Showing 84001 words to 87000 words out of 149977 words
Abun dayakeda Isa dashi hardashi yake Bata tsoro da shakkar idan zai aminta yabar Amal din har zuwa gaba.
Boye shakkarta tayi tareda kallon Amal data dawo da kallonta akanta itama idanuwanta na sauyawa.
Gaba tayi tana cewa,
"Kinji abinda ya fada ai
nxt time din saiki hada harda gaisuwa sbd wannan haline Zaki nuna wainda yake nuni da irin tarbiyar da Kika samu,
Bansan meyasa Zaki wahalarda kanki ki wahalar daniba akan maganar Nan,
Nace Miki ki nutsu ki Cire komai a ranki Ina Nan zanji da komai Amma kin kasa tausan zuciyarki,
Wannan zafin kan naki ba komai bane agaban nasa zafin kan,
Idan kikai danyen Kai wahala Zaki fara Sha da wuri dan kuwa alokacin ne zakiga cikakken ikonsa akanki Dan koni bazan hanasaba tunda yariga yasha gabanmu.
Dining ta nufa tabar Amal din a tsaye tana binta da kallo itama,
Kasa qarasawa gurin cin abincin tayi sbd apatite data rasa take,
Juyawa tayi ta koma dakinta tareda wucewa toilet Kai tsaye.
Tubewa tayi tayo wanka ta fito ta zauna gaban mirror sai alokacin ta samu ta nutsu tadawo daidai ta fizge tunaninsa kwata kwata daga kanta.
A natse tayi shirinta na makaranta Dan idan ba ficewa tayi daga gidanba bazata Dena Jin iskarta tadawo daidaiba sbd qamshinsa daya barmusu.
Riga da skirt ta saka na embellished atmp coffee brown sai qaramin veil iya wuya Wanda take saka irinsu.
Handbag da key din motarta kawai ta dauka ta sauko.
Mommynsu ta fita itama tana saukowa ta fice.
School ta Isa Kai tsaye sbd tanada lectures har biyu a ranar.
Da farko Babu kusan kowa yayi mamakin zuwant da Kuma shigarta wadda tasaba normally sbd sun dauka tunda tana auren AQEEL ASAD shigarta zata sauya wasu harsuna matsuwa da ganinta Acikin su jallabiya masu rufe jiki sosai.
Kaman yanda tasaba batada wasu friends na musamman saidai wainda take Dan gaisawa dasu Dan Haka Babu Wanda yaga Fuskar zuwa gurinta Dan samun qarin bayani akan aurenta Haka suka wuni suka Gama ta juyo a matuqar gajiye ta nufo hanyar gida,
Sai data biya makarantar Fahat ta daukesa sbd 6 ta wuce Daman 6 din suke tashi.
Koda suka iso gida angama sallar magrib Dan Haka tana parking Fahat bangaren su mum dinsa ya wuce ita Kuma tana kokarin rufe motar Aka bude gate motar AQEEL ASAD ta shigo harabar gidan.
Shine ya tuqo motar da Kansa bama wadda ya Saba zuwa da ita bace watace daban.
Saiti da tata motar yayi parkin
Bude motar yayi yafito sanyeda black jallabiya Mai tsadar gaske daya kwanta matuqa sai kyalli takeyi ajikinsa gashi kalar ta fidda hasken fatarsa sosai.
Juyawa tayi batareda takuma kallon inda yakeba bare ta nuna tagansa zata wuce abinda duk duniyarta Bata taba tunaniba shine Jin hannunta daya riqo cikin tattausan tafin hannunsa.
Tsayawa tayi cak ba tareda ta juyoba ta fizge hannunta zata wuce ya riqo qugunta gabaki daya ya dawo da ita bayanta na gap da haduwa da kirjinsa saidai ya Hana hakan faruwa sbd bazaizo jikinsu ya Hadu dinba.
Zafi zuciyarta keyi tana Mata tafarfasa tareda faduwar gaba sbd wani namiji kaf rayuwarta Bai ta'ba taba jikintaba irin hakan,
Hannuwansa dasuka riqo qugunta takeson Kai hannunta ta cire Amma bata son hannuwanta su taba nasan Dan Haka ta sake qwacewa da qarfi saidai kaman tasake tura kantane ta hade bayanta da kirjinsa abinda baisoba ko kadan Dan Haka yayi saurin sakinta tareda dauke kallonsa akanta gabaki daya yaja baya kadan kafin ya dago ya sake kallonta da Idanuwansa datakejinsu ajikin ahankali cikin nutsuwa yakai bakinsa saitin kunnenta daga bayanta qasan makoshinsa ya janyo muryarsa ahankali yace,
"Next time kada ki Kuma fita koina batareda saninaba,
Kayan jikinta yakalla tareda sake janyo muryarsa zaiyi magana sai kawai ya fasa ya miqe tsaye tareda rabata ya wucewarsa gaba batareda ya waiwayo ba kaman bashine yayi maganaba.
Kasa motsawa tayi daga inda take tsaye sbd nauyi da zafin da zuciyarta keyi,
Qamshinsa daya bar Mata agurin yasa ta tabbatarda shi dinne dai da gaske ba iskaba,
Meye hakan dayayi yake nufi?
Yasan meyayi?
Yasan meyake fada?
Yasan da waye yake magana??
Wani abune ya tokare maqoshinta na baqin ciki da takaici.
Cikin zafi ta daga qafafunta ta nufi ciki tana zare qaramin gyalenta dayake Kama da Babu Wanda ya dauki qamshinsa take..
Tana Shiga Palo tayi wurgi dashi tana cewa,
Bilkisu ki dauki wannan bana buqatansa Kuma.
Sama ta haye tana shiga palon da idonsa tafara cin karo Yana zaune tareda mommy fararen idanuwansa kallo daya sukai ya dauke Ido batareda ya sake kallontaba.
Ganin mommyn dake zaune yasata miqa musu gaisuwar jam'i ta wuce hanyar bedroom dinta ta shige tareda bugo kofar.
Satan kallonsa Haj Zainab tayi Dan ganin yanayin yanda zai kalli lamarin Dama Wanda zata fada Masa a yanzu din.
Fuskarsa Babu Wani abinda tagane a a yanayinsa Dan Haka ta Dan sauke boyayyan numfashi tareda sake kallonsa tana hada kalaman da zata fada Masa din.
Ganin yanda taketa neman hada maganar dazata fada yasashi kallonta a natse kaman Wanda yake karanto abinda yake ranta,
"Akwai wani abun ne??
Numfashi ta sauke a fili kafin ta daure Kai tsaye ta bayyanar Masa da abinda take buqata daga garesa na barin Amal din gida kafin komai ya Dan daidaita.
Zubawa Mamin Idanuwansa yayi bayan yagama Jin abinda ta fada,
Mintina yayi Yana kallonta batareda yace komaiba kafin Kai tsaye hankali kwance yace,
"Zaki iya Mami??
Zaki iya riqeta hannunki ayanzu datake matsayin matata??
Shiru Haj Zainab tayi tana qin kallonsa sbd batasan me zatace ba amma dai koma meyene tana son abar Mata Amal din kafin ayi wata maganar a gaba.
Batayi zato ba taji muryarsa yace,
"Ok,ba damuwa,
Ta zauna din har lokacinda kike buqatan.
Da sauri ta dago takallesa sbd batayi tunanin amincewar tasa cikin saukiba sbd sanin halayyarsa.
Wata ajiyar zuciya ta sauke tana da sake murmushin da batasan lokacinda yake saukowa fuskartaba.
Kallonta yakeyi har lokacin ganin yanda amincewar tasa tayi Mata Dadi.
Dauke idonsa yayi akanta ya maida kan hanyar dakin Amal yace,
"Bazata sake fitaba batareda saniba
Idan ta taka wannan dokar zata koma can gidan a ranar Mami.
Ajiyar zuciya Haj Zainab din ta sauke tareda kallonsa tace,
"Karatun nata fa?
Zanyi maganarsa daga baya yafada Yana kallon agogon hannunsa zaiyi magana Amal ta fito daga dakinta sanyeda doguwar Riga Mara hannu tana kawowa tsakiyar palon ta dauke Kai ta sauka qasa Kai tsaye ta nufi dining.
Bilkisu ce takawo abincin da mommyn tace ta hado takawo sama anan AQEEL zaiyi dinner tareda ita.
Siddi da Amal ne kawai sukaci abinci a dining suna gamawa suka koma sama suka shige dakin Amal din dan anan siddi zatayi fira tunda Mommy na tareda AQEEL ASAD a palon.
Tunda Amal ta shige bata Kuma fitowaba har yabar gidan Bata fitoba
Tayi kwanciyar ta adaki har Siddi tagama surutunta akan AQEEL ASAD din da charisma dinsa tabar dakin Bata kulata sbd ciwon kaima surutun ya sakar Mata.
*****Daga gidan asibiti yasake komawa sbd duba ummansa da kusan so uku kenan Yana komawa asibitin a ranar.
Zaune ya taddata Jamila Mai aikinta ta shekaru tana harhada sauran Yan kayansu an sallameta zasu wuce gida da ita.
Yasan da sallamar shiyasa yazo daukan nata da Kansa.
Ko kallonsa batayiba ya Kamata ta dakatar dashi Akan zata iya da kanta.
Tashi tayi ahankali ta nufi kofa duk suka biyo bayanta zuwa mota.
Saida tashiga motarsa ya rufe Mata ya zagaya ya Shiga yaja suka bar asibitin,
Jamila kuwa saidai tabi driver da dayar motar.
Har suka Isa Babu Wanda yayi magana acikinsu sbd ya lurada ko fuskarsa taqi kalla da alama Bata son ganinsa saita sauko shiyasa bazai iya takurata ba.
Suna Isa gida har palonta ya rakata
Tana shiga ta wuce dakinta Kai tsaye tabarsa tsaye.
Bai damuba ya juya a natse yabar sashen tareda nufar part dinsa Kai tsaye,
Nanma tunda Bilkees da mufeeda sukaji dawowarsa suka shige suka qi fitowa sbd son su daga Masa hankali yarasa gane komai har sai ummansa tadawo daga asibiti tukuna zata tada zancen a gaya Mata cikakkiyar gaskiyar abinda yake faruwa.
Babu Wanda yanema acikinsu sbd yasan kome sukeyi suna sane Dan Haka Kai tsaye ya wuce bedroom dinsa yayi Shirin baccinsa ya kwanta batareda damuwan kowaba a ransa sbd kowaccensu shine yakeda iko da ita hakama Babu wadda fushinta zai Jima yasani zasu nemesa ne da kansu daga umman harsu Bilkees da mufeeda...harma da ita Amal din.
Washe gari Kai tsaye Bai tsaya batawa Kansa time ba ya shirya cikin ash Armani's ya fito cikeda kwarjini da kyansa Mai sanyi da nutsuwa.
Mufeeda yafara gani a Palo tana jiran fitowarsa itama school zata takeson ya ajiyeta sbd Bata fara driving ba da kanta.
Gaidasa tayi batareda ta kallesa ba.
Shima Bai kalletaba ya amsa Kai tsaye yayi gaba ta bisa tana kallon hanyar kofar dakin umminta tana sake Jin tsanar Amal Idon Nera sbd akanta ne gashinan iyayenta sun samu matsalar da Basu taba samuba tun aurensu.
Gurinsu ummansa ya shiga Amma Babu wadda ta fito acikinsu dan Haka ya fito ya nufi motar dazasu fita da ita Kai tsaye.
Malam Rabiu ne yayi Masa barka da fitowa kafin suka fito.
A makaranta suka ajiye mufeeda kafin ya suka wuce gidan Maminsa Kai tsaye.
A harabar gidan suna shigowa suka tadda Haj Zainab zata fita itama tareda Siddi harma da Amal dake tsaye cikin kayan bacci yauma Riga da wando masu santsi ash.
Kallon mamin takeyi datace Mata kada ta fita koina umarnin Mijinta ne.
Mamaki da bacin Rai ne Mai tsanani a kan fuskarta musamman da mommyn ta nuna aminta da hakan..
Magana zatai motar AQEEL din tashigo harabar gidan.
Daga nesa yacewa malam Rabiu yayi parking ya fita yakoma waje gurin securities.
Fuskarsa a kame ya fito motar gabaki daya kwarjininsa da kame fuskar tasa yasa dukkaninsu yin shiru Banda Amal datake Jin kamar zata fasa kuka ta juya zuciyarta na ciwo tabar gurin kafin ya qaraso.
##MAMUH#
#HOTLOVE#AQEEL ASAD#AMAL IDON NERA.
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
44
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
44
Yana qasarawo Siddi ce tafara gaidasa cikin kulawa kafin shikuma ya gaida Maminsa Yana dauke kallonsa daga hanyar da Amal tabi.
Yanayinsa yasa Haj Zainab Dan fara bayanin Fitowar Amal din akan tanason binsu ne wani Dan gurin dazasu tafi Mai mahummanci.
Dan shiru yayi Yana sauraronta kafin ya Mata kallon nutsuwa yana karanto kauna da sobon datayi na kasa takurawa 'yayanta.
Rufe Ido yayi ya bude sbd shikuma bayajin zaa samu yanda akeso din daga garesa ta wannan bangaren.
Wucewa sukai shikuma ya qarasa ciki sbd kamar Amal din Bata fahimci abinda ya fada Mata ba daga ita har Mamin.
Yana shigowa Palo su Bilkisu suka gaidasa cikin girmamawa kansu aqasa.
Amsawa yayi Kai tsaye tareda wucewa palon Mami baya yacewa Bilkisu ta Kira Masa Amal.
Da sauri Bilkisun ta nufi kofar dakin Amal tai knocking ahankali tareda bude kofar ta tura ahankali.
Amal dake tsaye tana amsa waya ranta a bace duk sbd zuwansa da maganar rashin fitarta datake ji bakin umman da safen.
Meyake nufi da nuna wannan ikon nasa akanta?,
Yaje can ya nuna akan mahaukaciyar matarsa data Gama mutuwa a sonsa Kamar yanda Siddi datakeda lokacin iya sanin labarinsa tafada.
Jefarda wayarta tayi kan gafo tana juyowa ta kalli Bilkisu kyakkwar fuskarta a hade ta zuba Mata ido tana jiran Jin abinda ya kawota.
Bata qarasa shogowa gabaki dayaba dakin ta Dan sassauta muryar sbd Yana palon Na sama zai iya jiyosu tace,
"Auntie Amal Maigidan ne yake kiranki....
Wani kallo ta jehowa Bilkisu tana kokarin danne fushinta sbd kada ta sauke akanta tunda batada laifi Amma Kuma maganarta tayi mugun tinzirata da mamaki tace,
"Waye maigidan?
Kuma na wane gidan?
"Maigidanki Auntie.
Rasa abin fadawa Bilkisun tayi sai kawai ta nuna Mata Kofa da idanuwanta dasuka Dan fara sauyawa tai Mata alamar ta fice daga dakin.
Juyawa Bilkisu tayi tana sake kallon Amal sbd Koda take Yar aiki me Kai sako bazata taba iya zuwa gabansaba tace Masa Amal din ta korota da sakon.
Tsayawa tasake bayan takai kofa ta waiwayo tana rasa abin fada ko yi da idan ta dawo Masa da rashin amsa ko bada tabbacin Amal din na zuwa,
"Idan naje me zance Auntie??
Rufe fararen idanuwanta tayi tana sakin qaramin numfashi Mai zafi sbd ciwon kai Bilkisun zata saka Mata da bacin ran zancenta akan Wanda yake cinta,
Toilet ta juya kawai ta wuce tana danne zuciyarta daga bugawa akan rashin hanata fita fa ake magana,.
Mommy datake cewa saiya bada izinin komai nata yanzu idan ta tambaya,
Ta hakura da duk abinda zaace saita tambayesa Dan Babu ranarda takejin zata iya zubar Masa da kanta tayi Masa hakan.
Bata bawa Bilkisu amasaba ta shige toilet tareda bugo kofar,
Bilkisu na ganin hakan jikinta yayi sanyi ta juyo tana Dan hada abinda zata fada akan sakon.
A natse cikin girmamawa ta Dan tsaya nesa dashi kadan zatai magana ya katseta da tausasshiyar muryarsa Mai nutsuwa da kamewa yace,
Kije kawai.
Juyawa tayi tabar gurin Babu Bata lokaci ta sauko kasa Takoma kitchen gurin aikinta.
Wayarsa da ake Kira yakalla yaga sunan Al-Amin Kai tsaye ya dauka a natse cikin rashin Jan zancen yace,
"Bazan shigo office da wuri ba akwai abinda zanyi ka rage schedules dina na yau.
Kashe wayar yayi tareda ajiyewa gefensa ya Dan rintse idanuwansa ya bude batareda ya waiwaya ko kadanba ya kalli hanyar dakin nata.
Wanka tayo tafito daureda towel blue tana kokarin zaunawa gaban madubi wayarta tayi ringing.
Kamar bazata dubaba sai Kuma ta juya ta dauko wayar a kan gadon
Sunan mommynta ne Dan Haka ta dauka Mai tsaye ahankali tana cewa,
"Naam mommy.
"Amal akwai takardunku da muka manta na process din ganin likitanku da zaayi,
Kiduba suna kan gaban mirror ki bawa Bilkisu takaiwa Taju yakawon yanzu Ina jiransa a office zaa karba.
"Ok mommy" tace ahankali tana nufar kofar dakinta da wayar ahannunta ta nufi bedroom din Mommyn dake kusa da nata.
Gabaki daya ta manta dashi takuma San Babu kowa agidan
Ko akwai Daman iya sune suke hawawo sama.
Dakin ta shiga tadauko takardun ta nufi stairs zata qwala Kiran Bilkisu hancinta ya shaqo qamshinta a bayansa da sauri tayi saurin juyowa sbd firgitar datayi Kuma Bata lura da mutum a palon ba data fito.
Saurin ja da baya tayi tana Masa wani irin kallon mamaki da bacin ran ganinsa gabanta a yanayin datake ciki.
Shi kansa baiyi marmarin sake yimata kallo na biyu ba bayan na farkon da yayi.,
Baya tasake ja tana kokarin kaucewa ta wucesa komawa bedroom dinta fuskarta a daure,
Dawo da ita yayi gabansa ya tsayar ya kalli fuskarta shima tasa Fuskar a matukar kame Wanda yasata Dan sake kokarin ja da baya Amma wani kallon daya jefata dashi yasata kasa daga qafafun nata tana sake daure fuska gashi ya tsaya gabanta ta yanda bazata iya wucewaba sai jikinsu ya Hadu kokuma idan ba turesa zatayi ba
Cikin biyun bazata kaunaci ko dayaba sbd data iya Kai hannu jikinsa harma ta turesa tafisan tayita tsayuwa a gurin idan ya gaji ya janye ta wuce.
Son yimata kallon tsaf yakeyi Amma bayason hakan sbd tabbatarda maganarsa akan tsayuwa idan yayi.
Muryarsa Mai tattareda nutsuwa da bayyanarda tsayuwa da rashin son mamaita magana yace,
Bana maimaita zance wa iyalina,
The 3rd time da Zaki Kuma fitowa daga dakinki da sleeping dress ko makamancinsu shine last time da Zaki kwana a gidan Nan....
Jikinta ya jefawa wani kallon takaici tareda dauke Kai zaiyi magana ma saiya fasa kawai ya juya yawuce fuskarsa a daure.
Direct sauka yayi ya fice daga gidan gabaki daya.
Kasa magana ma tayai bare motsawa daga inda take tsaye tsabar takaici da baqin cikin yandama ya ganta ahakan Amma yake Mata kallon wulaqanci da wannan maganar.
Wani numfashin baqin ciki ta sauke ta juya a zuciye ta sake qwala Kiran Bilkisu wadda taji na farkon Amma takasa hawowa sbd Yana Nan din.
Da sauri ta hawo ko magana bataiba Amal din ta miqa Mata takardun ta juya ta nufi dakinta tana cewa,
"Ki kaiwa Taju yakaiwa mommy office yanzu.
Dakinta ta qarasa shigewa tareda rufo kofar da qarfi tana Jin zuciyarta na daukan zafi.
Shiryawa tai cikin Riga da skirt na atampa ta daga wayarta takira Mommy akan zata tafi makaranta da sauri Haj Zainab ta katseta da cewa,
"Karki fita Amal ko gate karki tafi bare fita idan har kinason a samu a lallabasa ayi tafiyar Nan dake tunda dake aka tsarata,
Ciwon maran Nan naki da rashin haihuwar siddin Nan Ni kadai nasan yanda nayi aka samu zamuga wannan likitan bayan kina gani daqyar muka samu appointment din nasa,
Yanzu duk Bayan nagama wahalar Nan ga aure yazo ya hau kanki da mijinda babu Fuskar muyi yanda Siddi keyi,
Tunda ya Hana fitarnan ki nutsu wlh musamu ya yardar Mana tafiyar Nan idan lokaci yayi sbd kema kisamu saukin wannan ciwon naki na Mara
Idan Kuma kikai zafin Kai wlh kece Zaki wahala AQEEL ASAD bazai bar tafiyar nan dakeba Kuma Dole mu tafi Babu abinda Zan iya Miki...
Dan Haka ki nutsu.
Kashe wayarta tayi bayan tagama fadan hakan tabar Amal din da waya a hannu cikin yanayi na damuwar data fara Bata mamaki,
Meyasa mommy ta dauki lamarin nan da zafi ne?
Shakkarsa takeyi kome?
Tayaya tana matsayin Maminsa kaman yanda yake fada Amma Kuma taji shakka ko tsoroma zata ce.
Jefarda wayarta takuma yi Akan katon gadonta tana zaunawa kan kujera zuciyarta na zafi da bacin Rai.
Ita gabaki daya ma rayuwarta neman takeyi ta sauya Mata,
Tana rayuwarta cikin kwanciyar hankali yanda takeso Babu damuwa bare takura Amma zuwansa rayuwarsu komai ya lalace musamman ita da aka tsayarwa rayuwa ta hanyar Dora Mata wannan nauyin da rayuwar auren da kwata kwata Bata shiryaba bare da Wanda bataso.
Haka ta zauna shiru a daki wuni daya ita kadai ranta sai sake daci da ciwo yakeyi.
Sai yamma su mommy suka dawo suna isowa gate cikin mamaki suke kallon sabbin securities da aka sauyawa gidan gabaki dayansu su biyun masu canja shift.
Securities biyu aka Kuma kawowa marasa sauki ko kadan
Gasu musulmai Amma ko kalma daya ta hausa basaji.
Wasu irin sabbin dokoki masu qarfin gaske suka taho dasu daga maigidansu dayasa aka kawosu Nan din,
Barka da zuwa sukaiwa haj Zainab din da siddi wadda ke Mamakin rashin daukan Renin AQEEL ASAD gameda iyalinsa.
Haj Zainab din dataji AQEEL ASAD ne yasa aka kawo sabbin securities shiru tayi kawai batareda tace komaiba
Itama daga yanzu tsayawa zatayi ta ringa kallon ikon Allah.
Zaune Amal take a palon qasa tana Dan chats da wayarta suka dawo din
Sannu da zuwa tayi musu kafin suka hau sama gabaki dayansu Siddi na Mata bayanin tafiyar zuwa qarshen watane zasuyi ta.
Gyadawa siddin Kai Kawai tayi tana cewa,
"Ok.
Amma a ranta batajin zata iya tambaya