Showing 42001 words to 45000 words out of 139085 words
Chapter 15 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
farin ciki ko karsashi, haka Bilal ya tafi makaranta Khadija kuma ta zauna kafin Uwani ta zo.
Bayan Uwai ta zo yau Khadija ta ji bata buk'atar raini a wajen Haseenah, hakanne ya sa ta d'auko tsohuwar ajiyar gas d'in ta mai d'aukar tukunya d'aya ta sa Uwani ta d'ora silalar nama dan suyi na su girkin, su na cikin aikin kam sai ga Kaltume ta sallamo, da farin ciki Khadija ta tarbi k'awar ta, sun jima suna hira anan wajen kafin aikin ya yi nisa Khadija ta barwa Uwani ta k'arasa kula da shi, d'aki su ka koma suka dinga hira har Khadija ta tsegunta mata abinda ya faru daga zuwan amarya har zuwa jiya, nan Kaltume ta jinjina al'amarin kafin ta d'ora da "Kinsan me na ke so dake k'awata?"
A raunane Khadija tace "Sai kin fad'a k'awata, wallahi kaina ya kulle."
Gyara zama Kaltume ta yi tace "Da alama yarinyar da fitsara ta shigo, amma ki bita ta bayan gida, ki nuna mata na gaba ya yi gaba, na baya kuma sai tsinkaye, ki nuna ke ba wai shekaru ku ka yi tare da shi ba, ki nuna mata ke goggagiyace a fannin sanin mijinki, ki nuna mata na ku ba irin na su bane, sannan *wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa*, kissa, k'awata yanzu kishi ma cikin kissa ake yin shi, kada ki kuskura ki bari yarinyar nan ta gane kina kishi da ita, bare harta fahimci kuna samun matsala da mijinki, k'awata abun ya na da wuya sosai, saboda ya na buk'atar k'arfin zuciya, amma ni nasan za ki iya, saboda kin jure fiye da wannan ma, yanzu ki fad'a min yaushe ne Usman zai dawo hannunki."
"Na yarda Hajiata, amma ai ko ban fad'a mi ki ba ai kin sani"
"Hakane kuma fa." Cewar Kaltume, matsowa ta yi ta rad'a mata abu a kunne, a tare suka bushe da dariya harda tafawa da hannu, Khadija ce tace "Banda mastala dake k'awata, nasan za ki gyara ni."
Bayan fitar Usman kam gida ya nufa, ya samu mahaifinshi ma na shirin fita, saida ya duk'a k'asa ya gaishe su kafin ya zauna kan tabarmar da Hajia ke zaune, fita malam ya yi Usman ya bishi da "A dawo lafiya."
"Allah ya sa." Ya fad'a fita, kallon Hajia ya yi yace "Su Nura har sun fita ne?"
"Sun fita tun safe." Cewar Hajia, d'orawa ya yi da "Ba wani abu da ku ke buk'ata?"
Ba tare da ta d'ago ba tace "Babu komai Fodio, Allah ya yi albarka."
"Ameen Hajia."
Shiru ne ya d'an ratsa kafin Hajia ta kalle shi da kyau tace "Jiya su Rabi'a sun zo nan su ke fad'a min wani abu da ban ji dad'in sa ba ko kad'an, sai dai kuma na yi mamaki da hakan ta faru a gidan ka, duba da tsayawarka akan iyalinka da kuma hak'urin ita Khadijar."
Ajiyar zuciya ya sauke yace "Hakane Hajia, nima abun ya ban mamaki, sai dai koma miye ni nafi ganin laifin Haseenah, tun da Khadija ai ba yau mu ke tare ba, ko tsakani na da ita bamu tab'a samun matsalar da za ta saka mu d'agawa juna murya ba."
"Toh, haka kai ka ke gani, amma yan uwanka ba haka su ke gani ba, sunfi ganin laifin Khadija."
Murmushi ya yi yace "To Hajia koma me su ke gani ai wannan matsalar su ce, tun da dai ni ga yanda nake gani kuma na sani."
"Hakane, Allah dai ya kyauta, amma dan Allah a saka ido sosai saboda gudun abin da zaije ya dawo."
"Insha Allahu Hajia."
Mik'ewa ya yi ya zura takalmin shi yace "Hajia ni zan wuce, amma anjima da dare zan dawo, dan mun kwana biyu bamu had'u da yan rigamar nawa ba (k'annan shi)."
Daroya ta yi tace "Gaskiya kam, dan tuni ma su ka fara k'orafin amarya ta b'oye ka."
"Na sani dama ayi hakan." Ya fad'a ya na dariya, har ya juya Hajia tace "Yawwa har na sha'ada ban fad'a ma ka ba."
Juyowa ya yi ya dawo ya sunkuya, d'orawa ta yi da "Jiya matar *Issoufou* (d'an k'anin baban shi) ta haihu, an samu 'ya, idan ka samu dama sai ka je, su ma kuma matan sai ka fad'a mu su."
"Ah masha Allah, insha Allah kam Hajia zanje, amma na yi mamaki da bai kira ni ba."
"Watak'ila ya manta ne."
"Ba shakka kam."
Da haka ya bar gidan kuma ya na shiga mota ya kira Issoufou, take yace mi shi su had'u gidan yanzu zai je, haka ko akayi, ka zuwan nashi alkairi ne, domin kuwa kud'i ya bashi ma su yawa ayi hidima, bayan tafiyar shi kuma sai ya ya sa aka kawo mi shi kayan abinci, daga nan kuma makaranta ya wuce d'aukar Bilal.
Suna ta hirar su cikin farin ciki sai ga Usman tare da Bilal, sannu da zuwa suka ma sa in da ya dinga tsokanar Kaltume su na wasa da dariya, da haka ya lek'a wajen Haseenah, ya samu ta na girki ba ta gama ba, dan haka ya fita yace sai ya dawo, saida ya dawo su ka yi sallama da Kaltume, sai dai mamaki ya kama shi ganin su na cin abinci har da Bilal ma, dan shigowar shi ya ga gas a waje da tukunya, sam bai kawo a ran shi abinci su ka girka ba, haka ya fita da tunani iri iri da kuma niyyar tsayar da wannan abun, dan ba zai yarda tun yanzu su raba mi shi kan gida ba ta hanyar raba abinci.
_Ah to banga laifinka ba._π€·ββ
*Luv u guy's*
24/01/2020 Γ 21:19 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
_*ALLAH GATAN BAWA*_
*16*
Farar miya Haseenah ta yi da shinkafa, ba wai miyar ba ta yi bane a wajen Usman, sai dai ji ya yi cin shinkafar ta gundure shi, kuma hakan baya rasa nasaba da sabon da Khadija ta mi shi na girka abinci kala kala, musamman da tasan ba ya san shinkafa sosai, sai ta yi wata d'aya ba ta girka ta ba, yanzun ma bai wani ci mai yawa ba ya bar shi, ko da ya yi wanka ya shirya falon Khadija ya shigo, Uwani na ganin haka ta mik'e ta fita, Bilal kuma dama ya na ciki ya na shiri, Kaltume kam ta na sallah la'asar ta wuce gida, zaune ya yi kalle ta ta na fad'in "Har ka fito?"
"Um." Ya fad'a ya na sake kafe ta da ido, ita kam gyara gilashinta ta yi ta kalle shi tace "Ya dai? Da magana ne? Wannan kallon haka."
K'asa ya kalla kafin ya kalle ta yace "D'azu da na shigo sai na ga kamar girki ku ka yi ko?"
Ba tare da shakka ba tace "Eh, girki na yi, da matsala ne?"
Gyara zama ya yi kamar zai had'e ta yace "Sosai ma, Khadija kar ki ce min ba ki hango matsalar da ni na hango ba, hakan bai dace ba, kuma gaskiya ba na so, idan har zai yiwu, to cikin d'aya dole ku yi d'aya, ko dai ku had'a kanku ku dinga girki tare, ko kuma dai duk ranar girkin d'aya to d'aya ba za ta tab'a d'ora min tukunya ba da sunan girki ba, wannan hukuncin yankakke ne, kuma umarni."
Mik'ewa ya yi ya juya ya kalli d'akin Bilal ya kalli agogon hannun shi, mik'ewa ta yi ta kalle shi tace "Ban k'i ta taka ba, amma kafin ka yanke wannan hukucin ya kamata ka fara fad'awa amaryarka cewa ba'a raba abinci a gidan nan, in dai har za ta ci gaba da ware mana abinci ni da yarona, to wallahi ba zan ci ba haka ma d'ana, kuma ko kaga ai bama zauna da yunwa ba alhalin Allah ya hore abinci ta ko ina, wannan shine."
Ta gaban shi ta rab'a za ta wuce ya rik'o hannunta, kallon ta ya yi yace "Na fad'a mi ki ba na so, raba abinci kuma na yan kwanaki ne da ba su taka kara sun karya ba, idan ki ka duba tsawon lokacin da mu ka d'auka tare hakan bai tab'a faruwa ba, me ya sa yanzu za ki gagara fahimta Khadija? D'an lokaci fa kawai tace a bata ita ma ta san ta na da miji, me ya sa za ki zama mai son kan ki dayawa, me zai rage ki idan ki ka hak'ura ki ka ci abincin, nan da lokacin da kwananta zai k'are fa shikenan komai ya wuce."
Rik'e k'ugu ta yi da hannu d'aya tace "Uhum! Anzo gurin, yau kuma sai gashi ka na fad'in wai ni ce mai son kai na, ni ce mai son kai na yau? To na ji kuma nagode, amma ka sani in dai wannan ne son kai to tabbas ni mai son kai na ce, wallahi ba zai tab'a yiwuwa ba ta barbarad'a min iskanci a abinci sannan ta bani na ci, wallahi ka ji na rantse ko ba zai yiwu ba, rai a baran mai shine, lafiya kuma uwar jiki, daidai da ciwon hannu wannan idan ya same ni akwai abin da za ka iya yi min ne? Ni fa zan ji zafin kuma na yi jinyata, hasalima duk soyayyar da ka ke sauki burutsun cewa kana min wallahi babu abin da za ka iya tsinana min, haka kawai kuma sai na jefa kai na a motar da na tabbatar ba ta da birki, rai fa guda d'aya ne."
Yanda take masifa sai abun ya ba shi dariya da mamaki, a zaman shi da ita bai tab'a ganin ta na fad'a haka ba sai yau, b'ata rai ya yi yace "Wallahi ba da wasa nake ba, kar ki sake d'ora min tukunya indai har ana girki a gidan nan, kinji na fad'a mi ki."
Za ta yi magana Bilal ya fito daga d'akin, sai kawai ta yi murmushi ta sa hannu ta shafo d'an gemunshi ta kashe masa ido tace "Ban ji da kyau, d'an sake maimaita min."
Dariya ce ta so sub'uce mi shi sai ya dake ya matsa kusan ta ya rad'a mata a kunne "Wallahi karki sake na sake ganin kin aza girkin ki, in ba haka ba rai zai b'ace fa."
Bilal ne ya shiga tsakansu ya na fad'in "Idan na bi taku sai na makara islamiyya, muje Abba."
Hannun shi ya kama ya na juyowa ya na kallon Khadija, ita kam wani shegen murgud'a baki ta yi irin ai ba ka ma isa d'in nan ba, daga yanda ya motsa bakin shi ya tabbatar mata da k'wafa ce ya yi, gwalo ta masa tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya ta d'auki wayar ta, su na fita ta ci gaba da latsa wayar ta hankali kwance, kamar daga sama ta ke jin k'amshin daddawar kalwa na bad'e ko ina na gidan, tashi ta yi ta fito farfajiyar gidan sai ta fahimci daga madafar su ne ya ke fitowa, kai tsaye ta shiga ta samu Haseenah ta zage ta na tuk'a tuwon shinkafa, da murmushi Khadija tace "Amarya sannu da aiki, yau kuma tuwo ake mana?"
Wani takaici ne ya taso ma Haseenah wacce ke wahalar tuk'a tuwon, k'ala ba tace mata ba sai Khadija ce ta sake cewa "Sai dai kuma mijinki baya cin tuwo da dare, ko bai tab'a fad'a mi ki ba? Musamman ma na ga wake ne ki ke miyar da shi, kuma ba ya cin wake ko kad'an, amma za ki iya had'a ma sa wani sassauk'an abun, mu sai mu ci tuwon dan munyi kewar shi."
Ran Haseenah ne ya yi mugun b'aci tace "Kutumar uba, baiwar Allah na fad'a mi ki ina neman taimakon ki ne? Kinga Khadija, gaskiya ba na son haka, mijin ki ba ya cin tuwo a lokacin da ke kad'ai ce cikin gidan, yanzu kuma Haseenah ta shigo, dan haka ki barni na yi rayuwa ta mana, ki barni ni ma na kafa salon nawa tarihin a gidan nan kuma a zuciyar miji na, amma ba ki dinga min shishigi ba, ba lallai dan kin saba mi shi da saka kalar fari ba ki ce nima wannan kalar ki ke so na saka mi shi, ki barni na yi abin da ya dace, nan gidan miji na ne."
Wani warrr Khadija ta yi da manyan idon ta kafin ta sa hannun ta tana fifita da shi tana fad'in "Wash Allah, zafi."
Kallon Haseenah ta yi da murmushi tace "Sannu mai miji, Allah ya bar k'auna."
"Ameen." Ta fad'a har da zaburowa, fita Khadija ta yi, tsaf Haseenah ta gama tuwonta ta mulmule, da kan ta ta kawowa Khadija na su tuwon, ko k'ala ita ma ba tace da ita ba har ta fita, Uwani ce ta tashi tafiya tace "Uwani d'auko wani kwano a d'akin can ki tafi da abincin nan."
D'aya d'akin ta shiga da ke da tarkacai abubuwan buk'ata ta fito, juye tuwon ta yi ta tafi da shi bayan sun yi sallama, Bilal ne ya shigo gida shi kad'ai da takarda a hannun shi, rumgume maman shi ya yi ita kuma tace "Wa ya dawo da kai ne?"
" *Bilyaminu* ne Abba ya tura ya d'auko ni, Mummy karb'i wannan." Ya fad'a bata takardar, ta na dubawa tace "Har wata ya k'are kenan?"
Kai kaxai ya d'aga mata, ba shi ta yi tace "To ka aje wurinka idan Abbanka ya dawo sai ka ba shi, amma ni zan iya mantawa."
A tare su ka tashi ita ta shiga d'akin ta saboda magriba ta gabato sosai, kaya kawai Bilal ya canza ya wuce masallaci, Khadija ma na idar da sallah ta shiga wanka, shiryawa ta yi sosai kafin ta lalabi gilashin ta na jiya da Usman ya cilla kan gadon, dan tun jiya bata waiwaye shi, shi ta saka dan ya fi mata kyau sannan ta fito, zaune suke ita da Bilal su na kallo su na hirar su, bayan sallah isha'i ko da su ka yi sallah abincin ranar da Uwani ta kwashe mata a kula ta d'auko ta zuba, tare su ka ci hankali kwance su ka k'oshi, hamdala su ka yi kafin su ka tashi kamar ba su ci ba.
Kamar yanda ya yi alk'awarin komawa gida haka ya wuce, ya kuma samu su Kabir Mannir da Nura, hakan ya sa suka bud'a babin hira su ka dinga yi, Haseenah da ke jiran shigowar shi taga shiru sai da ta kai ga kira, amma sai ya d'aga yace ya na gida zai zo ba da jimawa ba, amma fa bai zo d'in ba saboda suna tattaunawa da ahalin shi, sai wajen *22:20* ya baro gidan ya nufi gida, Khadija har sun kwanta ita da Bilal ya shigo, ko da ya ga babu wuta a falon sai ya wuce falon shi kai tsaye, Haseenah na ganin shi ta d'ago kai ta kalle shi, ba fara'a ko sakin fuska tace "Sannu da zuwa."
Sai da ya kamo hannun ta tayi tsaye ya rumgume ta yace "Sannu da gida."
Kamar ba ta son magana ta amsa da "Yawwa."
Kallon fuskarta ya yi yace "Ki yi hak'uri na barki ke kad'ai ko? Ina can gida tare da yaran nan su na ta min shirme."
Cikin shagwab'a tace "Na ji to, yanzu dai mu je ka yi wanka sai ka zo ka ci abinci."
Rimgume ta ya yi yace "Wallahi kamar kinsan kam na d'ebo yunwa, muje ki kintsani yanda ya kamata."
D'akin shi su ka nufa, bayan ta taya shi wanka ya canza kaya su ka fito, ya na jan kujera ya kalle ta yace "Da alama su Bilal har sun kwanta ko?"
Kallon shi ta yi tace "Eh to ban sani ba dai, amma tun da na ji shiru babu hayaniyar tv na ke tunanin haka."
Ba tare da ya kalle ta ba yace "Haseenah me zai hana idan ba na nan ki dinga zuwa wajen su ki na zama ku na hira? Ina ga hakan ai zaifi ko? Tunda daga ke sai sune a gidan, kuma sune abokan rayuwar ki a yanzun."
Ta na aza marar tuwo a farantin ya kalle ta, bai kai ga jin amsarta ba yace "Haseenah tuwo ki ka dafa?"
Kallon shi ta yi tace "Eh, da matsala ne?"
Ya na ci gaba da kallonta yace "Khadija ta ga ki na aikin nan?"
Sam Haseenah ta ma manta da abin da Khadija ta fad'a mata, sai kawai tace "Eh, me ya faru?"
Da wani irin kallo yace "Kuma ba ta fad'a mi ki komai a game da hakan?"
"A'a, wai me ya faru ne?" Ta fad'a cike da k'aguwa, a hankali yace "Shikenan kawai, zo zauna nan."
Janyota ya yi ya zaunar da ita akan cinyar shi ya na kallon fuskarta yace "Haseenah, ki yi hak'uri kinji, ina ganin laifi na ne da har mu ka yi soyayya da kai ba tare da kinsan abubuwa da dama a kai na ba, kuma hakan ya samo asaline saboda ba mu jima tare ba, sannan ni mutum ne da bai cika fad'an abin da ya shafe shi ba, amma a gaskiya ni ba na cin tuwo da dare, ba kuma shi kad'ai ba, akwai abin da ma kwata-kwata ba na cinsu kamar wake da nasan sa, sannan kinga shinkafa ma ban cika son ta ba haka, sannan kifi ma ba na cin shi da dare, wannan shine."
Bushewa ta yi da dariya ta sauka daga cinyar shi taja kujera mai fuskantar shi, da k'yar ta tsayar da dariyar tace "Miji na, ka na d'an africa, a africar ma a niger, kuma ka ce ba ka son shinkafa, lallai ka na jin dad'in ka."
Ganin ta mayar da abun kamar wasa ya sa ya d'an gimtse fuska yace "Ni dai ban son ta, na fad'a mi ki ne dan ki kiyaye."
Ita ma had'e fuska ta yi tace "To yanzu tuwon nan fa ya zanyi da shi?"
Shima dariya ya yi yace "Ku ba kun ci ba? Kawai ki samar min wani abu