Showing 135001 words to 138000 words out of 149977 words

Chapter 46 - IDON NERA BY MAMUHGEE CMPLT.txt

25 Nov 2024

6555

kwata harda tsoron wannan dalilin yasa taqi yarda da tarewar Amal din tun lokacinda aka daura auren.


Meyasa zai Mata Haka?


Uncle Lulu ne yayita Bata hakuri akan daukan kaddarar cikin.


Cikin takaici da kunyar yanda Suka samu kebewa aka samu cikin ta kalli Amal a qule tace,


"Bazaki bude Baki ki gayan cikine ajikintaba kokuwa???


Sanyi jikin Amal yayi tunda Babu tsira Babu dabara saita daga Kai ahankali wasu hawayen nakuma gangaro Mata.


"Wata nawa?" Mommy tasake tambaya bacin ranta da baqin cikinta na qaruwa.


Kasa magana Amal tayi dan bazata iya bude Baki ta fadaba kunyar tariga tayi Mata yawanda fada ma sake cusawa Kai kunya da damuwa ne.


A tsawace mommy tasake tambayar wata nawa ne cikin..


Anty Fareedah ce data karba takardar scanning din Dr tayo lokacinda zasu taho ta basu


Batama budeba sai alokacin ta bude tana cewa,


"Ga takardar scanning din bari a duba.


Budewa tayi tana karantawa taga cikin Kam Yana wata uku cikin koshin lafiyarsa.


Karantowa mommyn tayi


Mommyn tasake yin shiru tana rasa abin fada.


Duk barikinsu da budewar idonsu Allah yasani Bata taba shaawar yayanta su samu ciki tun suna gidaba Koda kuwa na aurene.


Tana Nan tana lissafin Shiri da gyaran da zatayiwa 'yarta ayi bikin alfarma duniya ta sheda ta aurar da sauran dayar 'yarta kaman yanda akai komai na alfarma a auren Siddi na farko Dana biyun Amma Ba wannan Damar itada AQEEL sun wargaza komai da rashin Hakurinsu Wanda batama buqatan sanin yanda sukai abubuwansu.


Amma babban takaicin da mamakin shine Rena Mata wayon da Amal tayi Dan tasan AQEEL tsaf idan tashine bazai boyewa kowa komaiba.


Tana tinanin ko Gama sanin juna basuyiba bare afara Tunanin tarewar Ashe itace Yar wahalar datake tinaninta ita kadai.


Kasa wata magana tayi sai Uncle ne daketa tausasa maganar sbd yanda Amal ke kuka da yanda tashiga wani irin kunya da damuwa sosai.


Miqewa Mommyn tayi kawai ta haye sama ta shige dakinta ta rufe idanuwanta na sauyawa sbd shikenan AQEEL yayi musu daurinda haukarsu su dukan bazata warware alaqarba da ko ita duk da tana tsananin son jika bataso yazo a wannan hanyarba Kuma duk yanda bataso dinba bazata taba yarda ayiwa yarta abortion ba Koda su umma zasu sheganta cikin ne bazaa taba Mata yartaba Amma Kam wlh daga AQEEL din har Amal sunci Amanar yardar datayi musu Dan taji zafin wannan abin sosai,bakuma komai ne yayi Mata zafinba kaman yanda Amal ta boye Mata da ciki ajikinta har tsawon wata uku sai takejin kanta kaman uwar data Gaza da tarbiyar yayanta tunda har akai ciki a gidanta tana sake da Baki Bata saniba.


Siddi ce taja Amal ta rakata har dakinta da Bilkisu tagama gyarawa sbd sanin yau zasu dawo din.


Suna shiga dakin Siddi ta Dan rungumeta ta sake rarrashinta tareda qarfafa Mata gwiwa da nuna farin cikinta sosai akan samuwar cikin tinda ai abin rabone gashinan ita tana nema takasa samu Allah Bai nufaba.


Bayan fitar siddi ruwa Mai Dan sanyi Bilkisu ta kawo Mata tana Mata sannu dan duk abinda aketa yiwa fada a palon tanaji Kuma itama taga cikin itama Kam gaskia tayiwa Amal din murnar samun cikin sbd harga Allah AQEEL ASAD mutumin arzikine.


Kasa Shan ruwan tai ta zauna bakin gado tareda rafka wani irin tagumi tana Shiga tinanin yanda nasa familyn zasu tinkari al'amarin.


*****Umma Al-Amin na Isa harabar gidan Bilkees na fitowa daga sashenta tareda mufeeda suna cikin nishadi da walwala tareda kwanciyar hankali sun samu rayuwarsu yanda sukeso.


Key ne a hannun mufeeda na motar da zasu fita da ita


Suna ganin umman Cameroon Al-Amin na rikota tana fitowa mota duk a yamutse take cikin baqin ciki da tashin hankalin abinda Allah ya hukunta musu.


Mufeeda Yi tayi kaman Bata lura da umman da a keta faman kamowaba ta Isa mota tashige tana cewa rigimar tsohuwar Nan tayi yawa,yanzu Haka wata masifar suka sake janyowa kansu.


Bilkees kuwa cikin kirsa ta nufi umma tana cewa,


"Lafiya kuwa?


Meya sameta?


Cikin motar take sake kalla tana cewa leqawa tace,


"Ina umma?


Ko hawan jinin ya tashi ne?


A kufule da tsananin takaicinta umman ta kalleta tana debewa rayuwar datakeyi a garin Lagos albarka tana cewa,


"Wlh Bilkisu da Aurenki gwara Babu,


Son abin duniyarki yasa bakya ganin komai sai rayuwar qarya gashinan kin ja mana hada iri da mugun abu,


Duk da kema wlh mugun abun ce hada iri dake ko masifa da asara gashinan yarki tana ganina cikin wannan halin tadauke Ido ta shige mota,


Tunda muka hada iri dake ai hada iri da Idon Nera shima ba komai bane tunda dukanku masifar ce.......


Tunda umman ke magana Bilkees ke Dan yamutsa fuska tana kosawa da jarabar tsufan umman saidataji kalman data tsayar da gudun jininta da qwaqwalwanta ta zuba Mata idanuwanta gabaki daya a hargitse ta katseta da cewa,


"Wane irin kike maganar zaa hada da Idon Nera????


Kai tsaye umman Dan qunsa Mata baqin cikin datake fatan yasa kanta ya juye gabaki daya su huta tace,


"Tsohon cikin Mijinki ne a jikin Amal Yar gidan Zainab....


Mufeeda dake jinsu a firgice ta fito mota tana isowa gurin qafafunta na neman hardewa zatayi magana.


##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*🔥


Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*🔥


Billyn Abdul


*IDON NERA*🔥


Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*🔥


Safiya huguma


*KI KULANI*🔥


Miss xoxo


Littafi daya---400


Biyu---600


Uku----800


Hudu-----1k


Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171


Maryam sani


Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪


*Ina yan uwa 'yan nijer?*


*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA


biyu---650CFA


uku----850CFA


hudu----1050 CFA


Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*


*Thanks for choosing us*🔥


71


*_Arewabooks@Mamuhgee_*


71


Kallon takaicin umma tayiwa mufeeda data iso gabanta jiki na rawa tana sake Tambayar umman abinda ta fada,


Bilkees da kunnuwanta ke Jin wata jiniya na qara cikin kanta itama sake maimacin maganar umman take jira sbd abinda ta fada a kwai Yar rudarwar tsufa suke gani.


Al-Amin dake gudun ta tambayesa da kanta yakasa Mata qarya juyawa yayi ya shige mota da hanzarinsa yabar gidan Yana Jinjina rigama irinta umman Cameroon Dan yanda ta fada din da gayya yasan so takeyi ta cinnawa Bilkees din hauka.


Mugun kallo umman ta sake jifan mufeeda dashi tana cewa,


"Da kikaji ubanki zai sake haihuwar wata 'yar ko 'dan shine Kika fito kikazo gabana sbd muguwar tarbiyar da uwarki tai Miki kenan Amma farko da Kika hango ni ranga ranga ko kallo ban ishekiba,


Wlh Bilkees kinci Amanar AQEEL da Kika lalata Masa tarbiyar 'ya,


Ai duk hakan mukewa kukan wannan cikin na zuriar Zainab ance azabarwa 'yaya uwa ta gari gashinan Muna gani akanki


Duk iliminsa da addininsa da iya kokarinsa akan tarbiyantar dake da 'yarsa bayan idonsa wargazawa kikeyi.,


Ai Allah yaqarama da Amal din tasamu ciki tunda ke kinzama shashashar banza da wofi.


Mufeeda ce ta katse umman da cewa,


"Haba umman Cameroon sai magana kikeyi kina tsine tsine batareda kinsan komaiba,.wayace Miki Amal Idon Nera nada ciki?


Cikin wata nannauyar murya me kokarin Hana Kai bugawa Bilkees ta katseta da cewa,


"Idanma tanada ciki wlh ba na mijina bane saidai idan a wajen mazan dakewa uwarta rawar qafa ta samoshi.


Sabon kallon firgici umma tayi Mata tana sake tabbatarda Bilkees rufa rufa akai Mata ta amsowa jikanta ita Dan akuwa alamu sun sake nunawa batada hankali,


Wannan masifa tayiwa 'dansu yawa Mata biyu Babu wadda ta fito hannun albarka gashi zaa Tara musu 'yayansu,


Ita Bilkees hanyar komawa Cameroon take daukowa kanta Dan kuwa ko su dasuke iyayensa duk abinsu bazasu iya sheganta cikin Amal ba Dan yanda taga AQEEL akan cikin ko ita tsaf zai maidata Cameroon ita data haifi uwarsama bare wannan mahaukaciyar matar tasa.


Kallon Bilkees tayi tace,


"Wallahi tallahi haukarki ta tsaya a iya Nan


Idan Kika qi Allah yasa kiyiwa kanki duk mu huta Daman ke mungaji dake,.Ina dalili Haba,mata kullum sai hauka daban daban kinbi kin ishemu mun rasa da balai da masifar Zainab zamuji kokuma da taji jarabar.


Ciki dai Amal Idon Nera cikine da ita Kuma na AQEEL ne, dan Allah ki haukace a kaiki gidan mahaukata sai kowa ya huta muji da masifar Zainab kawai.


Gaba tayi abinta tana hadawa daga Bilkees din da uwarta data cuceta akai Mata rufa rufa har Zainab da sunan duka Idon Nera tana debe musu albarka abin ya isheta ya ishi tsufanta.


daga Bilkees har mufeeda kasa motsi sukayi sbd kashesu da umman tayi da maganganunta da Babu wadda suka gane fes kaman maganar cikin AQEEL a jikin Amal Idon Nera..


Mufeeda da batada taurin zuciya irin na umminta Hannu ta Dora akai tana fasa kuka tace wlh umme shege Suka kwaso zasu maqalawa daddyna,


Umme Dan Allah karki Bari ta laqawa daddyna a hadani da wani jinin ace ubanmu daya Dan wlh ban yarda babyn daddyna bane.


Bilkees gabaki daya kanta da hankalinta tsayawa sukayi cak Bayan jiniya Babu abinda takeji a kunnuwanta da cikin kanta..


Tabbas an gunguma Mata babbar cuta da munafurci a gidan Nan,


Su umma suna sane da AQEEL Yana tareda Amal idan har umman Cameroon Kai tsaye zatace cikin AQEEL ne tabbas


To suna saneda meyake faruwa kenan akai shiru aka munafurceta sai yanzu taji wani maganar ciki kawai Rana tsaka,


Cabdijam


Ai kuwa wallahi tallahi bazata yardaba tafison a masifa ayi balain da kullum umman Cameroon ke kira idan yaso daga cikin ya zube,masu hawan jini ya Haye Suma su zube,masu bugawan zuciya su buga su wuce ita kanta dasukewa kirarin mahaukaciya tayi haukar a kaita gidan mahaukata Amma wlh saita Rama wannan abin.


Wato har tsohon ciki kaman yansa umma tafada.


Sbd sunason haihuwar batayiba shine suka juya gurin Amal tasamu sbd mutuwar zuciya irin tasu....


Huhmmmnn" ta sauke numfashi Mai tsananin zafi da tiririn zuciya ta fizge key din mota dake hannun mufeeda daketa faman kuka komai batace ba ta nufi mota ko ganin gabanta sosai batayi.


Tana fadawa motar ta tada


Da sauri mufeeda dake hawaye ta iso ta shiga itama ko Gama rufe motar batayiba Bilkees ta fizgeta da mugun gudu daman masu gadi sunbar Mata gate din bude sbd Al-Amin daya fita da mota itama sunga fitar zatayi shiyasa Basu rufeba.


Tana Hawa titi Kai tsaye ta daga wayarta takira Habib daya Saba Mata aikin Yan Media.


Yana dauka muryarta na fidda wani zafi tace,


"Yan media zaka tura gidan Idon Nera tonan asiri zaayi musu 'yarta Amal tasha nono daya da AQEEL ASAD yanzu Kuma tayo ciki wani gurin tace nasane,


Ka tabbatarda wannan labarin ya yadu a ayau dinnan Kuma a yanzu bada jimawaba a tura Yan media gidan suyi Mata tonon asiri da wannan labarin..


Shiru Habib yayi yana cewa,


"Bakowane labari fa Yan media ke zuwaba,


Wannan abinda kika fada bekai ace sunje dnba sbd abune da kusan koina Ana samun hakan,


Suna daukan labaraine akan abubuwan dasukasan Yana zama tamkar abin al'ajabi,


Sai Kuma idan na manyan masu kudine da duniya ta sani,


AQEEL ASAD Yana daya daga cikinsu Amma Kuma fidda wannan labarin ga media wlh babban hatsarine garemu da wainda ma zasu buga labarin dukanmu AQEEL ASAD bazai barmuba.


Cikin baqin ciki ta katsesa da cewa,


Ina ruwanka da abinda zai biyo baya kawai ka tabbatarda an watsa zancen yanzu Yan media din su tafi gidanta Dan suna samun labarin gidanta zasu nufa yanzu Dan wlh yau sauna cinnawa gidan Nan wuta.


Ko nawa ne zanbada,


Zanbaka kudinda zaka bar qasar kaje hutunda sai komai ya lafa yanzu nakeson wannan aikin banason Bata lokaci.


Kashe wayarta tayi tareda wurgi da ita bayan motar zuciyarta na wani irin tafasa kanta na neman kuncewa.


Mufeeda ma Jin abinda umminta zatayi saitaji sanyi ta dakatarda hawayenta sbd hakan zaisa koina cikin bazaikaiba da duniya ta sheganta auren da cikinma,


Daddynta ma idan yayi fushin Dan lokaci zai yafewa umminta tunda Yana sonta itakuma Daman baya fushi da ita kasancewarta tilon yarsa idanba yanzu da akeson kawo Mata wani mugun zancenda bazai karbu ba ta hada uba daya da 'dan karuwa ko 'ya.


Gidan Idon Nera ta nufa tana zuba wani irin gudu da mota kaman wadda ta rasa kanta gabaki daya,.


Babu abinda takeson gani kaman tai ido biyu da cikin jikin Amal tagansa.


Al-Amin kuwa ganin umman Cameroon ta fadawa Bilkees maganar yasan akwai matsala Dan Haka yana baro gidan Kai tsaye asibiti yakoma ya tadda Haj Maryamah ma ta Dan dawo daidai Amma numfashinta ahankali take yinsa ta nace akaita gida kawai.


Ganin yanda AQEEL din Kansa ya Dan dauki zafi yasa Bai sanar dashiba Kai tsaye yayi shiru tukuna Saida suka shiga mota suka Kama hanyar gida.


Shiru yayi yanata juya zancen to Amma ganin idan saisunje gida Kuma yafada Masa su dawo kaman lokacin kila wani abun yafaru to Amma sbd baida tabbacin ko Bilkees ta fita ko tana gida sai yabari idan sun Isa yaga batanan din ya fada Masa ko kila gidan IDON NERA ta nufa Dan yasan Allah ne kawai zai Hana Mata zuwa gidan.


Suna Isa Ana nude musu gate ko shigowa basuyiba ya hango ba motarta a harabar gidan Kai tsaye ya juyo ya kalli AQEEL din cikin damuwa da fargaban inda taje yafada Masa abinda ya faru.


"Wat" AQEEL yafada Yana kallon harabar gidan ba motarta ko umma Basu tsaya ajewaba Dan ko qarasa shigowa basuyiba yace Al-Amin ya juya zuwa gidan Maminsa.


Shiru AQEEL yayi Kansa na daukan wani irin zafi Wanda irin hakan idan ta faru shiru yakeyi Dan alamar tsananin bacin Rai ko tashin hankalinsa shiru yakesashi.


Kallo daya Haj Maryamah tayi Masa tasan yau 'yar wahalar matarsa tayi haukan taba wannan jarababben cikin kila harsu saisun sheda fushinsa da ita kanta Bata taba ganiba Dan na yau din yafi na kullum.


Dedeta numfashinta tayi dan dolenta ta Kama kanta sbd Allah ya hutar dasu Cikin sauki mahaukaciyarcan zata musu fadansu da bazasu iyaba Dan gudun fushi da bacin Ransa.


Wayarta ta daga ahankali ta saka Kiran ummanta taca a Aiko Mata driver yanzu yazo gidan Idon Nera ya daukota ya dawo da ita gida Dan ita ko gidan bazata iya shigaba gwara driver yazo ya juya da ita.


Ummanta najin hakan tasan wani balain Yakuma bullowa tunda taji Maryamah a gidan Zainab Dan Haka da kanta ta biyo driver din sukaje daukan Haj Maryamah din.


Bilkees dayake ta tsaya cire kudi masu yawan gaske tabawa Habib kafin ta wuce gabaki daya baa hayyacinta takeba shiyasama har lokacin Bata Isa gidanba.


Amal data Gama kuka ta rarrashin kanta tayo wanka tareda alwala tayi sallah tana idarwa ta fito ta nufi dakin mommynta jikinta a sanyaye.


Tana tura kofar dakin mommyn zata fito itama.


Kallonta tayi tana sake kallon cikin daya fito a straight doguwar Rigar data Sanya da hula.


Ita kanta Mommy kunyar cikin takeji shiyasa abin yazo Mata a wani iri.


Sun shammaceta,sun Kuma Bata mamaki iya mamaki wlh.


Wucewa zatayi Amal din ta riqota da sauri tana sake Mata hawaye cikin sanyin murya tafara Bata hakuri tana kokarin fada Mata lokacinda AQEEL yafara saninta...


Dakatar da ita Haj Zainab din tayi tana cewa Bata buqatan jin lokacinda suka zama Ma'aurata.


Siddi ce ta fito ta qaraso tareda riqe mommyn itama tana Bata hakuri tareda tinatar da ita jikan datake buqatane yazo maimakon tayi murna Kuma sai tana fushi Bayan itace taketa rokon Allah yabata jikan gashin yabata tunda gurin roka jikan kawai take fada bawai tace ga wadda takeson ta haifo jikanba.


Batace komaiba amma yanda ta Dan sake kallon Amal da cikin yasa Suka fahimci bawai cikin ne batasoba kwata kwata yanda komai na yanayin yazo.


Saukowa sukayi Suka nufi dining Siddi na riqeda Amal datace batajin cin abincin Amma sbd kallon da mommy tayi Mata yasata saukowa taredasu cin abincin.


Suna saukowa Anty Fareedah da uncle Lulu suka shigo palon ko dining Basu qarasaba Bilkisu ta shigo tana kallon Uncle Lulu tace,


"Hajiyar Mahaifiyar Sir AQEEL ce ta iso tana harabar gida.


Rintse Ido Haj Zainab tayi ahankali sbd tasan Daman zaa Rina,


Tasan saisunzo gida sbd bazasu taba karban cikin nanba,


Tasani sai sunzo sun aibata cikin da ita da yayanta a gidanta Dan Haka itace tafara nufar kofa tareda uncle Lulu kafin su Amal din gabaki dayansu Suma Suka bi bayanta.


Umma kuwa isowarta kenan daukan Haj Maryamah da Basu Riga sun isoba Dan tafisu kusa da hanyar gidan akan ta inda suka biyo su.


Motarta Suka nufa dukkaninsu itama tana ganin sun tinkarota ta fito fuskarta a daure tana kallon cikin Amal dayake tsole idanuwanta.


Kafin suyi wata magana motar Bilkees ta kunno kai cikin harabar gidan da baa Gama rufe gate dinba cikin wani mugun gudu daga nesa ta hango Amal da mommynta da umman Cameroon guri daya ga cikin da idanuwanta tsabar baqin ciki da fita hayyaci suke nuna Mata kaman yanzu zaa haifesa Kai tsaye Bata tsayaba ta danne motar tayi kansu


Mufeeda wani razanannan ihu tasake tana Kiran sunan ummin tata Amma idanuwan Bilkees sun rufe so take tayi cikinsu da motar matsalarta taqare daga yau din idan yaso taje gidan yari ta yarda, Dan kuwa Amal Idon Nera da Zainab Idon Nera sai umman Cameroon sune babbar matsalarta a yanzu.


Cikin mummunan tsoro da tashin hankali da gigicewa mufeeda ta fizge steering motar Suka daki motar Haj Zainab dake gurin take duka motacin suka farfashe da tasun data Haj Zainab.


##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*🔥


Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*🔥


Billyn Abdul


*IDON NERA*🔥


Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*🔥


Safiya huguma


*KI KULANI*🔥


Miss xoxo


Littafi daya---400


Biyu---600


Uku----800


Hudu-----1k


Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171


Maryam sani


Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪


*Ina yan uwa 'yan nijer?*


*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA


biyu---650CFA


uku----850CFA


hudu----1050 CFA


Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*


*Thanks for choosing us*🔥


72


*_Arewabooks@Mamuhgee_*


72


Umman Cameroon datayi suman tsaye tareda saddakarwa zuwa lahira tuni qafafunta Suka fara rawa tana zare Idon hankalinta na kasa dawowa jikinta da abinda taga Bilkees taso aikata musu,


Haj Zainab ma gabaki daya ta shiga mummunan tsoro da tashin hankali tareda rungume 'yarta datasan sbd ita Bilkees din takeson kashesu,


Amal kuwa tsabar tashin hankali da firgita kullewa mararta tayi take ta rige cikin tana neman durqusawa jikinta na rawa.


Al-Amin da kusan saura kadan shima yayi cikin su Uncle Lulu gurin buge mota Bilkees din daga Yi kansu Amal bugun motar Bilkees din yayi tasu suka tadan fashe daga gaban.


Haj Maryamah data rikice gabaki daya alokacinda Suka dannowa motar Bilkees data rigasu shiga Dan kusan tare Suka shigo layin Amma tarigasu Shigewa gidan akan idonsu tayi kansu umma tini jinin haj Maryamah yakusa kaiwa dari biyu da 'dori sbd ganin ummanta da zata tafi lahira ba shiri sosai ta firgita tashiga mummunan tashin hankali.


AQEEL daya Gama girgiza matuqa shima Yana fitowa motar Kai tsaye Amal dasu Mami ke tallafowa ya nufa ya taro jikinsa Yana Kiran sunata da wani wata shaqaqqiyar muryar da tsananin bacin Rai da zafi Mai tsanani suka dashe Masa ita.


Ganinsa yasata bude idanuwanta akansa tanajin tsiwon mararta na qaruwa kafin kace me sai jini yafara biyo qafafunta.


Wani mummunan tashin hankalin da Babu Wanda ya taba Tunanin zai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login