Showing 90001 words to 93000 words out of 149977 words

Chapter 31 - IDON NERA BY MAMUHGEE CMPLT.txt

25 Nov 2024

6534

a kame cikin nutsuwa kwarjininsa na qara bayyana Kamar bashine yayi abinda yayi aciki dinba.


Motar yanufa Kai tsaye yashiga daga ita harshi Babu Wanda ya kalli juna saidai qamshinsa datake ji maqale jikinta shima akwai nata qamshin daya mannewa kayansa.


Ahmed yakira a waya da sauri ya taho yashiga motar ya tada suka fice.


Kai tsaye gidan IDON NERA suka nufa akai Amal din kafin ya wuce gidansa Dan dawowarsa kenan daga airport yakira Ahmed din yazo ya daukesa malam Rabiu Kuma ya wuce Kai Al-Amin da gida.


****Haj Maryamah da umma suna Isa gidan IDON NERA Kai tsaye securities suka qi bude musu gate Saida suka sanar da Haj Zainab wadda tayi shiru da mamakin Jin su waye din.


Numfashi ta sauke kafin tace abari su shigo din


Daman tasan zaayi hakan


Sunma Dade Basu zo ba Dan Bata dauka zasuyi shiru har tsawon lokacinba.


Parking sukayi a harabar gidan


Bilkees ce ta tuqo su Kuma bada mufeeda sukazo ba yau din.


Itama haj Zainab tana kashe wayarta daga gate din ta miqe ta sauko kasa Dan Jin meya kawosu gidan Dan idanma akan auren AQEEL ne kofa zata nuna musu su can suyi dashi


Babu Wanda zai kasheta lokacinta baiyiba tana zaune lafiya cikin iyalinta.


Harta sauko Basu qaraso cikiba Dan Haka ta nufi kofa zata taresu tin acan harabar suyi acan saigashi sun shigo Bilkees ce agaba tana yiwa koina gidan kallon qazanta da qyama.


Haj Maryamah da umma ne a baya


wannan karon fuskokinsu Babu alamar sauki da gaske sukeson akawo karshen komai.


Batayi wahalar cewa su zaunaba da tasan ba zaman zsuyib ba Kai tsaye tace,


Lafiya dai inace ba???


Itama Haj Maryamah Bata tsaya batawa kanta lokaciba sbd ta gaji Kai tsaye tace,


"Kin shayar da AQEEL nononki nakeson ji daga bakinki.......


Wani kallo Haj Zainab ta dago tabi Haj Maryamah din dashi cikeda matsanancin mamakin dayafi na koyaushe,


Bata taba tunanin tsanar dasuke Mata takaisu ga rasa ilimin addinin dasuke dashiba.


Siddi data biyo mommyn tana bayanta ta fito bayanta itama cikeda mamaki tace,


"Nono kuma?


Kunsa me kuke fada kuwa?


Shayarda Shi na nufin aurensu ya haramta kenan fa??.....


Katseta Haj Maryamah tayi cikin fushi Mai tsanani da bacin Rai tace,


"Ki ringa tsayar da Yayanki inda Ina magana sbd tarbiyarsu daban take data yayan da muka sani,


Dake nake magana


Amsa Kuma nakeso idan ba hakanba kotu ce zatayimun maganin duk wani mummunan aikinki akan Dana tun Yana qanqaninsa.......


Cikin fushin dayafi na Haj Maryamah din Zainab ta katseta da cewa,


"Indai wannan shine halin yayan da kike magana akai to abarmin yayana ayanda suke din haka sbd jahilci da kaucewa Allah kawai nake hangowa a wannan rayuwar da kike fada..


Katseta itama umma tayi da cewa,


"Amsa aka tambaya ba rayuwar 'yayanki ba Zainab Idon Nera,


Kin shayar da AQEEL nononki ne Kuma sbd son abun duniya Kika Bari ya auri 'yarki da sukasha nono daya


Dan Haka auren ya haramta Babu Wani sauran Bata lokaci a warwaresa kawai.......


"Meyake faruwa Anan?" Sukaji anfada daga bayansu


Dukkaninsu suka juyo gabaki dayansu suna kallonsa.


Ganinsa tareda Amal wadda itama kallo daya tayi musu a ranta dayake baci da baqin cikin ganinsu tace,


"Meyasa duk haukan tsoffin Nan ya motsa anan suke zuwa su sauketa??ΒΏ


Bilkees da ganin AQEEL ASAD dinta da Amal din tare yasata sakin Baki zuciyarta na tsalle bakinta na neman bushewa sbd saninsu baya gari tsawon kwanakin to da ita yatafi kokuma Daman baiyi tafiyar bane Yana Nan ya tare???..


Cabdijam" suka fada dukkaninsu atare su ukun


Da Haj Maryamah da umma da Bilkees wadda tafara Jin zafi na shigota ta ko Ina.


Da mamakin ganinsu a gidan shima yasake maimaita tambayarsa fuskarsa akan mahaifiyarsa wadda take kallonsa cikin fushi.


A natse kamewarsa na tsananta ya sake kallonsu kafin ya kalli Mami wadda tagama girgiza da haukarsu ta wannan karon yace,


"Meyake faruwa Anan??....


Zuciyar Bilkees data gama konewa da baqin ciki da takaici babu shakka ko tauna zancen sbd gwara yaji yasan aurensa ya haramta da Amal


Tasan ba lallai sunsha nononba tunanin su umman ne kawai Amma gwara ace sunsha din auren ya watse kowa ya huta...


Kai tsaye tace,


"Maminka ta shayar dakai kana yaro Dan Haka aurenka da......


Wani irin kallon daya juya yayi matane yasa kalmomin bakinta watsewa suna gagara haduwa sbd duk abinda takeyi duk haukarka kallonsa daban ne..


Haj Maryamah dataga Bilkees din ta rude saita qarasa zancen da cewa,


"Aurenka ya haramta anan saika sakar Mata 'yarta....


Ita kanta Amal wani matsanancin mamaki tashiga Jin zancen gabanta yayi wani irin faduwa ta juya ahankali ta kalli mommynta wadda shima ita ya zubawa fararen idanuwansa dasuka sauya take yana jiran maganarta wadda kalma daya zata bude Baki tayi ya fahimci gaskiyar zancen.


Duk inda zafi da ciwon zancen yakai yayiwa Haj Zainab din ciwa mai tsananin gaske,


Me suke nufi?


A wancan lokacin tana budurwa me suke nufi da Tasha wani abin ta shayar dashi??


Ashe qiyayyar bamai rahama bace,


Wani Abu Mai ciwo da zafi ta hadiye sbd ta fahimci haqiqa sbd kawai su haramta aurensa da Amal a warware auren suka bullo da hakan Amma ta tabbatarda sunsan Bata shayar dashiba.


Idan Akan AQEEL ne suke Mata wanna qiyayyar to tagaji da lallabasu


Duk me mutuwa ya mutu Mai Rabin wahala Kuma saiya shirya...


AQEEL dake kallonta Yana jiran amsarta ta kalla kafin ta maida kallonta kansu umman da duk suka zuba Mata ido suna jiran tayi zuciya tace eh hakan ne sbd auren ya qare duk su huta,


Abinda zata fada sunsan shine AQEEL zai yarda dashi Dan Haka gabaki daya palon idanuwan kowa na kanta hankali tashe suke jira abinda zata fada Wanda yake duka zuciyar duk Wanda yake gurin musamman Amal data kasa motsawa daga inda take.


##MAMUH#


#HOT LOVE/AQEEL ASAD


*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯


Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*πŸ”₯


Billyn Abdul


*IDON NERA*πŸ”₯


Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯


Safiya huguma


*KI KULANI*πŸ”₯


Miss xoxo


Littafi daya---400


Biyu---600


Uku----800


Hudu-----1k


Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171


Maryam sani


Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ


*Ina yan uwa 'yan nijer?*


*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA


biyu---650CFA


uku----850CFA


hudu----1050 CFA


Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*


*Thanks for choosing us*πŸ”₯


47


*_Arewabooks@Mamuhgee_*


47


AQEEL ta kawai ta iya kalla cikin kaunarsa da Babu Wanda ya Isa ya cire Mata hakan duk mugun sharri ko qazantar dasu umman zaku bullo Mata dashi,


Maida kallonta tayi kan Haj Maryamah ta zuba Mata su tana kallon cikin idonta ta bude Baki tace,


"AQEEL bantaba shayar dakaiba,


Bantaba tunanin shayar da kaiba Koda Ina shayarwa awancan lokacin wallahi tallahi bazan taba shayar dakaiba sbd mafarkin irin wannan ranar da zaka iya zama jinana.


Dawo da kallonta tayi Kansa tace,


"Aurenka da Amal halastaccen Aure ne Babu ta inda kuka Sha nono daya duk Wanda ya fada ya fadane sbd son Rai da alamun samun matsalar qwaqwalwa dasuke bayyana ataredashi,


Auren Amal yariga ya dauru duk Wanda yakeda matsala da hakan zai iya faduwa ya mutu sbd a yanzu Kam Babu Wanda ya Isa ya sheganta auren Nan,


Kamar yanda kukeson rabuwar auren Haka nakeso Amma daga yau wallahi koshi Bai Isa ya saki wannan aurenba idan har na Isa inada iko dashi kaman yanda kuke fada zamu gani,


Wanda ya shirya ganin 'yayan AQEEL da 'yar karuwa saiya riqe lafiyarsa Wanda Bai shiryaba shirye nake da zuwa zaman makokinsa..


A zafafe umma ta bude Baki zatayi magana ya daga Mata hannu bacin Ransa da baya bayyana ko kadan


Yau din ya bayyana


Ran nasa a bace Amma cikin nutsuwa yace,


"Me zakice Bayan duka wainna abubuwan da kike jagoranta anayi wainda hankali da mutunci baya dauka.,


Kan mahaifiyarsa ya maida kallonsa itama shi take kallo cikin bacin rai da baqin cikin Yana musu fada gaban Zainab da 'yarta.


"Meye Haka kukeyi umma?


Meya amfanin ilimin da baa aiki dashi?


Kunce kune masu ilimin da mutuncin anan to me kukeyi umma?


Umma idan tsufa ya juyar Mata da hankali ke umma lafiyanki kalau Meye duka amfanin wannan??.....


Waye yafara kawo zancen shayarwar Nan??


Shiru sukayi kowa na jiran amsar da zaa fada,


Cikin zafi Yakuma cewa,


"Waye ya kawo maganar??


Umman Cameroon da bazata yarda yaji sune suka fara feso zancenba sbd zasu qarasa rasashine


Kuma Daman tana qule da lamarin Bilkees Dan Haka Kai tsaye tana matse fuska da baqin ciki tace,


"Matarka gatanan itace tace kafada Mata......


Wani mummunan tashin hankalin ba zata ne ya bugi Bilkees a rikice ta juyo gurin umman tana cewa,


"Laila ha illallahu,


Qalu innalillahi


Me wannan tsohuwar kike fada???


Wallahi qarya takemun......


Wani Abu Mai nauyi ya hadiye a kirjinsa kafin ya zubawa Bilkees fararen idanuwansa dasuka sauya gabaki daya lokaci daya,


Kasa qarasa zancenta tayi sbd tsabar rudewa da tashin hankali Mai tsananin gaske tana tsinewa umma da mugun tsufanta.


Baicewa Bilkees din komaiba ya juya ya kalli mahaifiyarsa yace,


Kingani daga umman har wannan din basuda cikakken hankali???


Meyasa Kika zabi biyewa...


Kuka Mai ciwo da qarfi umman Cameroon ta fashe dashi tana cewa,


"To daga qarshe dai gashinan AQEEL ya zageni yaci mutuncina,


Zainab burinki da buqatarki ta biya,


Allah ya Isa tsakanina dake da zuriarki,


Kin cuci halaccin da mukai Miki muka taimakeki alokacinda bakida kowa,


Allah ya Isa da wannan......


Cikin zafi da boye fushinsa ya dakatar da ita tareda Kama hannun mahaifiyarsa ya juya da ita.


Bilkees cikin tsananin mutuwa da tsoro ta biyo bayansa zatayi magana ya daka Mata wata irin tsawar datasata dakatawa tana kallonsa cikin firgici da tsoro.


Wucew yayi ya fice da mahaifiyarsa yabarsu umma na kuka sosai


Bilkees na hawayen tashin hankali.


Da gudu Bilkees tabi bayansa qafafunta na rawa saidai kafin ta Isa yabar gidan a motarsa da Haj Maryamah.


Motar da suka zo da itace ta nufa da sauri ta shiga hannuwanta da duka qafafunta na wata irin rawa tana kokarin Shiga umma ta fito ta nufo motar saidai kafin ta bude Bilkees cikin ficewar hayyaci tace,


"Aurena kikason kashewa umma


Me nayi Miki?


Kokuwa Nima angama Dani kamar yanda aka Gama da Zainab dinne?


Wallahi umma aurena ya mutu da AQEEL saina tabbatarda Bai rabu da Amal dinba sbd ku tabbata zuria daya dasu din da bakwa so.


Nude motarta tayi ta fada tareda ja da gudu tabar umman a tsaye tana sake shiga tashin hankali da mamakin wannan shegiyar Diya Bilkees..


Cikin fushi tace,


Wlh ko Bai sakekiba akan wannan saina saka ya koreki daga gidan


Wannan gwara ma karuwan da ke.


Barinta Bilkees tayi gidan ta tafiyarta


Rasa inda ta nufa tayi Dole ta nufi gate tana share hawayen baqin ciki da takaicin hada zuria da Bilkees din itama.


Uncle Lulu ne yadawo zai shigo gate yaga fitowarta tana share hawaye Kamar zai wuce sai Kuma dai ya tsaya yace ta shigo motar.


Batada zabi tinda ko waya babu ahannunta Dole tashiga tana matse fuska babu Wanda yayi magana acikinsu.


Juyawa yayi yakaita har gate din gidan AQEEL ASAD din tana fita Bai tsaya komaiba ya juya Kamar yanda itama Bata tsaya cewa komai dinba tayi ciki jininta na tafarfasa akan Bilkees.


Koda ta shigo palon Haj Maryamah ranta a bace tana hawayen abinda Bilkees Tai Mata sai ta taddasu dukkaninsu a tsaye cirko cirko Fuskar AQEEL Jin tayi ja kasacenwarsa fari sai bacin Rai da fushinsa yasa Fuskar yin jajir batareda yace komaiba.


Kallon Bilkees data baro umma sukeyi shida Haj Maryamah data rasa Abu fada akan Bilkees dinma.


Shigowar umma ta fashe da kuka tana cewa,


Yau zata kwashe kayanta tabar gidan gwara Takoma Cameroon dinta tunda tozarcin da Bilkees tayi Mata ya wuce tinani.


Bilkees datakejin Kamar mutuwa ta samu umman a lokacin tayi kowa ya huta kasa magana tayi daga ita har Haj Maryamah sbd fushin da bacin ran AQEEL wani Abu ne da Basu taba ganiba irin hakan,


Fushi ne sosai a ransa dayake kokarin controlling sbd kaucewa hukunci cikin fushi.


Dakatar da umma yai batareda ya iya magana itama ganin yanayinsa yasata yin shirun suna sauraronsa kamar shine uban nasu,


A zahiri Basu taba ganin bacin Ransa Haka ba shiyasa suka shiga shakkarsa Musamman Bilkees datasan ta taqare kila ko darajar mufeeda tasani bazata ciba tunda basune suka haifetaba bare taci darajar haihuwa.


Haj Maryamah da umma ya kalla cikin nutsuwa da kakkaifan sautinsa dake nuni da magana daya yace,


Maganar aurena da alaqata da Mami daga yanzu na zare kowa aciki,


Daga ranarda wani yasake shiga maganar Zan yanke alaqata dashi ko wanene bayan mahaifiyata,


Itace ta haifeni itace takeda iko Dani Amma ko ita nata ikon baikai na Allah ba,


Allah ne yayi Amal matatace Babu Wani Wanda ya Isa ya aibata ko yanke auren idan ba Allah daya nufa ba,


Dan Haka duk Wanda yasake yiwa lamarin Kai tsaye ko waye daga ranar na yankesa daga cikin ahalina.


Gurin Bilkees ya juyo yayi Mata wani irin kallo dayake bayyanarda ficewarta a ransa kwata kwata Amma zai sake Bata wata damar sbd kaucewa aiki cikin fushi.


Wannan maganar na kasheta anan


Ko mufeeda kartaji abinda yafaru ayau din,


Idan wannan maganar ta fita ta bangarenki ki shiryawa kanki hukuncin da Baki taba tsammaninsaba.


Ummansa ya kalla wadda tai zuru tana kallonsa cikin mamakin Wai zai yanke alaqa dasu aka auren 'yar Zainab...


"Gidan Mami ma na sokewa kowa zuwansa daga yau din idan kunyi hakurin abinda kukeson fada 'yarta na zuwa idan tazo saiku ringa fada Mata tana isar muku da sakon.


Juyawa yayi ya fice yabarsu sake da bakuna cikin tsananin sanyin jiki da mamaki da tashin hankali,


Ya harda baqar magana AQEEL yake fada musu akan zuwa gidan Zainab,


Yau sune AQEEL yake gindayawa sharudda da iyaka duk akan wannan auren na zuriar Zainab.


Bilkees da zuciyarta ta dauki wani masifaffen nauyi akan abinda AQEEL yau yafada mata,


Kamar fa barazana ce yayi Mata akan aurenta?


Wainnan tsofin nasa tasan tunda suna tsoron rasashi zasu iya yin shiru din dayace akan auren


Shikenan ita ancuceta ake nufi anmata kishiya da wadda tasan matsayinta a ransa daban ne.


Wallahi bazata yardaba


Ai sai duniya tasan da zancen maganar Shan nono daya dinnan


Basai ansan itace tayi zancenba tukuna zai iya daukan matakinΒΏ


Mamin tasa ko su Amal din zata maqalawa fidda zancen suje can suyita zuba balai daganan auren ya lalace kowa ya huta.


A fusace ta miqe ta fice itama tabar su haj Maryamah cikin rasa abinyi da abin fada.


Tana Isa sashensu ta tadda mufeeda tadawo school itama Dan Haka sukai cikin daki suka rufe ta fadawa mufeedan komai wadda itama tayi naam dasu fidda zancen idan yaso ayita aibata auren Harma asamu masu shiga cikin maganar a Bata auren gabaki daya.


Da wannan shawarar sukai tsit abinsu suna dubarun yanda lamarin nasu zai kasance.


Haj Maryamah da umma kuwa Suma Dole tsit din sukayi Basu sake kowane yunqurin ba Amma dai Babu dare Babu safiyar da basa miqa adduarsu ga ubangiji Akan kada Amal din ta tare a gidan 'dan su.


Shi kansa AQEEL ASAD din gabaki daya ya daukewa kowannensu wuta Babu me ganin sauki a fuskarsa musamman Bilkees daya tattarata ya ajiye gefe daya


A gidan mufeeda ce kawai ke ganin fuskarsa


itama sbd laifin Bai shafeta bane.


Su umma tun suna daukan lamarin da sauki harsun fara girgiza da fushin nasa Dan kuwa bayan gaisuwa dayake shigowa ya musu basa ganinsa gabaki daya baya wani zama a gida.


Ta bangaren su Haj Zainab dinma sunsan an tabasa sbd Suma ya dauke kafa a waya yake kiranta yaji lafiyansu,


Ahmed kullum Yana zuwa yakai Amal school ya dawo da ita kokuma duk inda zataje daga school din,


Yana sane da duk inda take zuwa sbd Ahmed na fada Masa Kuma itama tasan Ahmed din Dole zai fada Masa tana zuwa duk inda taga Dama Amma Bata damuba ta watsar da zancensa


Shima shiru yayi Mata Yana sane sbd fahimtar Mata kusan dukansu hankalinsu baya aiki duka,


**Hankalinta yakwanta takoma rayuwarta hankalinta kwance sbd rashin zuwansa yasa ta manta da duka wata damuwa da aurensa Dan haka yanda take rayuwarta yanzu sai tafi samun nutsuwa.


Haj Zainab kuwa rashin zuwan nasa yasa tafara shiga Yar damuwa sbd gashi tafiyarsu tazo Amma har lokacin Bata samu tayi maganar dashiba,


Tasan aqidunsa zai iya Hana Tafiyar da Amal Amma Kuma gaskia ita tanason zuwa da ita din Dan gaskia yanayinta itama Yana Bata tsoro duk wata


Ta Dade tana wahala tinda tafara period duk wata Haka take fama da wannan wahalar.


Daurewa tayi ranar da daddare ta Kira wayarsa alokacin shima yanada tafiya ne washe gari.


Cikin nutsuwa ya daga wayar Yana zaune palonsa Yana kallon labarai hankali kwance.


Gaisawa sukayi tana sake tambayarsa lafiyarsa.


Am fine Alhmdllh" yace yana sauraronta.


Ahankali ta Koro Masa bayanin ciwon Amal din da tafiyar tasu tana dorawa da rokon yabar Amal sbd tana Shan wahala sosai.


Shiru yayi tsawon sakanni bayan yagama jinta batareda yace komaiba.


Numfashi Mai sanyi ya sauke daga baya kafin yabude Baki anatse yace,


"Mami kuje kufara ganin likatan akan Siddi ita daga baya sai a kaita din.


##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯


Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*πŸ”₯


Billyn Abdul


*IDON NERA*πŸ”₯


Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯


Safiya huguma


*KI KULANI*πŸ”₯


Miss xoxo


Littafi daya---400


Biyu---600


Uku----800


Hudu-----1k


Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171


Maryam sani


Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ


*Ina yan uwa 'yan nijer?*


*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA


biyu---650CFA


uku----850CFA


hudu----1050 CFA


Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*


*Thanks for choosing us*πŸ”₯


48


*_Arewabook@Mamuhgee_*


48


Shiru itama Haj Zainab tayi Jin abinda ya fada din jikinta na sanyi


To Amma ba damuwa zataga yanda zatai idan sunje Koda ta wayane likitan suyi magana da Amal din Koda akwai abinda zai iya cewa akan matsalar.


Sallama sukayi itama tana sake Dan shiga sanyin jiki sbd har lokacin tasan Yana cikin quncin abinda yafaru dinne,


Shikadai yasan halinda suka kusa sakasa da zancensu na rashin tinani,


Sun girgiza fiyeda yanda Shi kansa yake tinani Dan Haka ya zabi bawa Kansa da zuciyarsa hutu Akan dukkaninsu kowa da kowa sai gashi hakan na azabtar da kowaccensu Banda Amal da hakan yayi Mata daidai yanda takeso wato fitarsa arayuwarta.


Lokacinda mommyn ta fada musu AQEEL Bai bar tafiyar da Amal ba shiru Amal din tayi batareda tace komaiba zuciyarta na nauyi duk da Daman tasan hakan zata iya faruwa Amma Kuma idan har yayi ne Dan ta rokesa da kanta to ta hakura da tafiyar itama.


Siddi datake mamaki da Jinjina lamarin da ita Bata Saba gani a rayuwar nata aurenba ta kalli Amal dataqi cewa komai kan maganar tace,


"Amal Zaki iya da AQEEL ASAD dinnan kuwa?


Kiga yanda fa yake magana Kai tsaye baya shakka ko tsayawa Dan inda inda,


Gaskia Amal ki kwantar da Kai Kawai ki rokesa yabarki sbd kina buqatan tafiyar Nan fa.


Girgiza Kai Amal tayi tana cigaba da duba wayarta tace,


"Nafasa tafiyar inada abubuwan Yi a school.


Haj Zainab dake jinsu kasa cewa komai tayi sbd damuwar rashin zuwa da Amal din dakuma taurin kanta dazai Hana ta rokesa yabarta duk da tasan koda Amal din ta roka tunda yace aa to bazai canjaba.


Dukkanin Shirin tafiyarsu angama


Su duka gidan zasuyi tafiyar harda uncle Lulu da Anty Fareedah hadda Fahat


Daga ita saisu Bilkisu zaa Bari,


Baqin ciki da bacin Rai ne a cikin zuciyarta Mai tsanani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login