Showing 78001 words to 81000 words out of 82682 words

Chapter 27 - MATAR DOCTOR COMPLT BY ESHAAT.txt

ESHAAT   

18 Jan 2025

4342

amma ina da wayau sosai, tun lokacin na lura mun dena zuwa masallaci se Church, kafin a cire ni a islamiya Malamin mu yana mana waazi tare nuna mana addinin Musulunci shine addinin gaskiya sannan babu inda yafi dacewa ayi ibada se masallaci, wannan dalilin yasa bana bin su Momma Church!




A haka har na gama karatuna na samu aiki a Kaduna, anan na hadu da Janan, ita ta fara nuna min tare da koya min sannin darajan Mutum, dabi'un ta da yanayin rayuwar ta yasa na fara kwadayin nima in kama addini guda daya, lokacin da muka je Seminar da aka bude Babban asibiti a Makarfi, a nan na hadu da Baba Liman, muna da wajen kwana amma yace me ze hana in sauka a gidan shi!
Tunda na zauna a gidan suke girmama ni da darajta ni, so da dama idan yana ma mutane karatu tare da fada musu hukunce hukunce a Musulunci na kan saurara, na lura akwai rikon addini a gidan Baba Liman kuma ba sa nuna kyama ga wanda ba Musulmi ba!


A haka na fara tuno maganganun Janan, ji nayi ina son nima in koma Musulunci!
Ana saura kwanaki 2 mu gama Seminar din mu naje na samu Baba Liman na fada mishi ina so in koma Musulunci, yayi farin ciki da jin haka! Ni nace a maida min sunan na farko wato SHUREIM!!


Tunda na shiga Musulunci nake karo da abubuwan alkhairi tare da cin nasara a duk abunda nasa agaba, kuma a lokacin ne nayiwa Yar Mataimakin Gwamna Plastic Surgery!


Ko san da na bar aiki na dawo gida naga su Momma still suna cikin addinin dana barsu ciki, nayi bakin ciki na so in fada musu na canza addini amma na san hankalin su ze tashi shiyasa ban sanar da su ba se dai na cigaba da musu addua'a Allah ya ganar dasu gaskiya !!!


Maganar shi ta kashe musu jiki sosai! Janan murna da farin ciki take yi sosai tare da godia ga Allah!


Zarah ita ma ta basu labarin komai da yanda ta Musulunta!




Dad yace "a yau zamu bar wannan addinin 'bata, kuma duk abunda na samu a cikin addinin zan barsu domin in yi kyakyawan tuba! Kuma ina rokon Allah ya yafe min duk zunubai na, Lallai munyi babban asara! Ya karasa maganan cikin kuka!


Dad da Momma kuka suke yi kamar za su shide, kowa na wajen jikin shi ya mutu ga tausayin su Dad na halin da suka shiga!


Baba Liman yayi gyran murya sannan ya fara da fadin "Yabo da godiya sun tabbata ga Allah, abubuwa sun faru wanda dama kaddara ce kuma yana nan a rubuce a cikin littafin kowannen mu, bamu isa mu canza abunda Allah ya tsara ba! Saboda haka mu gode mishi da har yasa baku mutu a cikin wannan addinin ba!


Nan suka karbi kalman shahada!
Kabbara kawai ke tashi a parlor'n! Se da suka ci abinci suka koshi sannan suka tafi cike da farin ciki mara misaltuwa!


Suna komawa gida suka yi wankan shiga addinin Musulunci! Se a lokacin suka samu natsuwa da kwaniyar hankalin da suka rasa na shekaru masu yawa!







Dr. Shureim sun kara fahimtan juna shi da Janan din shi, ga wani zumunci me karfi daya kara shiga tsakanin gidaje biyun!


Ya tambaye ta dalilin da yasa aka fasa auren ta da Imran! Bata boye ba ta fada mishi komai!


Wani irin soyayya ta ban mamaki ya kara shiga tsakanin su, magana tayi karfi dan har iyayen su sun san komai!




A haka hutun su ya kare suka koma sch inda a yanzu suke 300 lvl! Sosai Dr. Na kula da ita dan duk karshen sati se ya je sch din su ziyara!




*******


Tunda suke hanya za su dawo daki daga lectures Zarah take waya har se da suka shiga daki sannan ta ajiye wayan, Janan tace "Sis wai ke dawa kike waya tun dazu ne?


Zarah tace "Ni da Bro Saleem ne mana!


Janan tace "uhum! Ni fa ban gane tsakanin ku da Yaya Saleem ba, naga kuna wani mannewa ne kaman chewing gum!


"Bestie sa ido fa ba kyau! Me kike tunani toh!


"A! Ni ba ruwa na, nawa ido ne! In tayi wari ma ji!
Suka yi daria!




Duk wani abu da Dad yasan ta hanyan haram ya same su ya fitar ya maida musu Church harda takardun gidajen daya siya tare da tabbatar mu su ya bar addinin su ya koma Musulunci!


Sun yi bakin ciki tare da cewa za su bashi ninkin kudin da ya dawo da shi!


Dad yace "ni yanzu ba wannan bane a Gaba na, ina so in gyara kurakuran da nayi kuma in ma addini na hidima! Ya fice daga cocin!

Gidan su Ummiey ya je ya samu Momma, nan yake fada musu yanda suka yi, bayan Ummiey ta tashi yace ma Momma "Yanzu ina kike ganin zamu koma? Ba ni da komai daga mu se rigunan jikin mu!


Kusa dashi ta koma tare da kamo hannun shi tace "kada ka damu, Allah zai ba mu yanda za muyi!


Can yamma Dr. Shureim ya shigo gidan su Ummiey, bayan sun gaisa yace "Ummiey, Momma, Abbiey da Dad, ina so in roki alfarma a wajen ku, zamu je wani waje ne Gaba dayan mu!


Basu musa ba suka shiraya, a motan shi suka fita!


Kofan wani hadadden gida suka tsaya, gaba dayan suka fito yace su shiga! Komai yaji a gidan dan an tsara shi seda suka gama duba ko ina suka dawo parlor suka zauna!


Gaban su Momma da Dad yaje ya durkusa tare da ruko hannun su! Makulli ya sa musu a cikin hannun tare da fadin "wannan shine gidan ku, ina fatan zaku so shi kuma yayi muku!
A tare suka rungume shi suna sa mishi albarka!
Dadi ya dinga ji saboda ya faranta musu rai! Nan su Ummiey suka mishi godia!







Haduwa akayi bayan dogon nazari da lura aka sa auren Janan da Shureim, Saleem da Zarah, Khaleel da Hameeda sister'n Imran! Shi kuma Imran aka hada zumunci da Zee inda se da akayi da gaske ta yarda wai kar Janan tayi tunani zata ci amanarta!





Anyi hidima sosai tare da komai cikin tsari, duk da suna da kudi hakan be sa sun yi almubazzaranci ba!


Daurin auren su ya tara jama'a masu yawa inda aka daura auren Janan da Shureim, Saleem da Zarah akan sadaki mafi karanci dan auren yayi albarka! Angwaye sun sha akon cikin manyan fararen kaya!


Ana gama daurawa aka tafi Kaduna aka daura na Khaleel da Hameeda! Shi kuma Imran da Zainab!


Walima, Kamu da Dinner kadai akayi! Amare suka tare a gidajen su!!!












_RukkyBae_😏😏😏
[1/11, 10:50 AM] RukkyBae😏😏😏❣❣: [1/8, 10:29 AM] RukkyBae😏😏😏❣❣: ♥❤❤🖤♣♠♥♣♣♥♥♠♣♥♠♥♣♠♥♣♠♣♥♥♣♣♠♥♥♥♣♣♠♣♥♣♠♥♣♠♥♣ *MATAR DOCTOR* ♠♣♣♠♣♣♣♣♠♣♥♥♣♥♣♠♥♣♠♣♥♥♣♠








_RukkyBae_😏😏😏








🌐 *HAJOW* 🌐
✍🏻✍🏻 *_Hakuri Da Juriya Online Writers_* ✍🏻✍🏻✍🏻








_Alhamdulillah!_

_Alhamdulillah!!_
🖤
_Alhamdulillah!!!_







♥ *_LAST PAGE_* 🖤








1⃣2⃣0⃣










Da sallama Dr. Shureim ya shigo dakin Amaryar sa, zaune ya tadda ita a kan gado an nade jikin ta da Lapaya, a hankali ya karasa tare da ajiye ledojin hannun shi!
Gadon ya hau tare da bude mata fuska! Ido ta runtse sbd kunyar da take ji! Murmushi yayi yana fadin "Alhamdulillah! Nagode da Allah ya nuna min wannan rana wacce ba zan taba mantawa da ita ba, yau babban buri na ya cika, ina rokon Allah ya bani ikon kula dake tare da kare miki dukkan hakkin ki dake kaina, sannan ina neman alfarmar ki da kiyi hakuri da duk wani laifi da zan miki cikin sani ko akasin haka domin shi Dan Adam ajizi ne! Allah ya bamu hakurin zama da juna cikin so, kauna, rikon amana, gaskiya da kuma juriya!


Tun da ya fara maganan bata ce komai ba kuma bata dago ta kalle shi, ji tayi wani irin son mijin ta na ratsa dukkan sassan jikin ta ga kuma girman shi da a yau taji ya kara nunkuwa a zuciyar ta!


Ganin bata yi magana ba yasa shi tashi tare da cire malum_malum din shi sannan ya mika mata hannu alaman tazo! Cike da jin kunya ta rarrafo a hankali sannan ta mika mishi hannu, mikar da ita tsaye yayi sannan ya riko ta ta gefe suka wuce toilet! Alwala suka yi sannan suka fito! Da sauri Janan ta nufi akwatunan ta dake gefe ta ciro darduma guda 2 se dagon Hijjab da socks! Daya ta shimfida mishi sannan itama ta shimfida nata a baya, seda ya jira ta saka socks din sannan ya tada sallan!


A nutse tare da kaskantar da kai yake jan su sallan! Rakao'i biyu suka yi sannan ya sallame! Juyowa yayi yana kallon ta dai dai ta dago ido ya sakar mata murmushi, itama murmushin tayi, har gaban ta ya matsa sannan ya mika hannu ya daura a saman kanta, adduo'i ya dinga jerowa sannan yayi mata tambayoyi akan addinin ta, duk da ya san tana da ilimin amma yana so ya kara tunatar da ita, bayan ta amsa mishi ya umurce ta itama ta tambaye shi!


Tayi mamakin yanda ya dinga bata amsa ba tare da kuskure ba! Shi da kanshi ya dakko plate da cups ya zuba musu Holandia da gasasshiyar kaza! Da kyar ta iya ci sbd kunya danma shi ya dinga bata har suka koshi, tare suka nufa kitchen ta wanke kayan shi kuma ya dauraye ya maida su in da suka sannan suka koma daki, toilet suka shiga suka yi brush!. Gado suka hau tare da yin addua'a! Sun bautawa Allah tare da raya sunan Manzo Allah SAW a daren!




Haka zaman su ya dinga tafiya cike da so da kaunan juna gashi dama Dr. An bashi hutun, babu inda yake zuwa suna tare kullum se dai in ya tafi masallaci sallah!
Tare suke wanka, gyaran daki, shara, wanke_wanke da girki, komai tare suke yi hatta wanki da guga su suke yi da kan su!


Yau ta kama Weekend, bayan Dr. Shureim ya dawo daga sallan azahar suka shiraya suka nufi gidan su Momma, a nan suka tadda Abbiey da Ummiey, Janan taji dadi sosai dan tun bayan bikin su bata kara ganin su ba se dai suyi waya! Dr. Shureim ya duka har kasa ya gaida su sannan ya gaida su Momma!


Momma da kanta ta tashi ta debo musu dambun nama da juice, su na ta hiran su, Janan da Dr. Shureim kuwa suna ta faman kallon juna suna murmushi, ana haka Zarah da Yaya Saleem suka shigo!
Wani irin ihu Zarah tayi tare da fadowa kan Janan se gasu sun zube a kasa Dr. Shureim yace "ke miye haka? Kada ki karya ta mana! Ya tashi daga inda yake ya dago Janan yana fadin sorry Darling" gaba daya ya manta da su Ummiey a wajen ita ko Janan tayi kasa kasa da murya tace "ga fa su Momma a zauna kar suce ba muda kunya"
Kai ya dan sosa sannan ya mika hannu suka gaisa da Yaya Saleem!


Gefe Zarah taja Janan suka dinga hiran su, Mai Gadi yayi sallama daga waje, suka amsa Dr. Shureim ya tashi yaje yace "Ya dai?


Ina wuni Likita bokan turai? Be jira ya amsa ba ya cigaba da fadin, wasu Mutane ne su biyu suka zo wai suna neman Alhaji, dayan ma a keken guragu aka turo shi, shine suka ce in musu iso''


Kace su shigo! Watakila suna neman taimako ne!


(Tun bayan abunda ya faru da Dad yayi alkawarin taimaka wa duk wanda ba shida karfi! Gaba daya Dr. Shureim ya dauke nauyi su kuma duk wata yana turo musu kudi)


Dr. Shureim ya koma ciki ya fadawa Dad, sannan ya zauna!


Sallama aka yi tare da daga labulen! Zunbur Dad ya mike yana kallon su haka ma Momma, a hankali aka dinga turo wheel chair din har gaban Dad sannan suka tsaya!
Kallon su kawai Dad yake yi amma ya kasa magana dan ya rasa abunda ze ce be gane na tsayen ba amma ya gane na kan kujeran guragun!
Momma tayi karfin halin fadin "Yaya Hamza? Kaine? Kaine a haka? Kuka ya subuce mata ta koma ta zauna a kujera!
Dad da idon shi suka yi ja yace "me yasa ka neme ni? Me yasa ka tuno kana da wani dan Uwa a duniyar nan?


Yaya Hamza yace "Kayi hakuri Kanina, ka yafe min na san ban kyauta maka kuma ban yi maka adalci ba, na cutar da rayuwar ka, ni ne na turo yan fashi suka kwashe kudin ka sannan suka kona maka gida sbd ina so ka shiga wani hali.. Bayan na biya su an kwana biyu nima suka zo suka kwashe komai harda takardun gidaje na sannan suka min duka tare da karya min kafafu sanadin haka na zama gurgu! Kuka yaci karfin shi!
Salati kawai Dad yake yi sbd yanda jikin shi ke rawa... Duk wanda ke parlor'n se da ya dauke wuta sbd jin abunda Yaya Hamza ya fada! Momma, Ummiey, Janan da Zarah kuka kawai suke yi!
Dr. Shureim dake zaune ya tako har inda yake, da ganin shi yana cikin bacin rai da bakin ciki.. Dai dai setin kafafun shi ya durkusa yace "mun gode da abunda kayi mana kuma mun ji bayanin ka saboda haka ku tafi! Ya mike tsaye dan ya san in ya cigaba da magana ze iya fadan abunda be dace ba!
Kwata kwata Dad ya kasa magana se kallo kawai yake bin Yayan nashi da shi yana jin wani irin daci a zuciyar shi wai yau ace Dan Uwanka Uwa daya Uba daya ke maka wannan hassadar tare da son ganin bayan ka? Me ya tsare mishi? Daga ya karbi hakkin shi shikenan! Oh Duniya ina zaki damu ne?

Cikin dauriya da karfin hali ya bude baki yana fadin ''Lallai kaci amanan iyayen mu, ka ci amanar zumunci, ka cuce ni ka cuci kan ka, ka zama silan fadawa ta halaka ni da iyali na, saboda haka ni bani da dan Uwa illa wannan bawan Allahn da ka gani zaune ya nuna Abbiey, kuma ba zan taba yafe maka ba sannan daga karshe ina baka shawaran ka fice min daga gida kafin in sa a maka koran wulakanci kuma in kira yan sanda! Sannan baka ga komai ba ma in dai alhaki ne yanzu ya fara binka! Tari ya sarke shi a nan ya fadi kasa, gabaki daya suka yo kanshi, jijjiga shi Momma ta dinga yi amma kamar ba shida rai!
Da gudu Dr. Shureim ya nufi motan shi ya dakko kayan aiki, yana zuwa ya fara dudduba shi nan ya gano jinin shi ne ya hau sosai! Ruwan sanyi ya sa Zarah ta dakko a fridge ya dinga shafa mishi, can Dad yayi ajiyar zuciya alamar ya farfado kenan! Waigawa yayi ya ga Yayan shi yana nan be tafi ba, sake runtse ido yayi yana son yin magana! Ganin haka yasa Abbiey tashi yaje har gaban Yayan yace "kayi hakuri muje waje"
Jiki a sanyaye Yaron shi ya ja keken suka fita Abbiey na bin su a baya! A tsakar gidan suka tsaya Abbiey ya karaso yace "kayi hakuri da duk abunda ka gani, ka san dole abun ze mishi ciwo kuma ba zai iya furta ya yafe maka ba a cikin halin da yake ciki ba! Tas Abbiey ya kwashe duk abunda ya faru dasu Dad ya fadawa Yaya Hamza!
Hankalin Yaya Hamza ya tashi sosai da sosai, wani irin nadama da dana sani suka saukar mishi! Wasu hawaye masu zafin gaske suke ta zubo mishi, Lallai ya san cewa yayi babban kuskuren da baya fatan sake maimaitawa! Jiki a sanyaye suka bar gidan!
Gaba daya abunda ya faru ya dagula wa Dad lissafi, ya kasa mantawa, a haka Abbiey ya dinga mishi Nasiha yana fada mishi ladan da zai samu idan ya yafe ma Dan Uwan shi!
Se da akayi sati sannan Dad ya hakura, tare da Abbiey suka je gidan da Yaya Hamza ke haya wanda gidan kamar na almajirai saboda lalacewa!
Nan Dad ya tabbatar mishi da ya yafe mishi, suka rungume juna! Suna kukan farin ciki! Washe gari ya sama mishi gida yace su dawo shida yaran shi, ya jibge musu kayan abinci, harda masu aiki guda biyu!


In an samu hutu dukkan su suke tafiya Kano wajen Dangin Momma haka ma suna zuwa Sokoto wajen abokan arziki! Sosai Dad yake musu alkhairi!




Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, duk bayan sati 2 sukan je gidan su Momma ko gidan su Ummiey! Hakanan suna zuwa gidan su Zarah ko kuma su su zo! Har gidan su Yaya Khaleel suna zuwa!
Akwai randa suka shirya suka je gidan su Imran, sun ko ci saa yana gida, sosai yayi farin ciki da zuwan su! dr. Shureim da Dr. Imran suna ta hira ita kuma Zee da Janan suka shige daki suna nasu hiran! Se da yamma suka tafi cike da jin dadi!


Tunda Da Dr. Shureim ya koma wajen aiki Janan ta zama tamkar marainiya, duk da idan ya samu sararin aiki suna waya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login