Showing 15001 words to 18000 words out of 149977 words
saima qaruwa Dan kuwa har kullum baa Dena karatu a gidanba saima qaruwa da jamaa sukai kusan duk manya Yan anguwar dake karatun da 'yayansu manya a gidan Malam Sanda ke basu karatun kullum tsakanin magriba zuwa ishai,
Hakama dangin Alh Asad maza kusan dukkaninsu anan gidan ake karatun dasu kullum Wanda sbd sakawa rayuwar gidan ido yasa suka maida sallar magriba dinsu zuwa ishai anan suma suna qaruwa da karatun.
Duka wannan lamarin dayake faruwa a rayuwar gidan har tsawon wannan lokacin babu Wanda yasan Zainab jinin Haj maryamah dince
A matsayin me Aiki suka santa tun kuruciya har kawo yanzu data girma zama mace shiyasa Babu Wanda yake ganin girma ko wani mutuncinta saima mayyar kwadayayya dasuke kallonta Dan uwar wahalar datakesha suna ganin kwadayi kawai zaisa ka zauna irin wannan rayuwar.
Shi Kansa Aqeel baisan qanwar mahaifiyarsa bace,
A taqaice baisan sun hada jini da itaba saninsa Mai aikin gidance
Shikuma uwace agaresa.
Qarin abinda yasa wasu masu aikin da Dama dasuke tafiyarsu shine duk wahala da biyayyar Zainab Haj maryama Bata yabawa bare nuna wani Jin dadi sai jikinsu na mutuwa da tsoron Hakan,
Wasu Babbar sata suke zubawa su gudu wasu Kuma salin alin suke tafiyarsu Dan Zainab dasuke karkashinta meta zama duk shekarun bare suda abin duniya suka fito nema ba Wai zaman bautar banza ba.
Babban abinda yaqara saka Haj maryamah yiwa Zainab tsanani akan rashin barinta fita shine gudun tasamu mijin aure a lokacin tayi aure tabar Aqeel Wanda tasan bazai taba zamaba Zainab ta tafi tabarsa
Tasani Sarai bin Zainab din zaiyi Koda zata hauka ne akan bataso tasan saiyabi Zainab
Itakuma bazata iya Bari danta yayi rayuwa a qazamtaccen guriba.
Sabuwar dabia Mai karfi data shigeta shine tsanar duk wani Abu daya shafi gwagwarmaya da mutanen daba nagartattuba...
Ta tsani zuwa ko irin guraren dasuka shafi irin Hakan shiyasa ma gidanta yasake samun tsaro da dokoki
Ko masu aikin da ake kawowa batason wadda Alama ta nuna tagama lalacewa da sanin maza,
Sam Bata kaunar irinsu
Qyanqyaminsu takeyi tareda musu fatar shiriya daga nesa shiyasa duk tsanani idan Tana gida batacin abincin kowa saina Zainab itama sbd tanada tabbacin tsarkinta da tsaftar rayuwarta da Bata gurbata tako Ina.
Rayuwarsu tafara sauyawa ne lokacinda haj Maryamah ta nemawa Aqeel wata tsadaddiyar makarantar boarding Amma Kai tsaye yaqi yarda da makarantar bakuma sbd kowa yaqi makarantarba sai Dan Maminsa wadda yasan wanu gata da sanyin datake ji duk sbd shine Dan haka akai akai Amma yaqi yarda.
Kiran Zainab Haj maryamah din tayi tai fada sosai tareda cewa lallai saita rarrashesa tasa ya amince ya tafi makarantar Dan tariga ta kashe maqudan kudi sosai akan karatun nasa.
Da farko Zainab rarrashinsa tayi tareda nasihu da Jan hankali iri iri Amma Sam yaqi yarda
Duk da bai fadaba itama tasan sbd itane
Qarshe dabai yardaba hakura tayi ta qyalesa Dan Bata son takura Masa Tunda baya gardama da duk abinda ta sakasa sai wannan karon
Dan haka bazata takurasaba Dan Jin take kamar tace a qyalesa karsu takura Masa Amma Kuma ba Dama Tunda uwar data haifesa ce take magana akansa.
Issue din makarantar yasa ran haj Maryamah baci sosai qarshe ta dorawa Zainab din lefin Bata basa tarbiya Mai kyauba tunda har zai iya qin abinda tace ita data haifesa.
Fada da bacin rai sosai akai akan maganar makarantar tasa Wanda dukanin laifin akan Zainab aka dorasa karshe kukan datake dadewa bataiba sbd bushewar da idanuwanta da zuciyarta sukayi Amma wannan karon saida ta kwana Tana kukan bacin ran da lamarin ya kawo Dan kuwa ko umma ta Kira wayarta Babu kalar fada da gorin da baayi Mata ba Hakan ta Basu hakuri Dan batada komai na fada.
Aqeel kuwa abinda sukaiwa Mamin yasa yace bazai taba zuwa makarantar ba Dan farko harya fara sauka akan zaije din ganin Maminsa nata lallabasa.
Tunda akai wannan tashin hankalin sai haj Maryamah tafara Jin buqatar raba danta da Zainab tun kafin lokaci ya qure Mata Dan kuwa da Alama 'danta tanaji Tana gani zai bijire Mata
Wato dai kamar Zainab ta haifawa Dan kenan.
Ita kanta Zainab sake kame kanta tayi tareda shiga taka tsan tsan sbd ganin ran su umman da Haj maryamah ya baci sosai.
Aqeel baije boarding school dinba Amma Hakan daya faru yasa Haj maryamah yanke shawarar daukesa daga qasar kwata kwata zuwa wata qasar yayi karatunsa acan sbd da gaske take buqatar rabasa da Zainab yanzu sbd zuwa yanzuma tsoron irin kaunar dayakewa Zainab din takeyi Dan kuwa yafara maganar abawa Zainab qananun abubuwa zuwa gaba yayi girmanda zai karba dukiyarsa ta tabbatarda zai iya mallakawa Zainab komai nasa data Gama yawo da wahalar kular Masa da kare Masa.
Ta bangare daya malam Sanda ne ya zama malami na musamman ga Aqeel tareda cusa Masa akidu na so da kaunar karatun addnini sosai sbd harda shi acikin burikan mahaifinsa akansa,
Mahaifinsa yanada tsananin shaawa da buqatan 'dan nasa yasan Addininsa sosai yayi zurfi acikinsa Dan haka ahankali sai shima Aqeel din Hakan ya shigesa yafara zama Mai tsananin son addini da karatunsa sosai.
Yana karatun bokonsa Kuma Yana na addinin sosai,
Kokarinsa da nutsuwarsa akan Hakan yasa malam Sanda maida hankali gabaki daya akan Aqeel din Dan cika burin Alh Asad dakuma Dan samun qarin Wanda addnini zai qaru dashi.
Ahankali shaquwarsa da malam Sanda tayi zurfi sosai har yake Masa kallon mahaifi sbd shima ya manyanta yazama dattijo mai nutsuwa sbd ilimin addini daya ratsasa,
Sam baya tsallake maganar malam Sanda sbd ba qaramin girmansa yake ganiba musammam daya kasance ta wani bangaren kamar shi kadaine Bayan Maminsa Wanda yake fahimtarsa.
Yazama matashi Mai cikakkiyar nutsuwa da kamun Kai Kuma har lokacin Babu Abu daya rage na shaquwa da girman kaunarsa da Maminsa saima abinda yayi gaba,
MUHAMMAD AQEEL ASADULLAH yazama wani irin saurayi da kallo daya zakai Masa kasan 'dan gatane daya taso cikin gata da nitsatsiyar rayuwa,
Kyakkyawane Wanda ya dauko kamannin mahaifiyarsa sak wacce itama kyakkyawar tun asalinta.
Zainab Kuma zuwa wannan lokacin sosai ta fita a sahun matasa masu 'yan shekaru Dan kuwa tazama mace sosai gashi har Haj Maryamah data girmeta nesa sosai ta fita kyan gani da jikin kuruciya sbd Hutu da Jin dadi
Itakuma wahala duk ta sauyata tasa manyancin zuwar Mata da wuri.
Har wannan lokaci Babu wani Wanda yataba sanin matsayin Zainab agun Haj maryamah acikin gidan
Shi Kansa Aqeel Asad har lokacin Baisan alaqartaba agurin mahaifiyarsa wadda yanzu Yana girmamata sosai sbd girma da hankali dayayi tareda sanin matsayin uwa data wuce kowace irin Wasa da reni.
A fadin duniyarsu shi kadai ne matum daya dayasan Maminsa ciki da bai,
Shi kadai ne yasan menene abinda ranta bayaso da Wanda ranta yakeso duk da Sam batada wani raayi ko buqatar kanta sai tasu Amma ahakan yasan kowane yanayinta abinda yake nufi Dan haka yafara tsayuwa sosai akan duk wani lamarinta Dan kuwa ankai bagirenda shine da Kansa yasa aka kawo masu Aiki a gidan har uku yakuma daukewa Mamin tasa Aiki ko daya na gidan.
Zainab taji dadin Hakan Amma duk da Hakan tasaba da ayyukan wasu aikin Dole itace takeyi dakanta
Kamar lura da tsaftar babban bangaren mahaifinsa da aka maida sabon guri tareda zuba komai sabo na Jin dadi rayuwa na masu arziki yanzu shine aciki
duk da bayaso Yana Mata fadan yin aikin Amma takasa barwa kowa aikin kulawa da duk abinda ya shafesa sbd tasan rikakken halinsa daya gado gun mahaifiyarsa na kyankyami da rashin son takura Dan kusan yafi mahaifiyar tasa qyanqyami da tsandar abubuwa nesa ba kusa ba.
Hakama tsaftar bangaren Haj maryamah har kullum itace da wannan sbd Haj maryamah din nada tsananin qyanqyami da tsanda,
Abincinsa Dana Haj maryamah shima har Koda yaushe nata kawai suke ci Dan haka dai kusan anyi baayi bane.
Tunda ya kammala secondary School aka fara yimasa shirye shiryen tafiya karatu UK Kuma bai musaba sbd shi Kansa yana buqatar zuwan duk da Maminsa na cikin ransa ta yadda zai tafi yabarta baa qarqashin kulawar kowaba.
##MAMUH#
#LOVE/AQEEL ASAD/
#IDON NERA
#ROMANCE
#AMAL.
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
8
Da farko Jin tafiyarsa Zainab tashiga damuwa sosai saidai kuma Tunda karatu ne zaije,
Qaruwarsa ce hakama duk cigabansa tanaso Dan haka sai ta danne damuwarta kawai ta boye a ranta Tunda kafin zuwansa duniya cikin kadaici take rayuwarta batareda kowa Dan haka yanzu dinma zata iya idan Allah ya yarda.
Dayake Yana karantar yanayinta Kai tsaye kwana biyu duk yanda take dannewa ya gane Tana cikin damuwa da kadaicinsa tin yanzu Dan haka sai shima yaji damuwar barin nata ita kadai din.
Kwana biyu yafara tunani da neman yanda zaiyi da lamarin Dan kuwa bazai taba iya tafiya yabar Mamin cikin damuwa da kadaiciba Kuma Hakanan zuciyarsa takasa nutsuwa da barin nata...
Ficewa tafiyar tafara yi daga ransa sbd ita,
Jin yake zai iya hakura da tafiya wata qasar ya zauna yayi karatunsa anan sbd ita
Amma Tunda Haj maryamah tafara fahimtar abinda yake Shirin faruwa na sauyin raayinsa dayake Shirin Yi take Hankalinta ya tashi sosai Kuma ranta yayi mummanan baci Dan kuwa wannan karon batajin zata sassautawa Aqeel din bare Zainab idai akan tafiyarsa ne.
Farko Kai tsaye ta tarasu a babban palonta da Aqeel da Zainab din wadda take zaune a kujera jiki amace
Ita kanta zaman kujerar sbd Aqeel Yana gurin ne take zaune akai Dan tuni yayi Hani da Zamanta a qasa Dan bazai iya yarda Yana ganinta zaune a qasa ba shi Yana kan kujera
Haka Haj maryamah tanaji Tana gani ta dauki wannan dokar tasa ta barin zaman Zainab din a kujera a palonta idan suna tare sbd kaucewa bacin ransa.
A yau din ranta bace yake sosai Wanda kusan su dukansu sun shaida Hakan
Dan haka palon yayi tsit suna jiran abinda zata fada musamman Zainab data Gama sanyi akan ko wane irin laifine tariga tasan itace zaace ta aikata Tunda akai kiranta.
Take jikinta ya sake mutuwa Dama kwanakin sai ahankali Tunda maganar tafiyar 'dan nata ta tabbata takasa gane kanta Dan Jin takeyi idan ya tafi kamar sun rabu kenan...
Kai tsaye Zainab Haj maryamah ta kalla kafin ta maida kallonta akan Aqeel Wanda ya kalla Maminsa yaga yanda duk tayi sanyi take zuciyarsa tayi Dan nauyi Dan haka ya dauke kallonsa daga gefenta ya gyara zamansa tareda hade dogayen fararen yatsun hannuwansa guri daya Yana Dan lumshe fararen idanuwansa cikin Yar damuwa da rashin Jin dadi.
"Aqeel maganar tafiyarka UK nakeson nasake Jin raayinka Dan kasan yanzu Kai ba yaro bane da zan zauna muna Abu daya koyaushe akan tafiyarka karatu,
As you can see manyanci yariga yaxomin Dan haka Dole zaka maida hankali kan karatu Dan is dakemun wannan nauyin na Aiki da kula da komai Nima nasamu na huta na fuskanci gyaran gobe na.. so me kace gameda tafiyar???
Ahankali ya sauke idanuwansa akanta tareda Dan sauke idanuwansa qasa Dan girmamawarsa ga manyansa itace Sam baya iya kallon idanuwansu ko tsaida kallonsa akan fuskarsu Dan haka Bayan ya kalleta kadan saiya sauke idanuwansa..
Muryarsa data fara zama budaddiya irin na mazan dasuka amsa sunansu maza yace"
Umma inaga zanyi karatun anan hankalina zaifi kwanciya....
Katsesa Haj maryamah din tayi da cewa"
Sbd Zainab kake ganin karatun naka anan zaifi??
Baya qarya kwata kwata sbd ilimin addinin daya ratsasa yasan illarta barema ba halayyarsa bace Dan tarbiyar da Zainab tayi Masa Sam Babu gurbatacciya a cikinta Dan haka ka tsaye yace"
Eh harda ita a dalilin.....
Ajiyar zuciya Haj maryamah ta sauke zuciyarta na wani irin nauyi da 'daci tareda mutuwar jiki
Bata iya cewa komaiba ta juya ta kalli Zainab cikin sanyin murya tace"
Kinji da kunnenki ko?
Haka kikeson rayuwar tasa ta qare batareda karatun dazai Gina Kansa ba dama mu gabaki daya..
Haka kikeso ko Zainab??
Kasa magana Zainab tayi saidai AQEEL dinne ya duba umman cikin nutsuwarsa yace"
Umma Mami batasan da wannan tunanin nawa Dana yanke ba...
Cikin qosawa da halayensu Haj maryamah ta katsesa da cewa"
Tashi kaje nagama maganata dakai.
Miqewa yayi ba musu ya fice a natse Yana Dan rufe idon wasu halayen na iyaye Dole sai kana musu uzuri da kuwa sun wuce ka tsaya gardama ko sainsa da su.
Bayan fitarsa ahankali Zainab ta dago cikin sanyi ta Dan kalli Haj maryamah tace"
Anty wallahi bansan da wannan tunanin nasaba,
Koda nasani Anty wlh kinsan bazan taba barin ya zaba abinda zai daqile cigaban rayuwarsa ba....
Kasa magana Haj maryamah tayi sai data dafa goshinta dake sarawa Yana saka kanta wani matsanin ciwo Dama gashi rayuwarta gabaki daya tagama juyawa Tunda tazama itace komai hatta hawan jini na wahalar Aiki da tunanin duniya duk ya kamata gashi acikin gidanma Aqeel da Zainab na neman sake Dora mata wani hawan jinin akan Wanda take fama dashi.
Cikin sanyi tafara fada ranta amatuqar bace Dan ko energy din fadan sosai batada Amma ranta yayi bacin da Zainab din tajima Bata ganiba Dan haka takasa cewa komai sai hawaye datakeyi masu zafi da ciwo Dan kuwa maganganu ne masu 'daci da zafi take fada Mata akan ba itace ta haifi Aqeel dinba shiyasa zata lalata Masa rayuwa..
Tun Tana hawaye karshe wata irin sheshekar kuka takeyi Wanda yake bayyanarda tsananin zafi da ciwon harma da 'dacin da maganganun suke Mata a zuciya.
Ita kanta qarshe Haj maryamah din kukan tafara wandata jima batayiba Dan kuwa kusan komaima Yana cin zuciyarta gameda Zainab,
Har cikin ranta tarasa yanda zatayi ta karba Zainab cikin zuciyarta,
Tanajin dacin yanda suke rayuwar saidai shedan a kafirar zuciya irin tata yasa komai nasu yaqi gaba bare baya kullum suna tsaye guri daya
Dukkaninsu rayuwarsu Tana guri guda a tsaye.
Koda Zainab ta fita Jin tayi zuciyarta na Kara daukan 'daci da nauyi Dan haka umma takira ta sanar Mata komai tareda bada tabbacin matuqar Aqeel bai tafi karatun datakeso dinba Zainab zata bar Mata gidanta.
Hankalin umma ya tashi sosai da hukuncin Haj maryamah din sbd ko yayane batason su rabu gwara dai suna taren wata ran kila su hade kansu duk da dai kusan kaman an qurewa Hakan Tunda manyancin ya fara shigowa musamman maryamah da manyancin Kam yariga yazo ita kanta Zainab ta girma ai tafiya sawun Yan Mata ma.
Umma tsufa yazo batajin zata iya doguwar tafiyar da zata zo gurinsu.
Kwana biyu akai gidan bbu Mai dadin Rai sbd Haj maryamah ta dauki zafi sosai Kuma ko Aqeel din Bata bawa damar zuwa gurintaba bare ya lallabata yabata hakuri...
Zainab ma sosai ta bawa zuciyarta hakuri ta fara janyewa daga Aqeel din sbd kaucewa fitina da bacin rayuka kamar Hakan Dan umma ta kirata a waya tayi Mata fada sosai Dan haka duk sai taji a Karo na farko rayuwar tafara fice Mata arai.
Lamarin dai sai qara munana yakeyi sbd Kai tsaye Aqeel yasake tabbatarda bazai tafiba yabar Mamin tasa Dan haka Kai tsaye Haj maryamah itama ta sanar masa ko yatafi ko Mamin tabar gidan...
Shock suka shiga kusan shida Mamin tasa Dan kuwa Babu Wanda ya taba kawo Hakan zata faru.
Zainab tayi kukan data jima bataiba,
Tayi baqin cikin wannan rayuwar,
Tayi kukan rashin uwa da Uba,
Tayi kukan rashin sanin dangin uwa harma Dana uban,
Tayi kukan rashin samun mijin aure Wanda Koda baida komai idan har zai iya zama da ita cikin mutunci da mutuntawa.
Aqeel ma kwata kwata bai dauka lamarin zaije can ba hankalinsa ya tashi matuqa da yanayin da Mamin ta shiga Dan haka shida Kansa ya Kira umma yasake fada Mata komai Dan ita kadaice zata tankwasa Mahaifiyarsa,
Hakama ya Kira hajiya Kaka mahaifiyar Dadynsa itama tazo tabawa haj maryamah hakuri Amma dai itama Tana Bayan Aqeel din yatafi karatu Bata yarda da karatunsa anan ba.
Rigima dai Bata qareba saida umma ta taso daga Cameroon tazo aka zauna akai magana tareda tone tone inda anan Aqeel yaji asalin matsayin Maminsa ba 'yar aikin gidan bace qanwar mahaifiyarsa ce Uba daya.
Innalillahi wainna IlayhirRajiun......
Wani irin fitinannen tsoro da mamaki ya shiga na wannan mummanan alaqar da iyayen nasa Mata biyu suka gudanar tun qananun shekaru har manyanci....
Tsananin tausayi da sabuwar kaunar Maminsa ne ya shigesa Wanda a gabansu saida ya zubda qwallar wani irin 'daci da raunin da zuciyarsa ta samu na Jin wannan babban lamarin.
Kai tsaye ya amince da barin qasar zuwa UK Dan kuwa bazai taba barin sbd shi Mamin tabar gidanba Dan kuwa yasan batada gurin zuwa.... Amma a gabansu ya shimfida wani kyakkyawan alqawari Mai girma na cewa duk ya dawo zai dauki Maminsa har abada nauyinta zai dawo kansa yadauke musu nauyinta tun daga na jini harna jiki.
Da farko Haj maryamah Bata fahimtaba saida umma tasake nuna Mata illar Hakan da gaba zaa samu Dan haka tace Bata yardaba
Zainab qanwarta ce a hannunta zata zauna sai aure idan tanada rabon yinsa kenan.
Kalmar ta Sosa zuciyar Aqeel yakalli Mamin wadda take zaune batada abin cewa sai yanda akai da ita.
Take wani ciwo da daci yakuma mamaye zuciyarsa Dan haka baice komaiba aka bar zancen ahakan.
Umma sai datai kusan wata daya kafin ta tattara ta koma Cameroon tabarsu Bayan tayi musu Yan nasihu Amma dai kusan kowa yanzu zuciyarsa ta cire Rai daga Dan uwansa.
Zainab gabaki daya yanzu tasake zama wata iri tayi sanyi sosai fiyeda baya Dan an ankarar da ita ko zaman datakeyi gidan alfarma ce akeyi Mata
Batada wani amfanin da zaa mutunta Dan shi saima tunatar da ita da akai ita din ba kowa bace face Yar Aiki a gidan wadda zaa kora aduk lokacin da akaso.
A yanzu gidan Bayan Aiki da abinda aka sakata Yi Babu abinda takeyi
Data Gama take komawa inda dakinta yake ta zauna ta kame kanta.
Shi Kansa Aqeel yanzu tsakaninta dashi sai idan yazo dakinta da safe gaidata kamar yanda ya saba Amma duk wani alaqarta dashi ta Dan ja baya dashi.
Wannan sabon halin data shiga ya sakasa damuwa shima Amma Kuma shima cikin nasa yanayin na damuwar yake Dan haka kowa dai yazama sai ahankali gidan.
Ta bangare daya karatunsa na addini da malaminsa Kuma ubansa malam Sanda yayi zurfi,
Malam Sanda A yanda yakejin Aqeel shima tamkar shine ya haifesa musamman Dama baida da ko daya ba taba haihuwaba,
Asalinsa Dan Billiri dake gombe karatun almajiranci ne ya kawosa cikin gombe daga Nan aka ringa kaisu garuruwa almajirancin qarshe ya tsaya anan Jigawa harya girma yafara Dan sirkawa Dana Biko kadan kadan haryayi karatun secondary Amma daga Nan