Showing 27001 words to 30000 words out of 149977 words

Chapter 10 - IDON NERA BY MAMUHGEE CMPLT.txt

25 Nov 2024

6543

haka hankalinta gabaki daya nakan 'yarta MARYAMAH da itama tana Dan samun kuzari da kulawa sosai Dan kuwa Aqeel babu abinda bai tanadarba ya biya kafin ya wuce din.


Baa kawo mata abinci daga gida Dan haka itace take siyan abincinta taci anan duk da nata jegon dakuma damuwar rashin miji duk yasa cikinta a bushe yake batason cin abincin,
Wanda ma take nace tana siya tanaci sbd tanason tasamu Nononta ya taru MARYAMAH tasamu nono.


Wasu daga cikin maqotanta sunzo har asibitin sun dubata da yarta duk da baa bada babyn
Kuma dazasuzo kusan duka sun kawo mata abici wasu kudi harda kunun haihuwa mai kyau suka kawo mata Tasha kuma taji dadinsa sbd ya taimaka mata gurin samun nonon Dan ajiyewa tai tana shansa kwana biyu kafin yaqare dayake dakin akwai fridge harma da heater ta ruwan zafi.


Samun ruwan Nononta yasa babynta tafara samun kuzari da lafiya sosai Dan haka takesan nono sosai gashi Daman ba laifi babyn tanada Dan girma kadan ba irin sosai takeda rashin girman Nan ba ko kadan.


Acan gidan haj maryamah kuwa umma sati daya tayi ta komawarta bayan tasake zuwa asibitin so daya kafin ta wuce.


Aqeel kuwa ya Isa lfy yanata kokarin fara karatunsa Amma yakasa samun Maminsa
Yayiwa ummansa magana ta sanar dashi baa sallamosuba tukuna dole ya hakura harsu dawo gidan yasamu ko ummansa zata hadasa da mamin tasa a waya.


Haj maryamah kuwa tini ta tattara ta wuce Abuja itama kafin tawuce tazo asibitin ta sake dubata so daya taqara Bata wasu 10k din ta wucewarta bataredama zainab din tasan gari zata Bari ba.




Ahankali ahankali Saida zainab ta share kusan sati uku a asibitin kafin aka sallameta ta nufi gidanta da 'yarta.


Gidan yayi datti sosai dayake lokacin iska ne Dan haka dole ta goya Maryamah tafara aikin gyaran gidan.


Saidata gyare koina ta share ta wanke kafin ta fito ta samu yaro ya siyo gawayi ta Dora ruwan zafi tayi wanka tayiwa maryamah da aka koyo mata yanda zatayi mata daga asibitin.


Ruwan zafin Tasha da Lipton ta kwanta suka Dan samu bacci tana tashi maqotanta Wanda Basu samu zuwa asibitinba suka shigo sunatayi mata barka da qarin gaisuwar malam.


Da daddare Dole ta dafa shinkafa dayake akwai sauran abinci dasuke dashi.


Da manja taci shinkafar tasake Shan ruwan Lipton tagama sauran ayyukanta ta kwanta.


Washe gari ma haka ta wuni ita kadai a gidanta daga ita sai 'yarta dare yayi suka kwanta abinsu.


Haka ta runguma rayuwarta data 'yarta data zama sanyin idaniyarta Kuma sanyin zuciyarta,
A yanzu duniyarta 'yarta itace babban abinda yake gabanta,
Batada buri ko buqatan daya wuce inganta rayuwar yarta data warware abinta tayi mulmul sbd nono mai kyau da sauran madarar datake Bata wadda har lokacin sunada sauran kusan gwanwani biyu da Basu fasaba.


Aduk lokacinda tayi sallah iyayenta da Malam da Aqeel sune farko a adduarta da 'yarta kafin kanta,


Ayanxu wata rayuwa take gudanarwa ta kadaici da rashin kowa,


Batada wani farin ciki ko jin dadi
'yarta kawai take kalla taji qwarin gwiwa da farin cikin rayuwa,


Ba laifi tana hulfar arziki da maqotanta duk da babu Wanda ya taba zuwa yabata taimako ko tallafi daga cikin mutanen malam harna Aqeel Dan haka taci gaba da lallaba abubuwan datake dasu Shi abincinta tuni ya qare dole kayayyakin gidan ta tattara ta Saida tabar katifar kwanciyarsu kawai da kayan kitchen.


'yar sanaar Saida gawayi da kayan Miya tafara Amma mutane sun maida komai bashi take suke kwashe komai data kawo Amma bashi
Qarshe Kuma wasu da yawa basa biya haka zataita yawon bin bashin kudin Amma basa bayarwa koyaushe da qaryar da zasu fada.




Babu inda sanaar taje komai ya karye aka rasa kudin gabaki daya Takoma tana kame kame.


Watanta uku da dawowa hayarsu ta qare masu gidan suka Bata notice dole tafara tunanin barin gidan.


Batada gurin zuwa,
Batasan Ina zata da jinjirar 'ya ba gashi bazaso 'yarta tayi tashin garari ba.


Har notice yacika batada gurin zuwa,


Ana hakan ne Daren wata asabar wani mummunan tsautsayi ya sameta na shogowar qato gidanta
Allah bai basa ikon yimata komaiba saidai fuskarta ta kumbura da irin Marin daya ringa zabga mata sbd taqi yarda yayi Mata komai
Qarshe haka ya gudu bai samu damar lalata mutuncintaba haka itama Bata samu taga fuskarsaba.


Tunda take hankalinta bai taba tashi da tsoroba irin hakan Dan haka gari na wayewa takai maganar gurin Mai anguwa Amma qarshe dai haka mutuncinta ya zube babu wani takamaimai sheda ko tabbacin abinda ta fada din sbd kusan duka anguwar ansan juna
Basuda samari duka dattijai ne da tsofi
To tayaya take tunanin zasu yarda kowa da mutuncinsa zai shiga yayi irin hakan.


Qarshe hakuri aka Bata akan saidai daga wata anguwar aka shigo aka Mata hakan.


Wannan lamarin ya sake firgita tsayuwarta ta rasa inda zata saka kanta da 'yarta,
Tsoron gidan da anguwar ma takeji kwata kwata Dan kuwa duka rayuwarta ko yanda ake fyade Bata saniba sai yanzu da hakan yaso faruwa da ita,


Ba kanta takejiba
MARYAMAH dinta takeji tunda fyaden yanzu har yara qanana Ana yiwa,


Wannan tunanin ya toshe dukkanin wata basirarta da tunanin,...


Tunaninta kan rayuwarta na baya yakoma,
Da wani abun yasamu 'yarta gwara taje tayita bauta har tsufa acan din.


Batada zabi, batada dabara, batada mafita tunda ko abin kanta batada dolenta ta juya ta fuskantar bayanta.


Littafan addini da Alqur'anan malam masallacin anguwarsu ta bada aka aje Dan masu karatu hakama siturunsa badawa tayi akaiwa dattijan anguwar kyauta
Sauran kayan tarkacenta na kitchen saidawa tayi wasu Kuma ta bada sbd duk ba wasu kayan kirki bane.




Koda ta iso babban tsohuwar kurkukunta wato gidan haj maryamah Adam Asad babu kowa gidan sai masu gadin gidan biyu.


Dukkaninsu sun santa Dan haka babu Wanda ya hanata shiga saidai Basu bari ta qarasa cikiba dan koina a rufe yake Saida aka Kira Haj maryamah din tace abarta tashiga tukuna suka bata mukullan gidan.


Kai tsaye bayan ta bude koina inda tasan kanta a dah can takuma Kai kanta goye da 'yarta.


Babu inda baiyi wata irin quraba da datti a gidan,


Kallon kanta tayi taji hawayen baqin ciki na gangaro mata Dan kuwa tasan rayuwar data Bari ce tadawo
Amma Kuma zata iya kowace irin wahalace akan MARYAMAH dinta tasamu rayuwa a natsatsen guri da rayuwa Mai kyau.


Babban aikinta na farko data fara komawa shine aikin shara..


Goya MARYAMAH tayi ta rufeta sbd qura tafara aikin shara da gyaran koina.


Har harabar gidan sai data share ta gyare koina tas tadawo ta gyara Mata dakin ta wanke toilet tukuna ta sauke Maryamah sukayi wanka tazo tayi sallah ta kwanta daqyar tana rintse idanuwanta sbd ciwon baya Dana kwankwaso mai qarfi daya taso Mata.
##MAMUH#
#MARYAMAH AMAL IDON NERA
#MARRIAGE/HOTLOVE
#ZAINAB IDON NERA






*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯
Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*πŸ”₯
Billyn Abdul


*IDON NERA*πŸ”₯
Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯
Safiya huguma


*KI KULANI*πŸ”₯
Miss xoxo


Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171
Maryam sani
Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*πŸ”₯
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
15
Babu komai na abinci a gidan tunda ba kowa Dan haka sai data fita ta siyo bread da lemu tasha takwanta ita kadai a qaton gidan Kamar mayya.


Kusan ko anan dinma a tsorace take,
Tunda wancan lamarin ya faru da ita kowane dare a firgice take kwana rungume da MARYAMAH dinta.


Washe gari haka ta wuni zaune shiru Kamar hoto
Sai yamma sosai saiga drivern gidan shafi'u yazo da kayan abinci masu yawa an zuba a store.


Koda aka kawo abincin harya kwana biyu Bata tababa sbd babu gas Kuma batason tabawa tunda ba cewa akaiba nata ne.


Kullum bread da lemu ko garinta take siyowa Tasha tayi renon yarta dare yayi su kwanta.


Sai datai sati biyu ahakan saiga haj maryamah din tadawo da masu aikinta har biyu, daya yarinya dayar Kuma dattijuwa.


Zuwansu yasa akayo refilling duka cylinders na gidan da gas aka kawo dole itace ta Dora girkin tunda sun iso a gajiye Kuma su din Basu taba zuwa Nan ba acan Abujan aka Samar Mata su dan haka a gidan Basu San koinaba da komai.


Dayake bata taba tsallake inda takeba taje bangaren Haj Maryamah sai ya zama bangaren nata yana buqatan gyara sosai.


Masu aikin nata ne sukai aikin gyara Mata koina a sashen nata suka wanke komai tareda gogewa suka kunna AC Ac dasu fridge da sauran kayan dayake aiki da wuta.


Abincin Haj Maryamah din data Gama ta Basu suka jera Mata a dining ita sai daga baya bayan ta tabbatarda tagama cin abinci da hutawa taje ta gaidata tana rungume da MARYAMAH dataqi bacci tanata rigima sbd aikin girkin dasukai sunsha zafi.


Kallon zainab Haj Maryamah din tayi dakyau kafin ta maida kallonta kan yarinyar daketa Kika duk ta ruda palon.


Kasa magana tayi sai kawai ta amsa gaisuwarta tareda sallamarta Dan kukan gabaki daya ya rudasu su dukan.


Zainab na fitowa daki ta nufa tayiwa MARYAMAH din wanka ta canja Mata kaya cikin kayanta dasuka fara Mata kadan sbd bayan kayanda Aqeel ya siya Mata batada wasu kayan gashi tanata girma.


Baya tayi Mata wanka bacci tayi sai kawai ta kwantar da ita ta fito taje ta gyare kitchen din data Gama aiki ta tattara komai tadawo daki itama tai wanka tayi sallah ta zauna tana kallon MARYAMAH dake bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankalin irin na yara.




Da daddare kasa nutsuwa da gyaran da shafa Mai aikinta tayi Mata Haj Maryamah tayi sbd akwai qura sosai Sam aikin baiyiba.


Fada sosai tayiwa shafa'atu din kafin qarshe tasa aka Kira zainab itace tayi Mata gyara Mai kyau dayasa hankalinta kwanciyar tasamu ta kwanta.


Washe gari zainab bata fitoba sbd batasan me zatayiba idan ta fito
Babah ladi itace take aikin girkin gidan
Shafa'atu Kuma tanata aikin shara da gyaran koina Dan haka saita Kama kanta a daki musamman dataga suna Mata kallon wulaqanci Dan daukarsu itama Mai aikince
Gashi sunga an kushe gyaransu ansaka tayi sun dauka shiga tafisu samu agun hajiyar gidan basusan wulaqanta tafisuba.




Duk uban aikin dasuketa fama dashi kwana biyu babu Wanda Haj Maryamah ke yabawa sbd tsaurin raayinta da yai yawa,


Duk aikin dasuke Mata Dama acan Bata Jin dadinsa Kuma tana nunawa Koda yaushe Amma sbd su kadaine sai basa damuwa sunyi sabo da halinta shiyasa suka Dena damuwa,
Amma anan duk aikin dasukai bayayi saita saka zainab tayi Mata wani sai hakan yasa sukejin daci da zafin zainab din a ransu,


Musamman babah ladi data fito fili ta bayyanarda rashin kaunar zainab din dake ranta,
Ita shafa'atu tana Dan taqaitawa sbd MARYAMAH data shiga ranta Dan tana tsananin kaunar yara.


Girkin abincin gidan a hannun babah ladi yake Dan haka idan tagama kullum Dan kadan take bawa zainab
haka zataci ko Bata koshiba zata Sha ruwa ta Kama kanta gashi tana shayarwa tana buqatan abinci sosoi gashi mukullin store a hannun babah din yake koyaushe da gayya take yawo dashi a jikinta duk inda zata.


Idan har tasamu taci abinci isashe yanda ya Kamata to itace tayiwa Haj Maryamah girki aranar dan bako yaushe haj maryamah din ke Jin Dadin abincin babah ba.


Shi gyaran bangarenta Kuma tuni yadawo kan zainab din da batason na shafa'atu Kuma tanada qarancin yarda shiyasa zainab kawai ke Mata gyaran daki taji hankalinta akwance da dukiyarta.


Bayan gyaran sashen Haj Maryamah harda abincinta yadawo kanta sai gashi kusan duka aikin gidan kadan ne basa kanta ga MARYAMAH da rigima sosai harma da qyuya Dan haka duk aikin dazatayi tana bayanta ko hannunta.




Ahakan suka fara Jan lokaci sosai suna wani irin mugun zama a gidan tsakaninta dasu babah..


'yarta MARYAMAH tayi wayo sosai harta iya zama da rarrafe Amma batasan kowaba bayan mahaifiyarta,


Bata sabu dasu babah ba Dan basa janta ajiki bare hajiyar gidan da iyakacinta da ita idone.


Aqeel kuwa yayi rokon,
Yayi neman ummansa ta hadasa da mamin tasa Amma kullum uzuri take basa
Har waya yace asiya abata Amma duk dai hakan bai samuba Amma tunda dai ta sanar dashi suna lafiya hakanma yasa hankalinsa ya kwanta.




Babbar matsalar da aka fara samu a gidan shine tsanar da ake nunawa 'yarta wadda ko sunanta basa Kira sbd sunan hajiyar gidan ne da hakan qarfi da yaji suke Kiran yarta da KE, kokuma 'YAR ZAINAB..wannan kalmar itace abinda yake sosa ran Zainba aduk lokacinda suka Kira MARYAMAH dinta da hakan,


Tana danne wannan lamarin ne matsala ta bullo tsakaninta da Haj Maryamah akan MARYAMAH din datake zuwa da ita gyaran bangarenta Dan yarinyar nata barna sosai.


Tun lamarin na dannuwa a ranta har abin yafara yimata yawa Dan kuwa kusan kowa a gidan kyarar Mata 'ya sukeyi.


Daga ita har yarta kamar wasu almajirai suke a gidan Dan kuwa kayansu na sakawa tuni suka mutu wasuma duk basa shigar MARYAMAH din Amma ahakn take saka Mata su tunda basuda wasu.




MARYAMAH sai datai kusan shekara biyu Ta yayeta sbd yarinyar itama yanayin rayuwar dasuke ciki yafara tabata,
Sam yanzu batada walwala ko sakewa yarinyar,
Duk da qarancinta tasan batada sakewa komai tayi na barna dukanta su babah da shafa'atu sukeyi tun zainab na kauda Kai har tayi magana sai abin ya zama fitina
Dama babah mutuniyar banza ce gidan abinci a Tasha takeda Jin gida masu kudine zaa Kai yar aikin abinci ta rufe shagonta tazo ta karbi aikin shiyasa take tsula tsiyarta son ranta tunda Haj Maryamah din Bata wani zama ba ruwanta da Yan aiki gashi yanzu itace shugaban masu aikin gidan Dan haka take zuba tsiyarta son ranta.


Zainab rayuwa a gidan tafara yimata tsanani,
Komai ya juye a rayuwar gidan ba kamar da ba,
Idan zata sashen Haj Maryamah ta dena zuwa da MARYAMAH 'dinta sbd gudun fitinar dazata biyo baya idan tayi Mata wata barnar datafi fasa Mata laptop datayi ta aikinta.


Acan dinma idan tabarta kafin Takoma sai ta tadda bacin ran wani abun
Duk tabi ta fige da masifar gidan da yanzu komai ya lalace mata,


MARYAMAH sbd tsangwama da kyarar datakesha yasa gabaki daya ta rasa walwala da kuzari tareda sakewa irinta yara,
Idan har ba ajikin uwarta takeba Bata wani dogon motsi a gidan.


Wannan yasa itama zainab din ta tasa kuzarinta gabaki daya suka koma kamar Yan gudun hijirar gidan kullum suna daki kamar masu abin kunya.


Ana haka kwatsam Allah yayiwa mijin Haj Maryamah yace ta tattara tadawo Abuja gabaki daya.


Da farko shafa'atu aka fara sallama sbd idan Takoma Abuja Bata buqatar ya aiki da yawa sbd hutawa takeson Yi batason hayaniyarsu Dan can gidan baiyi girman wannan ba da bazakaji motsin masu aikinbama.


Ganin an sallami shafa'atu yasa hankalin babah tashi Dan ta fahimci zaiyi wuya a kori zainab duk da gata da 'ya da Bata barin tayi aiki dakyau.




Babban tashin hankalin farko data fara fuskanta akan tafiyar tasu Abuja shine Haj Maryamah data Kira umma akan zata Aika Mata da MARYAMAH Qarama acan Cameroon bazasu da ita Abujan ba.


Bugawar da zuciyar zainab tayi yasata dafa bango tana Dan bude idanuwanta dake Mata dishi dishi.


A gabanta umma da aka Kira Kai tsaye itama tace bazata iya riqon MARYAMAH dinba sbd tsufa yazo Mata Kuma dasuka riqe uwarta tun tana jinjira me ta saka musu dashi Banda butulci Dan haka ita ma wanna halin uwarta zatayi itakam bazata iyaba.


Haj Maryamah ma Kai tsaye ta nuna zainab bazataje da MARYAMAH dinba idan har umma bazata karbetaba to gwara zainab din ta nema dangin mahaifinta ta miqa musu ita.




Tunda zainab take Bata taba Jin daci da radadin zuciyaba akansu sai wannan karon,


'yarta ake ture turen inda zaa Kai kowa nacewa baya son saikace wani mugun abun,
Me tayi musu da tsanar dasuke Mata zata shafa 'yarta hakan wadda batasan komaiba.


Tafiyar na matsowa umma ta Dage akan bazata karbi maryamah dinba,


Kukan da zainab tayi Saida takai idanuwanta ma basa gani sosai,
Tayaya zata iya bada qanqanuwar marainiyar 'yarta har Cameroon itama taje ta taso Acikin qangi da wahala.


Kukan Rashi iyaye Dana Mijinta tayi tareda na Aqeel Wanda tuni ta cire Rai daga Kansa itada yarta.


Hada dukkanin tsumman kayanta tayi guri daya Dan tasan rigimarda zaayi idan tafada raayinta na bazata taba rabuwa da 'yartaba,
Idan har Haj Maryamah zataje Abuja da ita to zataje da yarta,


Tasan hakan zai kawo rigima tunda ansaba takuma san ran kowa zai baci Amma bazata iya barin arabata da yartaba.




Rigimar kuwa akayi sosai tareda bacin rayika alokacinda ta sanarda Haj Maryamah bazata tafi bada MARYAMAH dintaba.


Umma ranta kusan yafi na Haj Maryamah din baci sbd mamaki da takaicin zainab take tafara jero Mata gorin irin rokon da Aqeel yayi musu akan su amsheta ta zauna gurinsa shine yanzu an zabar Mata rayuwar sauki da Jin Dadi zatace bazata rabu da yartaba,
Ashe 'da yanada dadi shine ita ta raba haj Maryamah da nata Dan kullum cikin fada yake da mahaifiyarsa akanta.


Haj Maryamah kuwa tsabar takaicin da baqin ciki Kai tsaye ta Bata zabin Idan bazataba Saida yarta to tayi zamanta Amma tasan Wana gidan an saidashi gabaki daya har masu gadi tafiyarsu zasuyi.


Irin cin zarafi da tozarcinda umma tayi Mata dakuma maganganun Haj Maryamah din yasa ta sake hada kayanta guri daya.


Haj Maryamah ganin Bata bar gidanba yasa tayi tunanin ta aminta da tafiyar MARYAMAH din Cameroon Dan haka tasa babah ta shirya Dan itace zatakai MARYAMAH din har Cameroon.


Sai ranar tafiyar tun kafin asuba babah ta shirya sbd sammako zasuyi a tafiyar.


Ayau zainab ta fito tayi magana Kai tsaye cewan bazata bada 'yartaba,


Tsananin fushin da haj Maryamah da umma suka dauka yasa akai hayaniya mai girman gaske da har tasa Haj Maryamah sakarwa zainab Marin daya bawa kowa tsoro.


Kasa hawaye zainab tayi sbd zuciyarta datakai qololuwar 'daci da qunci,
Ayau ta tabbatarda har abada bazasu taba kaunartaba sbd qiyayyar dasuke Mata a jininsu take...


Maganganun Haj Maryamah suka rufe ganinta saidai batajin zata iya barin ko gari ya waye tunda umma tabata umarnin barin gidan daga ita har yarta dasuke neman aibatawa sbd rufewar zuciya.


Daurin kayanta ta dauka ta fito daga gidan tana Jin zuciyarta na tiririn zafi da azaba.
##MAMUH#
#SISTERS#
#MARYAMAH AMAL IDON NERA
#DR AQEEL ASAD
#LOVE/HOTLOVE






*_ZAFAFA BIYAR_*


*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯
Hafsat Rano


*DAUDAR GORA*πŸ”₯
Billyn Abdul


*IDON NERA*πŸ”₯
Mamuhgee


*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯
Safiya huguma


*KI KULANI*πŸ”₯
Miss xoxo


Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200


ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN


0022419171
Maryam sani
Access bank


Shedarka ta 09033181070


MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN


09166221261


πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+22799643131


Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*πŸ”₯
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
16


*_MG'S SKINCARE_*πŸ”₯πŸ”₯
Kunji takennan kunsake jinshi shin yar'uwa nace wai haryanzu baki jaraba products dinsu baπŸ˜΅β€πŸ’«yar'uwa mace fa yar ado da kwalliyace koda kina dakyau akace kikara da wanka😍sufa kayan mg's basa bleaching duka kayansu πŸ’― natural ne sannan organic zasu gyara sukuma goge Miki jikine kawai yakara bayya ar da ainihin zallar Madarar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login