Showing 30001 words to 33000 words out of 149977 words
kyawun halittar da Allah yayimiki🥰
Wai kinafama da pimples da spot afuska amma haryau baki nemi mg's ba🤔duk Mai tantama akan kayan gyaranjiki yacire mg's domin babu shakka sudin na dabanne indai problem dinki matsalan fatane yar'uwa kijaraba koda soap dinsu bi'iznillah zaki godemin👯♀️kayansu ga kamshi inkinjaraba kinga yanda suke na tabbatar bazakiso su Yanke Miki ba🤩08062991549 anatayi Baku sisters kusamu kugwada koda b duka kit din na gyaranjiki ba zakuga sauyin da fatarku zata samu cikin lokaci kalilan🥳jikin yazama so fresh ko Ina kikashiga kita glowing fatarki na walwali kamar madubi😘keda kanki zakina burge kanki balle wasu🤗08062991549
Adade anayi sai gaskiya sannan siyan nagari Maida kudi gida ❤️
Duk Mai bukatar products din mg's kutuntubi wadannan numbers din domin tasune kawai zaku samesu🙏
Chat 08062991549
07046881166,07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Team glow🧖♀️
Yauwa nace ba masu bukatar zuma original munadashi mekyau ba hadi Mai bukata yayimin mgn 08062991549
***********
Haj Maryamah na tsaye na kallonta cikeda zafi da dacin zuciya da wani mummunan nauyi a zuciyarta zainab din ta fice daga gidan rungume da yarta,
Babah dake gefen Haj Maryamah tsaye cikin shirinta tsaf na tafiya Cameroon duk jikinta neman mutuwa yakeyi da ganin samu da Rashi Dan kuwa da anbata 'yar saita Gama biye biyenta inda takeson zuwa kafin ta Isa Cameroon din.
Masu gadin gidan dasuka San zainab tun kuruciya da girma suna kallon wannan tashin hankalin zuciyoyinsu na kunci ta tafiyarta da 'yarta,
Babban tashin hankali da tsoronsu har ita Haj Maryamah din dawowar Aqeel ba zainab babu 'yarta Amma Kuma zuciyarta ta rinjayeta komai ya lalace tsakaninta da qanwarta.
Zainab kuwa tafiya kadan tayi aka fara Kiran sallar asuba Duk da hakan bata tsayaba tafiya takeyi batareda tasan inda take jefa qafafuntaba sbd rufewar ido Dana zuciya.
MARYAMAH dake goye bayanta tanajinta ba bacci takeyiba sbd tashin hankalin tuni ya tadata bacci gashi babah tsabar son tafiyar yasa Ana fara rikicin ta dauketa ta tsala Mata wanka da ruwan sanyi.
Har akai sallar asuba aka fito gari yafara haske tafiya takeyi batareda tasan inane gurin zuwantaba
Idanuwanta kuwa sun kada sunyi jajir sun bushe Dan kuwa kukanta tuni ya tsaya harna zuci.
Tafiya taci gaba da Yi har asalin anguwarsu na gidan ubansu Wanda daqyar takawo kanta harta gane saidai tana shogowa layinsu Bata hango alamar gidansuba Dan kuwa wani mahaukacin gida take hangowa Mai girman gaske dayake nuni da gidan manya ne,
Anguwar gabaki daya ta canza tazama kamar anguwar Yan shiyasa sbd kalar samari da mutanen datake gani marasa kamun Kai sai Yan siye da siyarwa dasukai yawa.
Kofar qaton gida data tabbatarda Nan ne gidan ubanta harma da kusan gidajen hudu da aka hade akai gida daya dasu take kallo da idanuwanta dasuke qara rinewa da tsananin qunci da radadin zuciya.
Batada komai batada kowa sai wannan gidan na ubanta Wanda takeda gado acikinsa,
Saidai Kuma wannan tsarin data tadda yasa tarasa Duk wani Dan kuzarin datake ganin ta hangowa kanta.
Guri tasamu daga gefen gidan ta zame ta zauna tareda rintse idanuwanta wani zazzabin sabon tashin hankaline yarufeta.
Agurin ta zauna tana Jin jikinta na rawar tashin hankali,
Wa zata tinkara da zancen Ina aka Kai gidan ubansu?
Wayema ya santa?
Maryamah da umma Kawai aka sani barema duka gidajen data sani na maqotansu babu gabaki daya anguwar ta zama kamar kasuwa kamar dandalin siyasa, ta Ina zata Samu mutumin arzkin da zata tambaya???
Shiru tayi tareda sunkuyar da Kai tana rasa tunanin kamawa,
MARYAMAH dake bayanta lafewa tayi a bayan nata sbd zazzabin wanka ruwan sanyin da babah tayi Mata tun kafin asuba hakama tagansu a inda Bata taba ganin sunzo ba Dan kusan MARYAMAH din Bata taba fitaba kullum suna gida Kamar mayu.
Ta Jima agurin zaune har Saida ta Dan dawo hayyacinta kadan kafin tafara kokarin miqewa sai kawai taji ihu da hayaniya ya gauraye koina
anguwar take ta dauki ihu anata gudu....
A tsorace take kallon mutane dake gudu ta miqe tana neman hanyar tsira saidai tuni anguwar ta dauki wani irin yamutsin fada na Yan ta'addar siyasa harda makamai dasu tiya gas.
Jefarda kayanta tayi tana neman hanyar gudu Amma babu Dan kuwa sare sare akeyi sosai
A rikice tasamu ta fada gidan dake kusada babban gidan masu gidan na neman tufewa ta fado suka rufe sunata masifa da zage zagen wannan masifa dataqi qarewa kullum haka suke a anguwar.
Itadai shirun tayi bayan babbar kofar jikinta babu inda Baya rawa sbd tashin hankali da quncin wannan rayuwar data samu kanta aciki Kuma.
Tana tsaye agurin itada wasu da yawa wainda da alama baqi ne a anguwar suma Dan hankalinsu duka a tashe yake saidai su dukkaninsu daga cikin gidan suka fito sabanin ita da shogowa tayi.
Harbe harben bindigar da akeyine yasa zuciyarta qarasa daskarewa sukuwa sauran sake shiga tsoron suka sbd tsoron kada ayi Kamen harna cikin gida tunda hukuma ce tazo ake harba bindigar.
"Allah dai ya tsinewa wainnan yayan banzan da Allah bai saka musu hakuri ba,
Ana abu daya duk zasubi su ishemu da kayan hayaniya,
Ina ramuwar baccin da banyiba sbd kasuwar Daren jiya shine zasu ishemu harda harbe harbe.""""
Daga bayansu zancen ke fitowa Dan haka dukkanin Maza da matan gurin tsoro da fargabansu yafara raguwa Dan kuwa LULU ce da kanta tafito take magana wato shahararren 'dan daudun daya Gama riquwa a bariki tareda gogewa a harkar duniyanci.
Fari ne tas dashi kyakkyawa Amma babu wani Abu daya nuna tsoro ko fargaban halinda suke ciki.
Kofar ya nufo Kai tsaye ya bude Yana cewa"
Kuzo ku fice qartin banza da wofi wlh sai antafi daku ai Dama na Hana kowace shegiya kawomun Maza a gida ku wuce.
Bude kofar yai gabaki daya ya fito batareda tsoro ba ko shakkar abinda yake faruwa a wajen.
Take kuwa yayiwa mazan cune aka shigo aka kamesu duka cikin tsautsayi aka hada harda zainab wadda kwata kwata takasa gane meke faruwa Dan hankalinta ya Jima da barin jikinta.
Har ansakata a mota ganinta da goyo Kuma kamar Bata hayyacinta yasa LULU cewa Banda ita.
Ba musu aka sauko da zainab Yan sandan suka wuce bayan sun cika mota uku da Yan ta'addar dasuka tada fadan Dama kwartayen dasuka kwana gidan karuwan LULU.
Bayan Kamen Yan sandan sun wuce anguwar ta lafa aka fara firfitowa kowa naci gaba da harkar gabansa..
Zainab kafafuwanta dake rawa takasa dagawa sbd tashiga babbar firgici na abinda yafaru din kamar kyaftawar ido.
Rasa nutsuwarta take neman Yi
Tafara rarraba ido tana neman daurin kayanta tabar anguwar..
A dage Lulu ya kalli zainab din cikin gatse yace"
Ke Kuma daga Ina haka?
Da Alama baquwar zuwa anguwar ce
To maza kija qafafunki kibar anguwar Dan ba gurin zuwan irinki bane..
Da sauri zainab tayi gaba har tana tuntube zata Fadi...
"Ke dawo, zo
Shege kikai Kika baro gidane??
Kasa magana zainab tayi sai tayi gaba tana fasa neman kayanta duk da taso Kayan Dan basuda wasu saina jikinsu daga ita har MARYAMAH.
Ganin yanda take a kamar Mata hankali tana kallon babban gidan da gadonta yake ciki yasa LULU biyota ya kirata zaiyi magana yaransa suka iso mota kusan biyu suna masa kirarin,
"sai hajiya LULU"
Washe Baki yahau Yi Yana kallonsu sbd sune abin Alfaharinsa
Dan kuwa sune masu cire Masa baqin cikin aike kowane irine.
Kallon wadda ta iso gefensa yayi yace"
Siddi ki kaimun baquwar Nan ciki Ina tafe.
Kallon zainab yayi yace,
"Kibita Ina zuwa zamuyi magana.
Qin binta zainab tayi saidai Kuma ganin shine maqocin babban gidan yasata tunanin jiran ko zata Samu bayanin dazai isar da ita inda gidan mahaifinsu yayi.
Shikuwa Lulu ganin yanda take kallon babban gidan makocinsa Kuma maqiyinsa yasashi son tsayar da ita yaji
Babbar fatarsa ace MANDE DS ne yayiwa matar wani abun yayi amfani da hakan ya lalata Masa suna da komai ya nuna Masa iyakarsa.
LUKMAN AHMED Wanda ake duniya ta sani da Lulu Asalin Dan anguwar ne Wanda mahaifinsa shima rasuwa yayi tun Yana qanqani,
Shi kadaine agun mahaifiyarsa namiji sai qanwarsa mace wadda ta rasu sanadiyar fyade da akai Mata da qananun shekaru,
Rasuwar qanwarsa ita tayi sanadiyar ta mahaifiyarsa wadda ta rasu bayan sunyi yawon Sharia Har qarfinsu yaqare babu nasara sbd Dan manya ne yayi Mata fyaden bayan yayi shaye shaye.
Lulu yayi gwagwarmayar rayuwa bayan rasuwar mahaifiyarsa ya dauki fansar abinda akaiwa qanwarsa da hannayensa ta hanyar saka mugun itace yaron da yayi barnar dukan da yayi sanadin daya rasa idonsa daya da qafafunsa duka biyun tareda hakoransa na Hana guda shida.
Hakan yajawa Lulu masifa Mai tsanani aka aikasa gidan yari tsawon shekaru goma Sha daya
Yana fitowa yashiga harkar siyasa inda yasamu shahara amatsayinsa na 'dan daudun daya Gama cire tsoro da shakkar kowa.
Lulu yasamu shiga da suna sosai duniyar Yan siyasa da Yan duniya,
Gidan abinci ya bude babba Mai kyau da tsada,.
Ana haka aka Kuma yiwa yarinyar datake Masa aikin abinci a restaurant dinsa fyade Wanda yaja aka rufe restaurant din nasa yayi hasarar duka Dan arzikinsa..
Lulu yasha gwagwarmaya da wahalar rayuwa matuqa kafin yasamu yadawo gidan ubansa ya gyara..
Tun bai Gama gyaranba alhaji MANDE DS mahaifin Yaron dayayiwa kanwarsa fyade ya siye gidajen layin kusan guda hudu a jere ya bugesu yayi babban gidansa agurin batarda ya dubi lalacewar da anguwar tayiba tareda ga Kuma qarin Shi din Dan siyasa ne take jamaarsa suka sake maida anguwar ta yan siyasa.
Alokacinda mande ds ya siye gidajen yasone ya siye harda gidan Lulu sbd abinda yayiwa dansa yaketa sakawawa Ana lalata komai na lulun,
Rikicin siyan gidan lulun dayaqi saidawa ne yasa yane mande ds ne ke lalata Masa komai na rayuwa Dan haka yaqi saidawa qarshe ya maida gidan nasa na karuwai Dan kuwa gidan babbane dakuna birjik.
Mugun zama sukeyi da junansu sbd babu Mai kaunar wani tsakanin Lulu da alhaji mande ds din,
Lulu siyasar dayasan baa kaunar mande ko kadan ita yakeyi bakin Rai Dan haka yasa anguwar kullum cikin fadan sare sare akeyi na siyasa ga Kuma qaramar kasuwa a gurin,
Ga gidan Lulu daya shahara na karuwai,
Ga babban gidan abinci daya Kuma budewa anan Dan haka dai anguwar ta lalace gabaki dayanta babu mutumin kirkin dake zuwa,
Lulu da qarfin iko da lalacewarsa da karuwansa yayi amfani ya lalata suna anguwar kwata kwata sbd kawai duk lokacinda aka ambaci anan gidan Alhaji mande ds yake mutuncinsa ya zube a idon mutane.
*****Zainab ya kalla bayan yashigo palonsa ya zauna a daya daga cikin kujerun palon Yana kallon zainab data kasa zama tana tsaye tana jiransa itama.
Cikin sakewarsa irin ta Wanda baida damuwa yace"
Kece zakiyi magana ko nine zanyi???
Batareda tayi Masa kallon duka idoba ahankali tayi Masa bayanin gidan mahaifinta tazo nema.
Da mamaki ya tambayeta gidan datake nufi Dan duka gidajen yasansu tunda shima anan ya tashi.
Bayanin gidansu da mahaifinta tayi Masa take yaganeta Dan shekarunsu daya.
Cikin danne dacin Ransa na shekaru dasuka wuce ya sanar da ita Shi Dan Iya Fatu ne wadda ta reneta bayan rasuwar mahaifiyarta.
Da mamaki ya tambayi yanda ta haifi Yar dake bayanta Amma takasa sanar dashi komai sbd tasake shiga tsoro da firgicin rayuwa Kuma bayan Jin abinda ya samu iya Fatu dashi lulun.
Zaman Dole yasata sbd kukan da MARYAMAH ta fara
Ta sauketa
Yasa aka kawo Mata abinci Mai kyau daga shagon kicin din restaurant dinsa tabawa MARYAMAH Dan ita bazata iya cin komaiba
Duniyarta da komai nata ya tsaya.
Sallar asuba da tashin hankali yasa bataiba tayi a Rana tsaka kafin taci Dan sauran abincin da MARYAMAH din ta rage bayan ta yagalgala.
Da fari hanata tafiya yai sbd zai bincika Mata tagurin wa mande ds ya siye gidan nasu.
Batada zabi batada mafita tunda ko ta fita batada gurin zuwa Dan haka ta zauna a gurin Lulu din Wanda kaf gidan dakinsane kawai yakeda Palo da dakuna biyu aciki kowane da toilet sbd shine Mai gidan Kuma shugaban gidan.
##MAMUH#
#IDON NERA
#AQEEL ASAD
#HOTLOVE/MARRIAGE
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
17
*_AROOS SCENTS_*
*_AROOS SCENTS_*
_JAMA’AR ZAFAFA BIYAR… DAMA MABIYA MASU KARATUN LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR…!!_
_BARKAN KU DA WAR HAKA… YAU DA YARDAR ALLAH MUNZO MUKU DA ABUN ARZIKI. KUNSAN KAMSHI RAHAMA NE. INA MASU NEMAN INDA ZASU SAYI TURARUKAN WUTA MASU KAMA GIDAH! DA TURAREN KAYA, TURAREN TSGUNNO, TURAREN WANKA DANA WANKI DA JIKI?_
-
_KAI BA ANAN KADAI SUKA TSAYA BA. SUNADA TURAREN KHUMRAH KALA KALA DA KULACCAMS NA KECE RAINI._
_AROOS_SCENTS_
_AROOS_SCENTS_
_AROOS_SCENTS_
_KUNJI SUNAN KO? *AROOS_SCENTS*_
_*AROOS SCENTS* SUNA GARIN *KADUNA* SUNA KUMA TURA KAYAN SU A FADIN NAJERIYA DA KETARE_
_LAMBAR WHATSAPP DIN SU :07067786384_
_INSTAGRAM : aroos _scents_
_SCENT HEAVEN😍SMELL RICH! LEAVE DEM WONDER WHAT YIU USED…😍A SCENT LIKE NO OTHER. SCENT THAT WARDS AWAY SMELLS_
_KYAU! INGANCHI DA KAMSHI MAI SANYAYA ZUCIYA SAI KAYAN TURAREN *aroos scents *_
*********
Yamma nayi zuciyarta takasa nutsuwa saidai Kuma ahakan tanajin sassaucin zama anan idan har tana tareda 'yarta akan zama a Abuja 'yarta na Cameroon batasan irin rayuwarda zatayiba acan tunda tanada tabbacin babu Wanda zai tsaya akanta ya Bata tarbiya,
Idan har Lulu zai karba Mata haqqinta na gidan babanta zataso hakan sbd Nan kawai takeda sauran hope na inda zata zauna tayi rayuwa da MARYAMAH dint hakama idan Aqeel yadawo zaiyi saukin samunsu a gidan baban nata.
Dakinsa 'daya ya bata itada 'yarta abinda bayayi baikuma taba ba
Wato barin wani ko bawa wani dakinsa 'dayaba sai akan zainab itama Dan ganinta ayau tareda gane wacece yakejin kamar 'yar uwarsa ce tadawo garesa tunda dukkaninsu har zainab din uwa daya ce ta renesu abinda baida tabbaci shine idan nono daya sukasha, wato idan iyarsa ta shayarda zainab din.
Itama zainab dayake Bata manta iyah dinba sbd kafin atafi da ita gidan Maryamah tun wancan lokacin iyah dince kawai take kaunarta take siya Mata wasu Yan abubuwan wasu lokacin har Saida aka tafi da ita gidan zainab sukai rabuwa Ashe tahar abada ce.
'Dakin baida girma sosai Amma nata na gidan Haj Maryamah baifi wannan din girma ba,
Qatuwar katifa da wardrobe ne Acikin dakin sai madubi da toilet.
Wanka tayiwa maryamah itama tayi tayi sallar ishai Dama ansake kawo musu abinci daga shagonsa sunci sun koshi.
Babu Bata lokaci bacci ya daukesu daga ita har MARYAMAH tunda a matuqar wahala suke.
Washe gari zaunar da ita Lulu yayi yai Mata bayanin gidansu dai agurin Mai anguwa Mande ds ya siya Kuma yasama tabbacin Shi Mai anguwa gidan a hannunsa su Maryamah suka barsa.
Shiru tayi Dan batasan me zatace ba,
Ita kwata kwata Bata gane komai Kuma,
Abinda takeson Jin gidan na ubansu ne kokuwa na haya ne?
Gidan na babanki ne halak malak ba haya ba
Dan haka dai yanzu haqqinki Dole zaa Baki idan DS yaci idan Mai anguwa babu Wanda zaici ya zauna lafiya.
Girgiza Kai tayi ahankali tana Dan rintse idanuwanta dasuka Dan sauya cikin mutuwar jiki tace abar maganar gidan ta hakura Dan ita din ba kowa bace,
Gadon nata ba batajin tanadashi tunda dai su umma basuma San tazo neman gidan ubanta dinba.
Fada Lulu ya rufeta dashi Yana takura da fadan sosai har Saida ta zayyane Masa komai na rayuwarta da dalilinta na baro gidan Yar uwar tata..
Sake Baki yayi jikinsa da bakinsa na mutuwa Dan bai dauka haryanxu akwai wainda zuciyarsu Bata aikiba
Dan kuwa zainab alamu sun nuna tata zuciyar a kwance take cikin ruwa ba jini ba..
Barinta yayi Yakuma ficewa Dan baisan mezai ceba Wanda zata gane Amma dai koma menene sai anbata gadonta wlh.
Daga ita zai MARYAMAH yabari wuni guda a dakin sai siddi daketa dawainiyar kawo musu abinci da abubuwan buqata.
Tunda tashigo ko kofar fita daga palonsa batayiba sbd gida koina karuwai ne da maza
Musamman yanzu da sukasan Lulu bayanan kowane namijin shogowa yakeyi ya shige dakin budurwarsa
Dan babbar qa'idar Lulu bayason maza na zuwa gidan gurin karuwansu,
Saidai kowace idan dare yayi kokum idan tana buqata tace gidan saurayin nata ko alhajin nata koma hotel ne.
Siddi sosai ta nuna musu kauna itada MARYAMAH dinta sbd siddin itace Yar hannun damar Lulu
Itama zaman kanta takeyi Amma tanada kamun Kai ba kamar yanda sauran karuwan keyiba.
Lulu idan akwai babban abinda ya tsana a rayuwarsa shine zalinci,
Bayason zalinci,
Ya tsani zalinci,
Musamman ga mace shiyasa duka Yan barikin dake gidansa aduk lokacinda aka cutatar dasu shine yake tsaya musu sai inda karfinsa ya qare Dan haka kowace Yar barikin dake gidan Kamar babbar Yaya suka dauki Lulu akwai Respect da bin umarni sosai a tsakaninsu dashi.
Yayi tir tareda Allah wadai da jinin umma da Haj Maryamah harma da 'dansu Aqeel Dan kuwa shima baiji ya Burgesa ba tunda jininsu umman ne.
Kai tsaye hukuma ya daukowa Mai anguwa aka kamasa suka kwasa zuwa police akan ya siyarda gidan marainiyar Dan Shi kwata kwata ya cire Haj Maryamah a lissafin gidan tunda tafi karfinsa ga wadda ke buqata Nan Dan inganta rayuwarta data marainiyar 'yarta Dan haka duk ubanda yakeda saka hannu a cinye gidan saiya fito.
Rigimace ta balle a gurin hukuma lokacinda aka kawa zainab ta Fadi ita wacece Mai anguwa yayi tsalle yace wlh qaryane ita ba 'yar marigayin bace Dan baisantaba...hasalima ita Yar marigayi malam adamu din itace da mahaifiyarta suka bada gidan aqara ayi masallacin da aketa kokarin ginawa a anguwar tin shekarun dasuka gabata..
Zainab najin haka jikinta yayi mummunan nauyi ta kasa cewa komai Dan kuwa Kai tsaye aka aibata sunanta daba Yar mahaifinta ba..
Riqe hawayenta tayi tana kallon Lulu Dan ya janye rigimar Amma yace wlh bazai janyeba tunda bacin suna yashigo ciki Kuma.
Case tun Yana qarami sai gashi ya girma yazama babba Dan kuwa hukuma babba tashigo ciki sbd sunan Mande ds daya fito a matsayin shine Wanda ya siya gidan.
Fitar zancen yasa rikicin yaqara girmama Dan kuwa tuni mutuncin DS yafara rawa Dan kota Ina yada zancen ake qarya da gaskia...
Ran DS yayi mummunan baci gashi tunda yaji Lulu a zancen yasan lulun bazai tsayaba saiya Gama lalata Masa suna da mutunci Dan haka take ya saki kudi aka fara neman rufe case din Amma tini Lulu ya juyar da case din zuwa gurin manyan hukuma ba Bata lokaci saiga zancen yashiga kotu.
Tun lamarin na wasa saiga komai ya girmama
Hankalin Zainba ya tashi sosai Dan kuwa Bata taba tunanin zata shiga rigima irin wannanba.
Ta bangare daya Sharia akeyi akan gidan mahaifinsu
Bangare daya Kuma duk masu shedan sun tabbatarda zainab din ba 'yarsa bace yarsa dasuka sani Haj Maryamah Kuma da kansu suka bada.
Ds yayi amfani da karfinsa da dukiya akan shariar sai gashi an wankesa tareda Kama Lulu da zainab akan kokarin Bata Masa suna..
'daga qara Lulu yayi sbd a wanke zainab da