Showing 60001 words to 63000 words out of 100319 words

Chapter 21 - Masarautar Jordan Book 1 Complete Document .txt

kuwa kamar tukunyar miya musaman nan ɗin nan" buge hannunshi nayi tare da tura bakina, nace.
"Dudu! Kafita idanuna mana kasani a gaba da maganar hancina ya cika girma. Sai na gayawa Ummina."
"Toh kajina har kun fara raba halin ko? Maza karɓa wannan kisha, yana taimakawa gun haihuwa."
Wato wannan alamarin yana matuƙar kwantar min da hali, domin kuwa bana jin daɗin Abba da matarshi Amma Umma babu ruwanta, mamie uwar yaɓ zakale kan ba acewa kome.
"Eyye lallai kuwa, wato ga bawa nan, kinga banza. Bari kisa min d'a aikin akan cikin shegenki, toh wallahi a hir ɗinki dan na rantse da Allah kika kuma samin ɗa aiki sai na miki rashin mutunci, tashi muje shashashar banza kawai, karuwa tasi ba fasinja."


"Alhamdulillah ni cikin shege nayi wasu kuwa, abinda suke aikatawa na shirka yafi karfin kare yaci." na gaya mata tare da mikewa, aikuwa a zuciye tayo kaina zata dake ni, Ummi tace.
"Amma rashin hankalinki ya girmama Nuratu zaki daki Mace da ciki ko? Hmm lallai kuwa bar ganin kina abu bana magana, kika sake na fusata wallahi kika taɓa min Y'a da ciki sai kinyi danasani, dan ko Badaru ne ya taɓa min ita sai duniya tajimu dashi dan ni yanzun ina zaune da kowa sabida Safinatu ne idan babu ita wallahi bazan zauna da shi ba, kisa kai ki ficce min a falo mara mutunci."


Bata taɓa ganin ɓacin ran Ummi ba sai yau, dan haka tuni tasa kai ta fita tare da kwafa, zata rama. Kaina ne a sunkuye ina zubda kwalla, sam bana son fitina, shi yasa har na jure wahalar da Samudawar Ashraf gashi yau gidanmu ana rigima sabida ni, Allah kaɗai yasan ma'anar kwafar Mamie dan naga Babu Allah a cikin alamarinta.

Mika min hank akayi na ɗago kaina, ina kallon Anim, bansan lokacin da na galla mishi harara ba, tunda na fara magana yake sake son yaji me zance amma bai samu danar haka ba, dake Ummi tana gama gayawa Mamie magana ta shige ciki, shi yasa basu gami ba, jin hannunshi nayi a cikin zanina yana shafa cinyata, bansan lokacin da na tsinka mishi mari, dafe kuncinsa yayi. Yashafo marin yakai bakinsa ya sumbata, sannan ya kai kan bakina na buge hannun, leka kofar Ummi yayi, da sauri ya sumbaci goshina, na ture shi, nace.
"Bana cike da iskanci Mugu Azzalumi kawai kai ko tunani haɗuwarƙa da Allah bakaƴi sai iskanci da kasa a gaba wai kana kira da so."


........


Oum Muwadda......
[2/5, 7:51 PM] +237 6 72 92 59 08: _HAZAƘA WRITERS ASSO_


*_MASARAUTAR JORDAN!!!_*
_Jordan Historical_
*©2020*
*BOOK ONE*
_Na sadaukarda wannan shafin ga Iyaye mata masu fafutukar kare Yaransu....A cikinsu Har da Mahaifiyata Allah ya jikanki da Rahama👏_


~_Ina muku fatan alkhairi Masoyan MJ daga Whatsp,Wattpad, Face book nagode_ ~

Page.٢٩-29


Daukar ɗaƴa yayi ya musu addu'ar da musulunci ta tanada domin ayiwa jarirai, yayiwa tafarkon wacce aka sayawa bam pink, sannan ya ɗauki wacce aka sanya mata purple bam, yayi mata kana ya maidasu cikin gadon.
"Dudu! Don Allah ɗaukesu a hoto sun min kyaune zan ɗaura a Status ɗina."


Tsuke fuska yaƴi tam sannan yace.
"Koda wasan wasa kar naga hotonsu akan social media, dan zan saɓawa kowa."

Tura baki tayi sannan tace.
"Plss zan ɗaura akan Dp ɗina,"
Hararar ta yaƴi sannan ya fito daga ciki ta biyo bayanshi, tana murmushi tace.
"Abban twins!"
Murmushi yayi ya tsaya, "Plss"
Mika mata wayarshi yayi ya barta ta koma, wani abinda ummi tayi ya kara haɗe kanmu ba kome bane sai cusa mana soyayyar junarmu, idan abu yasamu mutum ɗaya kama ya samu saurane, duk wani dabi'a irinta sako da sako duƙ bamu dashi, sam yadda take da sanyi hali haka muma muƙa ƙasance dan ita har wasu nace mata baci suna maryam ba, amma ko yayya ne mu dai muna son Uwarmu haka, dan tayi na mijin kokarin ganin mu tashi da tarbiya, akasin kaddara da ya faɗa min ne kawai zan iya ce wani abu.
D'akin ya dawo yasame Umma tana son komawa gida, Ummi da Sophia tare da Nanah suna nan, Abdul ya dawo da Umma ya kuma kwasosu Batul ya kawosu. Zuba min ido Khalil yayi sannan ya dubi Ummi yace.
"Allah yasa karshen matsalarta kenan"
"Amin" duk ɗakin suka amsa,
"Toh Ummi ina yaran suke?" Inji Khalilah, mika mata wayar Nanah.
"Duba gallary,"
Da sauri ta amsa, har suna rigayen karɓa, duba gallaryn tayi sai ga hotunan yaran,
"Masha Allah! Haka yaran suke da kyau,"
Aikuwa Khalil ya amshi wayar ya shiga bin hotunar yaran, sai murmushi yake sakewa.
"Ummina Didinmu ce ta haife su, masha Allah bari na ɗaura a Tweet.."
"Sai kasan amsar da zaka bawa Babansu dan Dudu ya hanani."
Inji Nanah,
"Ahtoh na hakura, tunda yace kar asaka."
Duk wannan yana cikin tsarin tarbiyan Umminmu domin idan babba yace kar ayi abu toh karami bai isa yayi ba, kuma koda laifi karami yayi bata taɓa kallonshi zata barshi da yayunsa su masa faɗa, sannan itama ta ɗaura da nasiharta, tunda Ummi ta haifeni har na girma Ummi bata taɓa dukana ba, sai tsawa shi yasa lokacin danaje jordan nasha wuyar jibgar sa suka min.


Basu bar Asibitin ba sai dare, aka bar Ummi, bayan tafiyarsu Dr HZ. Katagum ya shigo duba ni, sam Ummi bata san shine yayita hidima ba, cikin mutunta juna suka gaisa sannan. Ya kama abinda ya kawo shi yana gamawa yafita, ita kuma ta cigaba da laziminta.


***
Washi gari dakin ya kuma cika da yan uwana. Da mutanen arziki tun safe Abdul ya kira Nannah ya gaya mata haihuwar.
Tsabar murna kamar tafito ta wayar. Karfe biyar na yammacin ranar na farka, a sannu abubuwan da suka faru ya dawo min, lumshe idanuna nayi tare da fashewa da kuka. Kukan nawa ya sanar musu farkawata, Batul ce ta fita. Taje ta kira likita. Can sai gasu tare da Dr Katagum, yana shiga yace.
"Ku haɗa min tea! Sannan ku ɗan bamu guri, amma Mama karta fita ta tsaya dan taimaka min."
Duk suka fita, shi da Ummi aka bari. Ya ɗauko auduga tare da wani almakashin ɗaukar auduga, ya karɓi wani kofi. Da kanshi yakawo kwanon silve ya mikawa Ummi sannan ya umarce ni na buɗe bakina, ina ji ina gani ya wanke harshen tass, sannan ya kalle yadda nake kuka sosai,taɓe baki yaƴi cikin gatsali dan matsalarshi bai iya magana ba. Yace
"Yanzun ɗan wannan abin kikewa kuka, kika iya haihuwa sai wanke baki ne kike zubda hawayenki, toh ai sai ki ɗaura ɗammara dan yanzun zaki sha hot tea."
D'ago idanu nayi tare da kallonshi. Karɓan tea ɗin yaƴi sannan ya kurɓa, kana ya mika min.
"Ki godewa Allah da yabaki Jarumar Uwa! Inda nine da zafi zakisha, dan haka zuwa an jima zan dawo ki adana hawayenki"
Yana gamawa ya juya ga Ummi yace.
"Sannu Mama! Zaku iya amso mata yaran ta fara shayar dasu."


"Toh mun gode sosai," tace masa, har zai fita tace.
"Don Allah kaine Dr Katagum!"
Cike da jin kunya ya gyaɗa kanshi.
"Mungode sosai, da Hidima Allah yasaka da alkhairi."
"Amin, Mama!" yace sannan yabar ɗakin, da kallo nabishi sannan na kalle Ummi ina jiran karin bayani, karɓan tea ɗin tayi. Taje ban ɗaki ta haɗa min ruwan zafi sannan ta fito ta riko hannuna muka shiga ciki, Lallai na yarda Ummi Jarumar Uwa ce, ita da kanta tamin wanka tass bayan ta gasa min jikina yadda ya dace, sannan ta fito tace.
"Ki wanke jikinki kuma kisa ruwan zafi a gurin, banda shirme dan matuƙar baki gyara gurin ba kece a ruwa. Babu abinda ya dame ni."
Murmushi nayi a raina nace.
*Ummi kece kuwa me shiga damuwa*
Wanka sosai naƴi sannan na fito, riga da zani ta bani na saka, bakina yaƴi nauyi, dan haka bana magana sabida harshena.
Zama naƴi sai gasu da yaran, tea ɗin na karɓa ina sha tare da matse kwalla, ina gamawa ta mika min magani nasha, sannan ta shafa mun bonjula, akan harshena, ina gamawa tana samin yarinyar farko aƙan cinyata, d'ago kaina nayi na kalleta, murmushi tayi sannan tace.
"Idan da duniya zasu haɗu domin dakatar dake alokacin, tabbas rabonsu zan iya kashe mutumin da ya nemi dakatar dasu, Safinah rabon y'ace nada zafi tafi kowacce halitta zafin, Kuma ki duba da kyau yara biyu, ki godewa Allah da ina raye haka ta faru, da bana raye ko kuma Dudunki ba me kula bane, nayi imani da Allah mutuwa zakiyi, tunda kika ga sunzo toh ke baki isa dakatar dasu ba.Allah ya albarkaci rayuwarku dake dasuma."
Kuka nake sosai, ina kallon yaran, nama rasa me zance dan nayi kuskure a rayuwata, nice Babba kuma nice na fara zubda mutuncin gidanmu, ribar taurin kai har da shegu. Dafe goshina naƴi sakamakon sara min da yake Ummi tayi maza ta riko babyn.
Kallon Ummi nayi ina girgiza kaina nace.
"Ummina! Ni bazan shayardasu ba, kawai a shayar dasu Madar."
Make min bakina taƴi cikin wani irin ɓacin rai, wanda ban taɓa sanin tana dashi ba, ta kuma ɗaga hannu zata mare ni, haka ta kasa marin, saukewa taƴi ranta yana tafasa, ta dire min jaririyar ta ɗauki hijab ɗinta tace.
"Nagode."
Tasa kai zata fita, Khalil yace.
"Ummi! Ke da kika haifemu kikayi fushi da alamarinmu ina kuma wani na daban, Ummi idan kikayi fushi da ita bazata ga daidai ba, don Allah kiyi hakuri Didi bazata kuma ba."


Kallona yaƴi cikin jin haushi amma yayi kokarin haka yace.
"Didi baki kyauta ba ɗauketa ki bata abincinta ba a shayarwa ke aka shayardake,"


"Ibrahim sheg..."
"Ke kan wallahi baki da hankali." Inji Umma da tashigo ganin Ummi a tsaye yasa tsayawa a gun, gashi taji abinda Khalil ya faɗa min, uwa Uba katoɓarar da naƴi. Hmm bakin ciki yasa Ummi barin asibitin, ba ita ɗaƴa ba hatta yan uwana, dan Alakatafur naki bawa yaran nono, har Abdul sai da yaji haushina. Maida yaran akayi ni kuwa na cigaba da kuka na, Umma kaɗai aka bari. Muna zaune sai ga Dr Katagum ya shigo da yaran yana ɗauke da daya, nurse tana ɗauke da ɗaya..
Yana zuwa ya ja kujera ya zauna sannan yace min.
"Maza basu nono."
D'agowa nayi a tsiwa ce, muna haɗa ido naga ya cika min ido, dole na sunkuyar da kaina, na buɗe rigar na rasa ya zanyi da babyn, nurse yayiwa magana, sannan ya juya gun Umma da take min faɗa da harshen shuwa, tana gamawa, ta shiga masa godiya.
Nuna min yadda zan bawa babyn nono tayi, sannan ta ajiye min ɗayar, ta fita.
Babyn tana kama nono na lumshe idanu, sabida zafi.
Haka mukayita dambe da Babyn sannan ya amsheta ya sakata a kafaɗarsa, sannan yanuna min ɗayar.
Na ɗauka fita Umma tayi dan ana kiranta a wayarta bata ji.


Tana fita sai bumm muka ji kamar an wurgo shi ɗakin, ɗ'ago kaina nayi, bansan lokacin da yawu ya sarke min ba, tari na fara. Dr Katagum ya mike yazo ya amshi yarinyar ya kwantar da ita, sannan ya zuba min ruwa a kofi na zafi sannan ya ɗauki na goran faro ya zuba min, tare da mika min, da sauri na amsa.
Takowa Anim yayi yazo ya kalle yaran, cikin mugunta yace.
"Sannu uwar yan biyu, riba har da uwar kuɗi kenan."
Rike rigar Dr nayi ina girgiza kaina, kallon Anim yayi ciki mamaki yadda yake murmushi.
Gashi yana kokari taɓa yaran, cikin kuka nace.
"Karka barshi ya taɓa min su!"
Aikuwa ya rike hannunshi, tare da maidashi baya, dariya Anim yayi..
"Kice anan ma kin kuma samun aboƙin tayi, toh su yaran ubanansu nawane haka?"
Kuka ne ya ci karfina sosai.
"Wai Anim me yasa kake son cin mutuncina ne, laifin me na maka ne da zafi,me na tare maka a rayuwar duniya? Nayi danasanin saninka a rayuwata, kuma Ubangiji sai yayo min sakayya."

"Dalla rufa min baki, meye kika min, bayan kin lalata min nawa rayuwa, kika je kika kwaso wasu shegu a rayuwarmu."


"Yarana ba shegu bane, domin sa Ubansu sai dai kaine dai basu ba."
"Keee! Ni kika zaga?" cikin kwarin gwiwa nace.
"Eh ɗin na zageka."
Dukda ciwon dake harshena bai hanani kare mutuncina ba, kaina yayo zai dake ni, Dr Katagum ya dakatar dashi ta hanyar mai dashi baya.
"Dalla malam matsa min, dakai ba kaine aka yaudara ba, ka tmbayeta abinda ta min, da sadakina taje wank katon iska ya lalata min tanadina,"


Dafe goshina nayi hawaye na zuba wannan na ƙoran wanan. Dr yace.
"Shin wani irin tanadi aka lalata maka?"
"Bada mutuncinta na ace da tayi shine tanadina."


Murmushi Dr yayi sannan yace.
"Kenan dama ba ita kake so ba, Budurcinta ƙake hari, da zaka samu a waje bazaka taɓa damuwa da taje gidanka ba, ko kuma kana aurenta kaji yadda take ana kwana biyu zaka saketa ko?"
*Wacce amsa Anim zai bada???*


Oum Muwaddah......👏👏👏
[2/5, 7:51 PM] +237 6 72 92 59 08: _HAZAƘA WRITER'S ASSO_


*_MASARAUTAR JORDAN!!!_*
_Jordan Historical_
*©2020*
*BOOK ONE*



*_Labarin daban yake da sauran._*





Page.٣٠-30


Wuri-wuri Anim yayi da idanunshi zuciyarshi tana wani irin buga, kankance idanunshi yayi ranshi na kara ɓaci. A fusace yace.
"Kai waye? Da zaka sani a gaba da tambayoyi! Ita ɗin dadironkace, ko abar kaunarka ce? Gata nan da cikin jikinta na shayar da ita madaran jikina ko karya ce na miki? Da kanta tazo gurina muka tsallaka tsakiyar taku da ita har na wata gud.."


"Azzalumin macuci Allah sai ya gwada maka iyakarka, wallahi babu abinda ya taɓa haɗani da shi, Wallahi ni ba fajira bace" na faɗa cikin kuka,
"Toh cikin da kika haifa taya kika same su?"
Dafe goshina nayi dan tsakanin da Allah Anim yake son lalata min farin cikina, a yanzun da nake kokarin tattara d'an kuzarin da na rasa shine bari ya lalata min su, ban tsammaci jin magana me kyau daga bakin Dr ba sai da ya doki dodon kunnena.
"Malam! Idan na fahimta kana yin haka ne dan taki amincewa da kai ? Ni a tunani na idan kana son mace kuma ka ganta a gidan karuwai, babu abinda ya dameka ɗaukota zakayi ka aureta, sai gashi kaddara da rabo sunsa kana cutar da zuciyarta da ruhinta, kuma kana kiran haka da *SO* bayan babu wani masoyin gaskiyan da zai so cutar da abokiyar soyayyarsa, zan faɗa maka wani abu guda ba a haka zaka nuna soyayyarka ba, dan kana kusantata da ɓacin rai yana rage kima a idanunta."


Tsaki yayi zai magana, sai gashi ya fita. A zafaffe Dr ya juya gareni tare da tsare ni da mayun idanunshi masu, matukar karfi da haiba.
"Taya kika same su? Iya gaskiyar da kika faɗa shi zai bani damar dakatar dashi."


D'ago kaina nayi na zuba masa ido, a sannu nayi kasa da kaina. Sannan na fara basu labari dan bashi kaɗai bane a ɗakin har da Umma da kuma Abbanmu wanda ya kira Abdul ya kawo shi.
Da nazo inda kaddaran cikin yaran kasa faɗa musu kome nayi, kuka na sake me taɓa zuciya da ruhin me sauraranshi, sai da nayi ya ishe ni sannan na ɗago kaina na cigaba da cewa.
"Sam baya cikin hankalinshi, dan sun masa sihiri da ya samu taɓen hankali, nasan waye Ashraf dan na zauna dashi kafin faruwa alamarin bai taba kallona cikakke na sec, balle na mint. Mutum ne da ya kame kanshi daga masha'a da ace zai min haka da tuntuni yayi min, amma haka ya tsare kanshi har na shiga rayuwarshi."
Ɗago kaina nayi na kalle Abba, tare da girgiza kaina nace.
"Abbana! Nasan dalilinka na korata dan zan zubar maka da kimarka, wallahi ko da wasa ban taba barin wani ya taɓa kimarka ba, da sona ne yaran nan bazasu kasance a raye ba, amma sun zame min kaddara wanda bazan iƴa kankaresu ba, don Allah ka kira Nannah ta ɗaukesu zan zauna da kai kuma zan maka biyayya."
Kura min ido yayi cikin zubda hawaye yace.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login