Showing 75001 words to 78000 words out of 82682 words

Chapter 26 - MATAR DOCTOR COMPLT BY ESHAAT.txt

ESHAAT   

18 Jan 2025

4335

ta me kamshi, Darduma ta shimfida ta dakko dogon Hijjab da socks ta saka sannan ta tayar da sallah tana me farin ciki, zuciyar ta cike da nishadi!
Tana raka'an karshe taji alaman an shigo dakin dan yau bata kulle ba tunda su Momma basa gida, gaban ta ne ya dinga faduwa amma haka ta kara maida hankali kan sallan ta, tana idarwa ta waiga dan taga waye! Dr. Godwin ta gani tsaye ya harde hannuwan shi a kirji yana kallon ta, ido ta zaro waje tare da dafe kirjin ta, bakin ta na rawa tana shirin mishi magana suka jiyo muryan su Momma alaman sun dawo, da sauri ta cire Hijjab din tare da tura shi cikin drawer tana waigowa taga Momma a tsaye a kofan dakin tana musu kallo me nuna alaman lafiya?
Da kafa Annabelle (Zarah) ta dinga jan darduman har seda ta tura karkashin gado! Wayancewa tayi da fadin "Momma sannun ku da zuwa ina Dad?
A haka ta samu ta janye ta zuwa parlor Dr. Godwin na biye da su!


Abincin rana suke ci amma duk ta tsargu dan data dago za su hada ido da Dr. Godwin, gani take yi kamar ze fadawa su Momma! Ya gane abun da take nufi dan haka suna sake hada ido yayi mata murmushi tare da girgiza kai! Se a sannan hankalin ta yadan kwanta!
Suna gamawa suka dan taba hira, nan ta kara musu tuni akan zuwa gidan su Janan!! Dr. Godwin yaji yau yana son ganin kawar Lil Sis din shi dan haka ya dau aniyar bin su!


Se da aka yi sallan Isha'i sannan suka shiraya tafiya, Godwin wasu carton brown half kaftan ya saka, yayi kyau sosai, Zarah tayi mamakin jin Yayan ta ze bisu!


A tare suka fito, motar shi yace suyi anfanin da ita, Momma da Zarah suka shiga baya, Dad ya zauna a gaba, Dr. Godwin ya ja motan suka tafi!!!


Kwatance Zarah ta dinga yi mishi har suka kai bakin kofan gidan, parking suka yi tare da gaisawa da Mai gadi, yana ganin Annabelle (Zarah) ya gane ta da sauri yace su shigo, kin shiga suka yi Dad yace "Princess je ki fadawa mutanen gidan tare muke dan kar mu shigan musu gida ba tare da izinin su ba"


Tace ''OK Dad" sannan tayi shigewar ta!


A parlor ta tarar dasu Ummiey da wasu dattijai 2 amma Janan bata parlor'n, har kasa ta duka ta gaida su tare da fada musu dasu Dad suke, Nan Abbiey yace "aa, ya suka tsaya a waje? Je ki shigo da su! Da sauri ta fita tace musu su shigo!
Gaban Dr. Godwin se faduwa yake amma ya rasa dalilin hakan!


A tare suka shiga parlor'n, dai dai Janan ta fito daga dakin ta!


Wani irin abune ya gilma musu kamar walkiya, Dr. Godwin yace *JANAN!!* tare da nuna ta, Be gama Mamaki ba yaji ance *SHRUIEM!!* yana juyawa yaga daya daga cikin dattijan ke mishi magana, Dr. Godwin yace *BABA LIMAN!!*


Abbiey ya kalli Dad tare da fadin *MR. AHMAD!!*


Dad yace *BARRISTER PHAROUK MAKARFI!!*


Ummiey ta kalli MOMMA tace *HAJIA HALEEMAH!!!*


Momma kuma tace *HAJIA NANA!!*












_RukkyBae_😏😏😏
[12/31/2017, 12:17 AM] RukkyBae😏😏😏❣❣: [12/28, 8:54 PM] RukkyBae😏😏😏❣❣: ❤🖤♣♥♠♣♥♣♠♣♥♣♣♥♣♠♥♥♣♠♥♥♣♠♣♥♥♣♥♥♠♥♥♣♥ *MATAR DOCTOR* ❤♠♣❤♥♠🖤♣♥❤♣❤♥♣🖤❤♣🖤♠🖤❤♣♥🖤♠♥🖤♣♠🖤♣♥♥♣♠♥










_RukkyBae_😏😏😏






🌐 *HAJOW*🌐
✍🏻✍🏻 *_Hakuri Da Juriya Online Writers_*✍🏻✍🏻






_Wannan Shafin naku ne gabaki dayan ku Makaranta kuma Masoya littafin MATAR DOCTOR!! Ina godia da kulawar ku da soyayyar ku a gare ni!! Ina gaishe ku tare da muku fatan alkhairi a duk in da kuke!! Allah ya kara mana son juna!!...._









1⃣1⃣8⃣








Gaba dayan su sun zama confused se kallon kallo suke yi a tsakanin su! Abbiey ne yayi karfin halin samun kujera ya zauna, su Momma suma suka zauna, Dr. Godwin da Janan kuma suna tsaye kamar an dasa su!!


Shiru ya ratsa dakin se T.V kadai ke aiki, fuskan Dad aka nuno a alon TV yana preaching a Church! Tambaya da mamaki ne a fuskan Abbiey, Ummiey da Baba Liman! Se yanzu suka lura Momma ko Dankwali babu akan ta!


Abbiey yace "Mr&Mrs Ahmad??


Dad ya gane Abbiey na neman karin bayani ne!


Shiru ya dan yi se ga hawaye suna fita daga idon shi, ganin haka yasa su Janan suka zauna dan abun da mamaki Babban Mutum kamar Dad yana zubda hawaye!


Dai dai lokacin Yaya Khaleel da Yaya Saleem suka shigo!
Abbiey ya musu nuni da su zauna!


Godwin, Annabelle yau zaku san abunda baku sani ba, gara kai Godwin zaka iya tuno wasu abubuwan!! Dad yace



*TUSHEN LABARI!!*




Asalin su Dad yan garin Sokoto ne, sunan Mahaifin su Malam Shureim, su biyu kadai iyayen su suka haifa Dad (Ahmad) da Yayan shi Hamza! Sun yi karatun primary da secondary duk a nan Sokoto, mahaifin su ya rasu da shekara daya da rabi Mahaifiyar su itama ta rasu, sun yi kuka har suka dangana, lokacin Dad yana Ss2, shi kuma Yayan shi ya fara zuwa Jami'ar Dan Fodio, yau dadi gobe ba dadi a haka Dad ya fara aikin kanikanci, da haka ya samu ya biya kudin WAEC da NECO harda Jamb, cikin sa'a ya samu ya ci komai inda ya tafi Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria ya karanta Geography, kwata kwata Yayan shi be cika damuwa da shi ba, da kyar da wahala ya samu yake karatun nan, ana haka kudin Baban su na Pension ya fito
Da yake lokacin kudi na da daraja se suka dan samu da tsoka, ya kira Dad ya fada mishi kudin Baban su ya fito, yaji dadi dan ya san ko ba komai ze huta da wahala, ba abunda ya sauya daga rashin kulan da Yayan shi ke mishi, haka ya samu ya kammala karatun shi cike da nasara, a lokacin Yayan shi ya yi aure suka zauna a gidan su da Baban ya bar musu, tun lokacin Dad yace a raba gado aba kowa nashi sbd yana so ya fara kasuwan ci amma Yayan shi ya ki yarda, babu yanda Dad ya iya haka ya kyale shi, wani dan mokocin su dake zuwa Lagos saro kaya ya fara bi suna siyo kayan tare ana bashi lada...


Kudin ya dinga tarawa har shima ya fara saida takalma, cikin hukuncin Allah ya hadu da Haleema (Momma) lokacin yaje Kano saro takalma, sun shaku da juna har suka yi aure, bayan da kyar Yayan shi ya yarda!


Tun bayan auren su da Momma yake samun budi amma basu samu haihuwa ba, cinikin takalma ya habbaka da haka ya koma Lagos, ganin yana ciniki kuma Alhamdulillah yana da rufin asiri yasa shi be nema aiki ba, lokacin daya zo Sokoto dan duba Yayan shi se yake ce mishi "Ahmad yanzu baka son zuwa garin nan kuma ka san bani da kowa se kai amma ka kyale ni a nan, me yasa nima ba zaka samamin wuri a can ba in dawo kusa da kai!


Ba haka Dad yaso ba amma daya fadawa Momma ta dinga murna tace ai ba komai gara su zauna kusa da shi!


Bayan ya dawo ya neman mishi wani gida ba nisa tsakanin su, tunda ya dawo Dad ke dawainiya dashi!


Wani abokin kasuwancin shi yace "Malam Ahmad me yasa ba zaka sa kudin a hannun jari ba? Ana samun riba sosai da sosai fa!


Maganan abokin kasuwan cin shi ya tsaya mishi a rai dan haka ya fada wa Momma komai ita kuma ta bashi shawara ya fada wa Yayan shi Hamza!


Bayan ya fada mishi komai da irin riban da zasu samu se yace "toh ai wannan cigaba ne a gare mu baki daya ka bari kudin gadon mu se in sa mana a ciki ko ya ka gani?


Ba tare da wani tunani ba ya yarda da shawaran Yayan nashi!


Duk wani shige da ficen kudin ta hannun Yaya Hamza yake fita, a haka har abun ya bunkasa ya gina haddaden gida!


Duk Dad be ce komai sbd hakuri da kawaici, a haka kasuwancin shi ya fara kasa ga Momma da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe, duk ya fita hayyacin shi tun yana daurewa har ya fara sarewa, wajen Yayan shi yaje akan ya bashi rance a kudin su amma ya rufe ido yayi mishi kacakaca! Jiki a sanyaye ya dawo gida, Momma ta lura mijin ta baya cikin kwanciyar hankali ga nakuda ta fara, a haka ta dinga kokarin kwantar mishi da hankali! Washe gari yana shirin tafiya kasuwa yaga tana cije cije, tambayan ta yayi ko lfya amma tace ba komai, haka ya shirya ya fita ko nisa be yiba faya ta fashe, mantuwa yayi dan haka da sauri ya dawo gida, yana shigowa ya ganta a wannan halin ga wani ruwa dake bin kafafun ta, cikin hanzari ya fita ya nemo me taxi ya kwashe ta se asibiti! Labor room aka wuce da ita, bada dadewa Nurse ta fito tana tambayan kayan haihuwa dan ta kusa sauka, shi gaba daya ma ya rude ya manta da wani abu wai kayan haihuwa dan haka da sauri ya koma ya kwaso dan tun cikin be yi kwari ba yake siyo kayan haihuwa!


Bayan mintuna 30 aka mishi albishir da ta haifi dan ta namiji! Yayi farin ciki sosai, da Baby da Maman duk suna cikin koshin lfya! Kwanaki 2 bayan haka aka sallame su, nan ya sa ma yaro sunan Baban shi marigayi (Shureim) suna kiran shi da Baba!


Haihuwan Baba ya sa sun samu alkhairi dayawa daga wajen mutane ta fanni daban daban! A haka suka cigaba da manajin rayuwa har Baba ya fara zuwa makaranta, kuma Momma bata kara haihuwa ba!!
Ganin alamura sun kara kasa yasa Dad komawa wajen Yayan shi kan kudin gadon shi, wannan karan ma rashin mutunci ya sake mishi dan haka Dad yace "ba zan yarda ka danne min hakki na ba shekara da shekaru dan haka kotu ce zata raba mu! Fuu ya fita daga gidan, abunka da wanda be iya fushi ba, da barin gidan Yayan shi kotu ya tafi ya kai kara nan aka hada shi da Barrister Pharouk Makarfi (Abbiey)! Be boye mishi komai ba tun daga tasowan su har zuwa yanzu!


Daya koma gida ya ba Momma lbr bata ji dadin haka amma ta mishi fatan alkhairi!


Sammaci aka aikawa Yaya Hamza, abun yazo mishi a ba zata dan haka ya dinga bala'i daga karshe shima ya nemo lawyer!






Bayan zama da hujjoji masu yawa su Abbiey suka cinye shari'a kuma a take a kotu Alkali yasa aka raba kudin kowa aka bashi!


Dad yayi farin ciki tare da godia ga Allah, bayan barin su kotu ya ciro kudi masu yawa ya ba Abbiey amma yace shi ba zai karba, Dan Allah ya taimake shi!


Tun daga lokacin suka kulla alaka suka zama tamkar yan uwa!
Haka Momma (Haleema) da Ummiey (Nana Khadeeja) suka zama kawaye! Har hutu Shrueim na zuwa yi a gidan da yake sa'anni suke da Saleem!




Tamfatsetsen gida Dad ya gina suka koma ciki, ya hada walima dan godema Allah! Har gidan Yayan shi ya zo yace "kada ka kuskura ka nuna ni a matsayin dan uwanka kuma duk abunda ya same ka kada ka sake kazo inda nake, bani ba kai! Ya fice daga gidan!


Abun ya dade yana damun Dad tare da mamakin hali irin na Yayan shi!!




Hannun jari ya cigaba da zubawa kafin ya samu sana'an yi!




Ya dade yana tunanin abunda ze yi ya saka ma Abbiey amma ya rasa dan haka ya biya ma dukkan su kudin aikin Hajji, Ummiey da Abbiey sun yi farin ciki dan haka aka kai su Shrueim, Khaleel da Saleem Makarfi kafin su dawo!!











Bayan dawowan su da wata 3 aka ma Abbiey canjin wajen aiki! Harda su Dad suka je suka ga sabon gidan da su Abbiey suka koma! Lokaci zuwa Lokaci suna ziyartan junan su!






Bayan Shekaru 9 Momma ta samu ciki, sun yi murna sosai!
Dad ganin yayi karfi a cikin hannun jari yasa shi janyewa, gaba daya kudaden shi ya kwaso dan yana so ya fara business a Dubai, a daren ranan yan fashi suka duro gidan tare da kwashe duka kudin sannan suka cinnawa gidan wuta, Allah yayi da sauran rayuwa a tare da su Dad suka fito a guje, Shureim yana hannun Dad!


Wani kongo suka samu suka rakube dan basu san inda suka dosa ba! A haka suka kwana su tashi a cikin kongon nan, ba suda abinci se gari, haka Dad ze fita nemo musu abunda za su ci amma baya samu, Haka Shureim shima ze fita yana dako duk da kankancin shekarun shi!


Wani dare hadari ya hadu a take aka fara ruwa! A nan nakuda ya turnuke Momma duk inda suka je a taimaka musu babu wanda ke kallon su, a haka ya samu ya nemo me mota suka kaita asibiti (labarin baya da Dr. Godwin ya ba Janan a ranan birthday din su kan dalilin da yasa ya tsani kalman taimako)


Tana labour Dad ya fito haraban asibitin nan aka bashi lbrn an tafi da dan shi police station! Ya shiga rudu ya ma rasa ta ina ze fara, kongon da suke kwana ya koma ya hada kai da gwiwa yana kuka! Horn din mota ya dinga ji amma be damu daya dago ba, ji yayi an dafa shi da sauri ya dago fuska yana kallon su, wasu mutane ne guda 2 sanye da coat, daya yace "da gani kana cikin matsala, toh kada ka damu mu zamu taimake ke amma idan muka taimake ka zaka mana duk abunda muke so"


Cikin muryan kuka yace '' wani abu kuke so in muku?


"zamu fada maka amma yanzu kai ka fara fada mana damuwar ka mu nan masu taimako ne!


"gida na ya kone, matata tana asibiti tana nakuda, ba nida kudin da zan biya asibiti, 'Dana yana police station wajen en sanda, ta ina zaku fara taimaka min?


Kallon juna suka yi tare da murmushi, motar suka koma suka ce ya biyo su! Babu musu ya bi su! Wani gida me kyau suka kai shi tare da fadin "ga sabon gida nan mun baka, wani brief case suka miko mishi, wannan kudi ne ka je ka yi settling bills dinka na asibiti kuma ka yi bailing yaron ka, nan da sati daya zamu dawo kuma lokacin zamu fada maka abunda muke so"


Dad ya dinga godia yana kuka! A haka suka wuce suka barshi!


Se da yayi bailing Shureim sannan suka biya komai na asibiti tare da dawowa sabon gidan su! Momma tayi mamaki kan sauyin da suka samu dan haka ta dinga tambayan shi yanda aka yi, be boye mata komai ba ya fada mata! Ita dai jikin ta be yarda da mutanen ba amma haka tayi shiru!




Kamar yanda suka fada sati na zagayowa suka zo gidan! A parlor suka zauna bayan sun huta suka ce "Mr. Ahmad kamar yanda muka yi da kai yau zaka cika mana alkawarin mu!
Dad da Momma suka kalli juna! Dad yace "ina jin ku, ku fadi abunda kuke so!


'' So muke ka bar addinin ka ka koma addinin mu na Christian!!


Wani irin mikewa Dad da Momma suka yi lokaci guda suna fadin ''What!!


Suka ce "Calm down, ai deal muka hada dan haka babu ja da baya!


Zuciyar Dad na tafarfasa ya ce "ba zan taba barin addini na ba, duk abunda kuka bani zan dawo muku dashi nan da sati daya nima!


Murmushi suka yi sannan suka tashi tsaye " OK nan da sati daya idan muka dawo baka biya mu komai namu ba baka da wani option illa ka dawo addinin mu! Da haka suka bar gidan!


Momma tayi kuka kamar ranta ze fita, haka ma Dad ya shiga tashin hankalin da be taba shiga ba!


Duk inda ya san ze samu kudi yabi amma be samu ba gashi saura kwana 2 sati daya ta cika dan haka ya yanke shawara ya tafi garin da aka maida Abbiey dan tun kafin suyi gobara yaje shida su Momma! Yana zuwa yaji labarin an canza ma Abbiey wajen aiki kuma suma basu san inda ya koma ba!
Tun a hanya yake kuka da dana sani har ya iso gida!
Tunda ya fadawa Momma be samu su Abbiey take ta faman kuka! Kullum ba suda aiki se kuka! A haka har satin ya zagayo, mutanen suka dawo, su Dad ba suda mafita face suka koma addinin kiristanci! Inda Momma daga *Haleema* ta koma *Lidia*
Dad daga *Ahmad* ya koma *Williams*
*Shuruiem* ya koma *Godwin*
Ita kuma jaririya aka sa mata *Annabelle*!!




Sosai suke daukan dawainiyar mu ga kudi da ake sake mana, a haka har muka fara zuwa Church nan aka yanke shawaran a bani Babban Pastor a Cocin sbd kar ma in samu hanyar barin addinin!!!!.....


Dad ya karasa labarin yana gunjin kuka!!!


Kowa a dakin kuka yake sbd labarin akwai tausayi da daga hankali! Abbiey cikin kuka yace "nima nazo Lagos yafi so a kirga ina neman ka amma na kasa samun ka ashe abunda ya faru kenan" ya karasa maganan yana kuka!




Nan Dr.Godwin yace nima ina da labarin da zan bada!!!
















_RukkyBae_😏😏😏
[1/2, 10:06 PM] RukkyBae😏😏😏❣❣: [1/2, 5:57 PM] RukkyBae😏😏😏❣❣: ❤🖤♥♣♠♥♣♠♥♥♣♠♣♥♣♠♥♣♠♣♥♣♠♣♥♣♠♣♥♣♥♠♣♥♣ *MATAR DOCTOR* ♠♥🖤♣♥♥🖤♣♠♥♥♣♠♥🖤♥♥♥♥♣🖤🖤♥♠
















_RukkyBae_😏😏😏








🌐 *HAJOW*
✍🏻✍🏻 _Hakuri Da Juriya Online Writers_✍🏻✍🏻✍🏻








_Musulunci shine mika wuya ga Allah da kadai tashi tare da yi Mishi biyayya da bauta Mishi!_








1⃣1⃣9⃣










Dr.Godwin ya fara magana "tun lokacin da naji Dad ya canza min suna na tsani sunan, lokacin shekaru na ba suda yawa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login