Showing 21001 words to 24000 words out of 149977 words
Maminsa yanzu Tana hannu na gari Dan haka yasan koda ya tafi hankalinsa a kwance yake da inda yasan yabarta zai dawo ya sameta.
****Cikin ikon Allah da rabo daga garesa wani babban al'amarin farin ciki ya samesu na samun rabon ciki daga Zainab..
Sunyi murna sun godewa Allah musamman malam Sanda sbd yariga ya tsufa baida 'dan Kansa
Lamarin da kwata kwata bai saka raiba badan ya cire Rai daga rahamar ubangijinsa ba.
Zainab kuwa kunyar kanta ta ringa ji musamman da cikin yafara girma Aqeel ya gane.
Shi Kansa Aqeel din yaji nauyin Amma farin cikin daya shiga yafi na nauyin Dan haka sai ya zama shine yake kulawa da ita sosai.
Da Kansa yakaita asibiti akai Mata komai na ganin likita duk Bayan sati biyu.
Duk ranar zuwa ganin likita shine yake kaita ya dawo daita..
Babbar damuwarsa da rashin Jin dadinsa shine baya qasar Maminsa zata haifar Masa 'dan uwansa ko 'yar uwarsa Wanda ya tabbatarda kafin su hadu ya daukesu cikin hannuwansa ya rungumesu sai sun girma Tunda ba kusa zai dawoba,
Saidai su gansa a hoto shima ya gansu a hoto.
Labarin cikin Zainab ya samu Haj maryamah da umma Amma har lokacin Babu Wanda ya iya daukar kirantaba.
Komai na alaqarta da Yar uwarta Haj maryamah da umma yagama lalacewa sbd sun tabbatar Mata da Basu ba ita din har abada kamar yanda suka Bata zabi.
Cikinta yakai wata bakwai ta zama wata yar lukuta da ita,
Babu kalar kulawa da tattalinda Bata samu daga malam Sanda da Aqeel Wanda kejin kamar ya Ciro babyn dake cikin ya ganta kafin ya tafi Amma ba Hali Dan haka saidai yake kulawa da Mamin tasa kadai.
Ba qananun kudi yake kashewa Mamin ba da Kuma kayan baby komai order yakeyi online yasiyo yakawowa Mamin wadda takejin kamar ma Aqeel din yafita zakwadin babyn.
Haj maryamah dakeda bayanin komai daga PA dinta akan yanda Aqeel ke kashewa babyn da Zainab zata Haifa kudi ranta ya sake baci takirasa tayi Masa tas karshe hadda umma saida taji zancen ita Kuma takira Zainab din da rabon dasuyi magana tun aurenta Amma yau da kanta takirata tayi Mata kaca kaca da fada har saida baiwar Allah tayita kuka karshe duka abinda Aqeel yabata tace ya maida inda ya siyo ya karbo kudadensa.
Bai karba ba Kuma ransa ya sosu matuqa da abinda itama Mamin tayi Masa Dan haka kwana biyu saiya dauke Kansa ga kowa ya maida hankali kan tafiyarsa da batafi sati biyu ba.
Kwana biyu da baya zuwa gidan sai itama Bata nemesa ba sbd malam Sanda dake fama da ciwon ciki Dana Kai a kwanakin sosai shiyasama koda akai rigimar harma da Kiran da umma tayi Mata tana fada duk bai iya saka bakiba sbd sosai ciwon cikin ke damunsa ko bacci baya samu sosai a kwanakin.
Aqeel baisan da halinda suke ciki ba Dan sbd shima tafiyarsa tazo ga Haj maryamah tadawo sbd tafiya tasa Dan haka ya maida hankali sosai gurin shiryawa da mahaifiyarsa,
Bayason ya tafi Tana Mai fushi dashi Dan haka ya tattara lokacinsa gabaki daya ya Bata gashi itama Tana fama da nata rashin isashiyar lafiyar hawan jini ya sakota gaba.
Jikin malam Sanda ya Dan tsananta Dan sunkai a kwance yake yanzu.
Taso Kiran Aqeel yazo sukai malam din asibiti saiga Kiran umma kamar tasani ta gargadeta akan kada ta sake Shiga tsakanin maryamah da 'danta tabari su rabu lafiya cikin kauna da kulawa Tunda Aqeel din tafiya zaiyi yabarta.
Jin Yana tareda mahaifiyarsa sunata daidatawa da begen juna kafin ya wuce yasa ta fasa nemansa ta kame kanta Dan gudun sabuwar matsala Tunda ansamu sun daidata din.
Itada malam din sukaje asibiti yaga likita Amma Basu samu wani cikakkiyar bayani akan abinda yake damunsa ba andai rubuta musu test da hoto harma da wasu Yan magani tukuna kafin result din yafuto.
A hanya suka siyo maganin suka dawo gida daqyar yasha ruwan zafi da abinci kadan yasha maganin yayi sallah ya kwanta.
Sai data ga bacci ya daukesa tukuna ta fito tayi alwala jiki a mace tayi sallar la'asar Dan tun safe suna asibitin suna fama sai qarfe uku suka baro.
Itama abincin taci kadan sbd Jin duk batajin dadin jikinta da yayi sanyi da ciwon nasa Dan abune da Bata taba ganiba.
Da daddare jikinsa ya matsa sosai Allah yasa Basu kwantaba Dan haka ta rasa yanda zatai Dole takira Aqeel suna gaisawa cikin kewar juna taji Yana tareda mahaifiyarsa Dan haka saita fasa fada Masa kawai sukai sallama ta kashe ta ajiye wayar.
Magani tasake basa ya Sha sai ciwon cikin ya Dan lafa.
Ruwan zafi yasa takawo Masa yayi alwala acikin babbar roba ya zauna Yana nafilu.
Itama kasa komawa baccin tayi Dan haka tayo tata alwalar tsakar gida tadawo ta shimfida daddumar sallah a bayansa ta fara Jero nafilar itama.
Har kusan qarfe ukun dare tukuna yakoma ya kwanta take bacci ya Dan daukesa.
Da asuba ma jikin nasa tashi yayi sosai
ciwon cikin Mai tsanani ya dawo Dan haka Dole tasamo abun Hawa suka Kuma komawa asibitin saidai Basu samu ganin likitaba haka suka dawo sbd kamar kada su nufa asibiti ciwon cikin yakoma ya kwanta.
Suna dawowa itama zazzabin takeji sbd yanayinta na juna biyu ga damuwa da tashin hankalin ciwon mijinta.
Ganin Yana ciwon ciki yasata dama kunun tsamiya ta zuba a flask saita dafa farar shinkafa kawai da Mai da Dan yaji sbd ita kanta batada wani apatite na cin abinci.
Haka ya wuni a kwance Yana bacci Mai nauyi sosai sai yamma ciwon yakuma tadashi daqyar yayi sallolinsa yasha kunun kadan Amma Sam bai zauna a cikinba ya amayar duka take qarfinsa yayi qasa sosai.
Duk inda hankalin Zainab yake ya tashi Dan haka ta zauna gabansa bayan kuka Mara sauti Babu abinda takeyi sbd Babu wata mafita.
Batasan me zatayiba Kuma,
Aqeel ne gatanta harma Dana malam din Amma Kuma batason lalata Masa komai tsakaninsa da mahaifiyarsa,
Idan takirasa komaima faruwa zaiyi Dan haka saita zauna tanaci gaba da kukanta sbd duka maganin da aka rubuto Babu Wanda Basu sayaba hakama babu Wanda bayasha
Gashi sunkoma asibitin Amma Basu samu ganin likitaba ance sai emergency patient kawai zaa iya gani,
Su ankasa yarda da emergency dinne.
A wunin azabar ciwon yafi na kullum Dan haka take malam din gabaki dayansa ya sauya lokaci daya kamaninnsa duk suka sauya.
Tsananin tsoron dake zuciyar Zainab yasa kukan natama ya tsaya qarfe itama zabgewa Tai lokaci daya.
Dare nayi jikinsa yayi tsananin da bazata iya kasa Kiran Aqeel ba sai gashi Tana Kira wayar tasa a kashe
Take jikinta ya dauki rawa Tana fashewa da wani irin kuka.
Shi Kansa malam din jikinsa yayi nauyinsa bazai iya ko bude Baki yayi magana ba......
Bugun kofar gidansu taji guraren goma saura.
Bata tsaya tambayar wayeba ta nufi kofar ta bude idanuwanta ko gani basayi sosai.
Aqeel ne,.
Kallonta yakeyi kamar yanda itama take kallonsa Tana fashewa da qaramin kukan qunci ahankali.
Cikin mamaki da dan firgici yace,
"Mami lafiya?
Meya sameki?
Jikin ne?
Ina baba Malam??
Ahankali ta takaita kukanta tareda share fuskarta Tana bawa kanta hakuri da qarfin zuciya tace"
Malam dinne ba lafiya sosai tun shekaran jiya.....
What????
Mami meyasa Baki sanar daniba?
Ya Salam....
Ciki suka qarasa da sauri saidai Koda suka Isa malam din yayi nisa....
Kansa yayi da sauri Yana ambatar,
"Innalillahi wainna IlayhirRajiun
Haka jikin yayi tsanani Mami?
Innalillahi.
Kokarin kamasa yakeyi Yana cewa"
Mami asibiti zamu kaisa yanzu.
Da Kansa ya kamashi Mamin tasa ta Kama Masa suka kaisa mota yaja motar suka nufi Babbar private asibin kakarsa Haj Kaka.
Suna Isa asibiti aka karbesa da gaggawa sbd yafara nisa sosai.
Waje aka koro Aqeel din da Maminsa suka zauna kowannensu hankali tashe
Bayan fata da adduar samun saukinsa Babu abinda kowannensu yake kitsawa cikin ransa.
Zainab gabaki daya jikinta yagama saki da komai,
Zuciyarta ta riga tayi nauyi Jin take kamar kirjinta bazai dauki nauyin zuciyar ba.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
12
Zainab Tunda ta zaunar da duwawunta kan gurin zama ta sunkuyar da kanta Bata sake motsiba bare iya magana.
Zuciyarta ta Dena harbawa da qarfi sbd rashin kuzarin jikinta dayayi sanyi matuqa da Hakan tayi shiru Tana jiran hukuncin Allah akansu.
Aqeel ma kallo daya yayi Mata ya fahimci tsananin sanyi da sarewar datayi Dan haka shima ya kasa magana suka barwa Allah komai.
Haj maryamah daketa faman kiransa a waya bai dagaba sbd wayar ya Barta a mota da Haka take Hankalinta ya tashi itama sbd taji fitar motarsa da daddaren.
Takira Haj Kaka Amma ance baya can gidan Dan Haka Kai tsaye insha Allah Yana gurin Zainab.
Wurgi tayi da wayarta kan gado tareda Dan rufe ido Tana dafe goshinta qaramin tsoki na fitowa bakinta.
A asibiti kuwa komai ya lalacewa su Zainab da likitoci sukaita fada akan rashin kawosa asibiti da wuri yaga likita.
Zainab dai Bata iya cewa komaiba saidai AQEEL dinne kawai yake iya Basu hakuri Yana sanar musu da shima bai sani rashin lafiyar tasaba.
Tun suna saka ran Jin wani bayani daga likitoci bayan tarin magani da allurai da drips dasuka rubuta aka siyo Babu abinda suka sanar musu sbd malam din dai su kansu Basu samu ya farfadoba Amma dai suna saka ran farfadowar tasa Koda tsakiyar dare ne.
Anan suka cinye Daren zaune kofar dakin emergency babu Mai iya doguwar magana acikinsu...
Qarfe biyar na asuba Allah ya karbi ran malam Umar sanda Bayan ya bude idanuwansa akan Zainab Aqeel dake gefen.,
Kallonta kawai yayi tsawon sakanni kamarma baisan meyake kalloba sbd kwata kwata baya hayyacinsa na lafiya,
Akan Aqeel yakuma juyar da kwayar idanuwansa shima ya kafesa da kallo daga Hakan ya iya bude Baki daqyar yana kokarin Jan shahada ahankali ahakan Ransa ya fita.
Innalillahi wainna IlayhirRajiun
Innalillahi wainna IlayhirRajiun"
Shi kadaine kalmar da Aqeel yake iya kamowa bakinsa da zuciyarsa..
Zainab kuwa ahankali ta Isa garesa tareda zuba Masa idanuwanta dasuka Gama galabaituwa.
Ahankali Allah yabata ikon iya bude Baki tace"
Ya rasu ne Aqeel????
Sunkuyar dakai Aqeel yayi Yana kasa riqe jarumtarsa hawaye na kufce Masa masu yawan gaske.
Ganin Hakan yasata itama sauke kan ahankali tareda matsawa ta zauna bakin gadon takai hannunta na rawa ta Dora akan na malam din,
Sam idanuwanta bushewa sukayi suna Mata wani radadin yaji Amma kukan yakasa zuwa tsabar tashin hankali da duhun daya rufe zuciyarta.
AQEEL kuwa kuka yakeyi na hawaye sosai sbd rasuwar shikam tazo Masa ne Kai tsaye daga sama sbd baisan uban nasa Kuma malaminsa baida lafiyaba duk kwanakin.
Rufe gawar akai suka fito daga dakin suka zauna Babu Mai iya magana acikinsu Dan kuwa dukkansu sunyi nisa a fita hayyaci.
Ta bangaren Haj maryamah ma kuwa Bata daina kiransaba tsawon Daren sbd bai taba kwana ba a waje duk rayuwarsa
Idan dai baya gida to Yana gidan Haj Kaka Amma yau din tazo da sabon Al'amari.
Kiransa take Tana sakewa Amma baya dauka sbd wayar na mota...
Duk yanda takai ga danne zuciyarta saida ranta yakai maqura a baci tareda shiga tsoro da tashin hankalin idan ba wani abun ya samu Dan nataba,
Tanason Kiran Zainab taji idan gurinta yazo Amma zuciyarta taqi barinta Kiran dan Haka a tsakiyar Daren gaf da asuba takira umma ta sanar da ita sbd ita takira Zainab din.
Adaidai lokacinda ake fitowa sallar asuba alokacin Kiran umma yashigo wayar Zainab dake zaune kofar dakin da gawar mijinta yake, AQEEL kuwa yashiga masallacin asibitin sallah baidawoba.
Idanuwanta sunyi wani irin nauyi sosai,Babu abinda yake cikinsa sai radadin bushewa na kukan da suka gaza,
Daqyar ta iya gane sunan Mai Kiran ta daga ahankali takai kunnenta tareda Yar shaqaqqiyar sallama sbd makoshinta daya bushe tun tsakar dare har zuwa lokacinda mijinta ya karba Kiran ubangiji.
Umman na Jin Zainab ta dauki wayar Bata tsaya Jin komaiba Kai tsaye tace"
AQEEL na gurinki???
Daqyar Zainab taja numfashi tace,
"Eh....
Bayan Hakan umma Bata tsaya Jin komaiba ta rufe Zainab din da fada sosai akan bazata iya Bari maryamah ta Sabu da 'danta ba harsai ya tafi Babu sabo da shakuwa tsakaninsu,
Meyasa bazata zama sanadi na alkhairi ba saina fitina,,???
Kuma ita Maryamah data haifi 'dan batai qyashin bar Mata shi Yana yaroba sai itace zataji qyashin barin maryamah da 'dan su samu nasu lokacin suma......
Dan batasan zafi da ciwon ciki da haihuwar 'da bane shiyasa take saka son Kai a lamarin uwar data haifi 'da...
Zainab zuciyarta takusa bugawa ta tarwatse tun lokacinda rai ya fita ajikin malam sai alokacin tasamu kuka Mai karfi yazo Mata Dama nemansa takeyi Amma zuciyarta ta mushe qyam sbd girman tashin hankalin data Shiga sai gashi masifar su umman tasa kukan yasamu zuwa.
Umma cikin waya dataji kukan sai ta tsaya da mamaki Tana cewa,
"Lallai Zainab kin samu sake,
Ina fara Miki fadan shine Zaki fashemun da wannan kukan kamar wadda na kashewa miji
Wato ke bakyason fada yanzu......
Wurgi Zainab tayi da wayar da qarfi Tana sake fashewa da kuka sosai Mai bayyanarda tsananin qunci da radadin dake cikin zuciya da jininta ga wani ciwon Mara Mai qarfi daya soketa a take sbd tsananin tashin hankalin baqin ciki da qunci wani akan wani..
Irin kukan datakeyi yasa AQEEL daya kusa isowa gurinta ya qaraso da sauri hankalinsa na sake tashi sbd bai taba ganin Mamin tayi irin wannan kukanba.
Yana isowa gurinta taji nauyin zuciyarta ya qaru sbd itadai Allah ne ya saka Mata kaunarsa fiyeda komai Amma koyaushe baqin jininta da kukan da ake sakata akansa ne....
Wane tashin hankali yafi na rashin mijinta Wanda shi kadai ne gatanta,
Rufin asirinta,
Uban cikinta, tarasashi ayau Amma ko ayau din laifinta ake gani tareda gorin haihuwa da maganganu masu qunar Rai da qarin radadi akan Wanda tasamu kanta aciki yau.
Neman rikicewa Aqeel keyi da yanayinta Amma ta dakatar dashi ta hanyar dakatar da kukan nata aka Basu gawar a motar asibiti suka nufi gida.
Koda suka iso gida kusan duka dattijan anguwa wasu daga jama'arsa da dalibansa manya da yara kusan duk sun fara halarta Dan Jin labarin rasuwar tasa.
Babu Bata lokaci aka hau gyara gawar Dan janaizarsa,
Aqeel duk da matashi ne da shekarunsa Basu Gama zama na manya sosai ba dashi akai komai sbd shine tamkar Dan malam din Dan Haka kusan kowama shi yakewa gaisuwar rasuwar.
Ahaka akai janaizar Malam Umar Sanda mijin Zainab aka kaisa gidansa na gaskia.
Dangin mahaifin Aqeel din wasu da yawansu sun halarci janaizar sbd Malam din dakuma Aqeel dayayi rashin wani uban a Karo na biyu.
Gashi rasuwar ta dakesa sosai shima kamar yanda tayiwa Zainab mugun duka.
Acan cikin gida kuwa Zainab Tunda suka dawo makotanta ne a tareda ita suna tayata zaman,.
Bayansu batada dangi batada kowa da zaizo Mata.
Haj maryamah sai bayan da aka kaisa makwancinsa aka dawo Aqeel ya iya samun damar kiranta ya sanar Mata abinda yafaru.
Addua tayiwa malam din tareda nema Masa rahamar Allah daga Hakan sukai sallama.
Umma Haj maryamah dince takirata ta sanar da ita sai alokacin ta fahimci abinda yasa Zainab ta kashe Mata waya dazu Dan kuwa harta dauka zafi da Hakan matuqa.
Itama adduar samun rahama tayiwa malam Sanda din sukai sallama.
Kiran wayar Zainab din sukayi su dukan Dan Yi Mata taaziya Amma Bata shiga sbd Tunda tayi wurgi da ita a asibiti batasake bi kan neman wayarba Hankalinta baya kan wayar kwata kwata.
Da daddare gidan yakoma daga ita sai Aqeel Wanda daqyar ya iya sata taci abinci da maganin zazzabi sbd zazzabi Mai qarfin gaske ta wuni dashi dan har wani hucin zafi jikinta keyi na zazzabi...
A gidan ya kwana palon malam sbd bazai iya barinta takwana gidanba ita kadai sbd yanayinta.
Cikin tsakiyar dare ciwon Mara Mai qarfi dataketa daurewa tun safe ya taso Mata gadan gadan..
Tsoro da tashin hankalin rasa cikinta yasata kasa neman Aqeel ta zauna Tana hawaye da hada uban zufan azaba.
Cikinta wata bakwai ne tasan bai Isa haihuwaba Amma ayanda takejin wannan azabar da wuya idan ba barin cikin zatayiba.
Acan bangaren Aqeel Tunda ya shige yaketa sallolin darensa daya saba
Yana idarwa yayi adduoinsa ya zauna Yana Shiga tunanin daketa addabar ransa tun Bayan janaizar Baba malam wato jibi ne tafiyarsa UK
Yaya zaiyi da Maminsa kenan yanzu??
Ga juna biyu ajikinta Dan Haka a yanzu dinne tafi buqatarsa itada babyn Dan kuwa sunzama amanarsa yanzu,
Sun zama ahalinsa da zai tsaya musu ya zama gatansu Dan kuwa Amanar Hakan ce malam yabar Masa alokacinda ya kafesa da ido gabanin rasuwar tasa.
Yanzu tayaya zai iya tafiya yabarsu anan tsawon shekaru?
Waye zai kula Masa dasu kafin yadawo din??
Bazaiso qaninsa ko qanwarsa su taso ba acikin gata da kulawarsaba.......
Nishin Maminsa Mai qara yasashi juyawa ya kalli kofar palon Yana Dan miqewa tsaye ahankali yanufi kofar Dan tabbatarda abinda yakeji.
Wani wahalallen nishin takuma saki cikin azaba
Ba shiri ya fito Yana Kiran sunanta cikin kulawa da damuwa daga bakin kofar dakinta yace"
Mami bakida lafiya ne?
Meyake faruwa??
Daqyar ta iya Kiran sunansa Tana cewa yashigo.
Da saurinsa ya shigo Yana kallonta zaune ta hada gumi da hawaye sosai
Kusan ma azabar taci qarfinta da Haka ba wani tsaiko Tunda baisan mezaiyiba ya kamata suka fito
Allah yasa motarsa na taredashi bai aka gida ba sbd Nan din ba gurin ajiye motar Dole sai kofar gida.
Dare ne sosai Amma baiji shakkar komaiba ya nufi asibiti da ita
Duk hankalinsa yagama tashi,
Tsoro yakeji yanzu na mutuwa,
Yana tsananin son Maminsa bazaizo mutuwa ta rabasu ba yanzu,
Idan itama ta tafi tabarsa a duniyarsa baida kowa kenan Dan kuwa Maminsa itace yakejinta a jininsa tamkar itace jininta yake yawo ajikinsa.
Kai tsaye labour room akai da ita sbd da Alama haihuwace tazo Mata gadan gadan Babu shiri lokaci baiyiba.
Kasa zama yayi Tunda aka Shiga da ita gashi yakira wayar ummansa yafi so ashirin Bata dagawa duk da yasan darene Amma yasan batada nauyin bacci Kuma takan tashi itama sallar dare wani lokacin Dan Haka zaiyi wuya a nemeta baa sametaba da dare.
Magani da duka abubuwan da ake buqata aka rubuta Masa yaje pharmacy din dake cikin asibitin ya siyosu Komai ishashe Mai yawa.
Kaya akace yaje yakawo sbd haihuwace zatayi.
Da mamaki da tsoro yace,
"Mamin ce zata haihu yanzu?
Dama lokacin yayi ne?
Bayani sukai Masa na cewan preterm labor ce maana haihuwa a wata bakwai din zata sbd matsalolin da cikin yasamu gashi bai kaiba.
Da sauri ya juya ya nufi gurin motarsa saikuma ya tsaya sbd yasan Babu inda zai samu shago a lokacin.
Dawowa yayi Yana jiran afito sallar asuba dasuke kokarin Shiga shima yai alwala ya Shiga masallacin.
Ana idarwa sama sama yayi adhkar ya fito ya ja mota ya nufi gidan tsohon driver din Dadynsa da yanzu shagone