallayar mu da d'abi'ar mu za ta banbanta, ba lallai abin da ta maka ba ni ma shi zan maka, dan haka na fad'a maka Alhaji na bacci."
Ta na fad'a ta fito daga madafar ta bud'a k'ofar falon ta shiga, ta na shiga Usman kam bacci yake hankali kwance, kai tsaye wajen wayar shi ta nufa dan ta na nesa da shi kuma ta na vibration, d'auka ta yi ta kashe wayar gaba d'aya sannan ta aje ta fito, ta gaban Nura ta sake wucewa ta koma madafa ta ci gaba da aikin ta, shi kam ko da ya kira ba'a d'aga ba kuma da ya sake kira ya ji a kashe yasan ita ce, rai b'ace ya juya ya fita dan a cewar shi in ya tsaya ya na kallon ta to tabbas zai d'auki man da take suya da shine ya k'ona mata fuska da shi, dan haka ya fita daga gidan.
Ko da ta kammala abin da take wanka ta yi ta shirya ta taso Usman, taya shi ta yi ya yi wanka ya shirya ya fito suka fara kari, cike da kasala ya kalle ta yace "Wai ina waya ta ne ban ganta ba?"
"Ta na d'aki." Ta fad'a a tak'aice, wata hamma ya yi ya kalle ta yace "Wallahi gaba d'aya jiki ba dad'i, ba na da ra'ayin fita yau kam."
Murmushi ta yi tace "Zan so kasancewa tare da kai na tsawon wunin nan, idan haka ta faru zan ji dad'i sosai."
"To shikenan, yanzu kije ki fito min da k'ananan kaya na canza wannan manyan da na ji dad'in zaman gidan."
"To." Ta fad'a da azama ta nufi d'akin shi, d'orawa ya yi da "Ki biyo min da waya ta dan Allah."
"Ok." Ta fad'a ba wani fargaba a tare da ita, ba jimawa ta dawo da kayan da wayar, da ka ta ta saka mi shi kayan ta ninke waccen ta mayar d'aki, ta na shiga d'akin ya kunna wayar ya fara kiran wayar Bilal, ya yi mamaki da yaron ya kasa d'aukar wayar shi, dole ya hak'ura ya barshi sai lokacin ya ga sak'o da ke nuna Nura ya kira shi bai samu ba, kiran Nuran ya yi wanda har yanzu yake cika ya na batsewa cike da haushin Haseenah, a kakkauce suka gaisa kafin Usman yace "Jiya na ce ka zo ka same ni gida, akan wani dalili ne ba ka zo ba, ko ka na so ka nuna ban isa bane?"
Cikin b'acin rai Nura yace "Kuma yaya, ka tambayi wannan shed'aniyar amaryar ta ka mana, tunda safe na zo amma tace ka na bacci wai ba za'a tashe ka ba, ni kuma naga ko shugaban k'asa ne kai tunda har kai ka ce na zo ai dole a barni na ganka, amma ta rufe ido wai ita mai miji." Ya k'arashe maganar da k'wafa, Usman da ya yi shiru ya na sauraren shi zuciyar shi na tafasa saboda ya tab'o masoyiyar shi, tabbas da ya na tsaye gaban shi wallahi da ya sai ya mare shi, dan haka ya gyara zama daidai lokacin kuma Haseenah ta fito daga d'akin, cikin b'acin rai Usman ya fara fad'in "...
*Yan uwa ku taya ni da addu'a, bΓ©bΓ© Abdul Latif ba lafiya, Allah ya bashi lafiya.*
24/02/2020 Γ 21:49 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*31*
"Yanzu Nura ni ka ke kallo ka ke fad'a ma haka? Ko dan ka na ganin a waya ne shine ya ba ka damar fad'a min abin da ka ga dama? Lallai wuyan ka ya isa yanka Nura, har ni za ka bud'a baki ka aibata matata a gaba na a dodon kunnuwa na, to nagode, kuma ka yi hak'uri idan ran ka ya b'ace saboda kiran da na ma ka, ni dama ba aikin ka zanyi ba, na ce ka zo ne dan na baka kud'in da za ka fara shirye-shiryen bikin ka tunda an riga da an gama magana, amma tunda har ka ci mutuncin matata a gaba na ba tare da fargaba ba, to na fasa sai ka je ka samu malam saiya ma ka komai, ko kuma ka je ka fad'awa wacce ta sanya aka nemo ma ka auren ka ga saita d'auki nauyin komai."
Ya na fad'a ya kashe wayar ya jefa kan kujera, zaune ta yi ta na kallon shi tace "Ya dai babban mutum na ji ka na waya haka kamar ka na fad'a? Kai da wa ne haka?"
Cikin fusata yace "Ni da wannan banzan Nura fa, wai har ni zai kalli