Showing 18001 words to 21000 words out of 94974 words

Chapter 7 - ASHE ZAMUGA JUNA COMPLET BY MRS ISHAM.txt

28 Dec 2024

8659

aganina bayi da amfani su Abbie ko Abdulhameed su kaita tunda kinga duk suna da wajan zuwa ni zan kaita da kaina shisa nace babu amfani " jinta kawai sukayi , tsaki anty amarya ta yi ciki_ciki ta ce " bana bukata ko ni zan kai ƴata makaranta base kin kaita ba " ta yi maganar tana gyara dankwalin kanta sannan tabar part din fuuuuu kamar zata tashi sama.
kunya ne sosai yarufe Hajiya hurairah saboda yanda anty amarya ta sace mata guiwa murmushi ta yi ta ce" Allah sarki Abida kamar ranta yabaci , bari zanje in bata hakuri " kallon juna Ammi da Hajiya babba sukayi suka tabe baki , Ammi ta ce" karki damu ba se kinje ba zan mata magana " haka ta mike ta basu guri.
" Allah yakyauta to" cewar Hajiya babba Ammi ta ce" ameen ameen".






5:00pm na yamma dukkansu amma fa babu Tajuddeen aciki , sun hallara a spot area Babban wajen dake cikin gidan wanda yafi girman part biyu ko uku , duk wasu kayan nau'in game babu wanda babu awajen ko ina da shi harda bangaren gym , su Jawan suna buga ball , manyan cikinsu su Abbas kuma basa ma gida sunje gidan ya'yunsu da yau wata biyu kenan da yin aurensu Sakeena da Sameera sun kai musu ziyara gidan Sakeena suka fara zuwa daga nan suka wuce gidan Sameera.
Umaisha, Asrah, Rameesa,Parsa,Zoya, Iklas boji_boji sukeyi se dariya da tsalle_tsalle sukeyi cike da farin ciki , Rameesa da idonta ke adaure da ƙyelle tanata lalubawa acikin filin ko zata gansu amma ta ka sa kama ko mutum daya dakyar tasamu ta cafke Asrah, Parsa ce ta kulle mata idanunta su kuma suka boye haka suka ta wasansu har kusan mangrib suka koma ciki saboda suyi sallah .




DAMATURU




malam Mamman ne ya shigo gidanshi bakinshi a washe kamar ba shi ba hannunsa na rike da ledoji niƙi_niƙi ,abakin murhu yasamu Maryam tana durƙushe se hura wuta takeyi tun dazun amma yaƙi kamawa batamasan ya shigo ba , gyaran murya ya yi ,agigice ta juyo ta kalleshi. mamakine ya bayyana ƙarara akan fuskarta da ya haɗa zufa ga idonta ya yi ja saboda hayakin murhun da take kunnawa. sakaka Maryam ta yi da baki tana kallon fuskar malam Mamman da har izuwa lokacin bakin shi yaƙi rufuwa se murmushi yake . Mikewa tsaye ta yi ta gyara kodedden zaninta da take daure dashi miko mata ledar ya yi yana faɗin" Maryam matar Mamman kinsan yanda nake sonki kawai de saboda wannan yarinyar ce yasa nake jin haushinki amma yanzu dukkan ku inasonku sosai wallahi" ita de ta kasa janye idonta akanshi tsaban ruwan mamakin da yabata domin duk abinda yake faɗa ita de bawai ta gasgata bane .
lura da ya yi taƙi sakin jiki dashi ne yasa ya ajiye ledojin hannunshi,yaje can bakin dakinshi ya dauko tabarma yazo ya shimfida , ya jawo hannunta ya zaunar da ita ,buɗe manyan ledojin ya yi yafito da dangwala_dangwalan kaji da suka sha ga'shi se maiƙo sukeyi ga yajin kajin daure agefe , kamshim namar kazar ne ya da ki hancin Maryam, hadiye wani yawu ta yi da se da maƙoshinta ya ce "kwatt" , nan take yawunta ya tsinke. Maryam baiwar Allah rabonta da taga irin wannan tun lokacin da suke shan soyayya da malam Mamman kafin ta haifi Asmita.
Duk da yanda ranta yabiya da namar kazar amma taƙi saka hannunta aciki , malam Mamman ya ce" Maryamata kici mana saboda ke da yarmu Asmita na siyo wa'yannan kayan daɗin amma kin ƙi ci.
Sa ke kallon shi ta yi murya asanyaye ta ce " dagaske Malam ka karbi Asmita amatsayin yarka ?" Jiki na rawa ya ce " kwarai ma kuwa nakarbeta kuma nagane kuskurena! Tunda na dawo ma banganta ba ina take " ya yi magana yana kalle_kalle agidan kwala kiranta ya yi" yar baba Asmita kizoki "


Fitowa Asmita ta yi tana rakube_rakube saboda tsananin tsoronshi da takeji mikewa ya yi ya daukota ya zaunar da ita akan tabarman.
Daga Maryam har Asmita jin lamarin sukayi bankwarakwai , cinyar kaza ya dauka ya bawa Asmita " maza ci yata , ci nama" da sauri Asmita ta karba tafara ci ,haka suka za ge suka ci kaji dakuma su kayan kwalba da malam Mamman yakawo ranar de sunci dadi sosai, da dare ma yasake kawo musu kayan daɗin suka ci suka kwanta , Maryam tana ta murna mijinta yadawo kan hanya.






Kamar yanda na faɗa de yawan comments dinku yawan read more din da zan yi muku,infact ma in bakwayin comment Wallahi hutu zan tafi in yaso in kun shirya yin comments din se muci gaba amma bazeyu ina muku posting ace wai comment ya gagara ba.




Comment,like and share 🖋️🖋️




🌹🌹*ASHE ZAMUGA JUNA*🌹🌹



Page 09



*_ story $ written _*


By


* _ MRS 🌹 ISHAM 🌹_*
(Yar lelen Jarumai)




*The writer of*
*NIDA PATIENT DINA*


~And now~
*🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*






📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️






Page 09




Washe gari


As usual kamar yanda suka saba duk sun shirya cikin shiga ta uniform dinsu da ya kasance fari da maron , riga da skirt ɗan guntu se legis fari da suke sanye dashi a ta ciki, se fararen sandals da safa a ƙafafunsu ga baby hijab dinsu suna sanye dashi sunyi kyau sosai sede fah yanda suke tafiya matan su biyar yau ansamu ƙarin mutum daya wato Asrah sun zama su shida yanzu , anyi mata komai da komai zata fara zuwa yau , se murna takeyi itama yau zata cigaba da zuwa makaranta , rabonta da makaranta tunda suka baro California shisa she's very excited yau , duk sun gama breakfast , su sahil suna waje sunyi gaba. Abbu ne yafito hannunshi riƙe da car key ya ce" kuzo in kaiku " dukkansu ihu suka yi suna " yeeeeh yau Abbu ne ze kaimu school" dariya Abbu ya yi ya girgiza kai ya yi gaba suka biyo shi a baya.
Dropping dinsu ya yi acikin school din yana kallonsu seda ya tabbatar sun shiga class sannan ya tafi .
Shiga sukayi class din suka samu seniors din su sun shigo yan SS2 ,kallonsu sukayi sukaga babu yayyunsu maza aciki su Saghar,jawan a SS1 suke. Sudais da Salim,Sahil, sune suke aji daya da su Tajuddeen wato SS2 sede shi ya rubuta paper tare da yan SS3 shisa ya dena zuwa makarantar.


Wuce seniors din sukayi suna gaishesu cikin harshen turanci. Asrah dake bayansu tazo ta wuce bata ko kallesu ba daya daga cikinsu ne ya ce " hey you come here " juyowa ta yi ta kafesu da wa'yannan mayun oiling eyes dinta tana kwabe fuska , sosai Asrah ta tafi da imanin Fu'ad Abubakar Daula ji ya yi be taba kallon yarinya me irin kyau din Asrah ba hakan yasa ya ji yana sonta , magana friends dinshi suke mishi amma shi gaba daya akalar hankalinshi yanaga Asrah.
Matsowa kusa da ita ya yi ya ce " what is your name?" " am Asrah Abdulhameed Bishara by name "ta bashi amsa murmushi ya sa'ke jin yar gidansu Tajuddeen ce ya ce" good go and sit down" wucewa ta yi taje ta zauna a kusa da Zoya .


Bacci yakeyi amma ji ya yi kamar ana kallonshi hakan yasa ya tashi yana Dan mutsuke ido , sauke idon ya yi akan Ammi dake zaune a gefen gadonshi ta zuba mishi idanu kamar zata cinye kauda kanshi gefe ya yi ya tashi akan gadon ya nufi toilet ya yi brush ya wanke fuskanshi ya fito ya zauna akan gadon batare da ya ɗago kai sun hada ido ba .
Ammi girgiza kai ta yi dan tasan inzasu shekara a haka Tajuddeen bazece mata komai ba ta ce " ina kwana Tajuddeen?" tunda yake be taba jin kunya ba irin na yau saboda shi babu agender kunya ma arayuwarshi amma yau se yaji ya kunyata a gaban Ammi, na gaidashi da ta yi hakan yasa ya ji kamar be kyauta ba , kamar yadda yake kuma nature shi yake kullum babu walwala atattare dashi murya ciki_ciki ya ce " ina kwananki " da sauri Ammi ta kalleshi tana tantaman shin maganar nan da gaske daga bakin shi ya fito ko kuma kunnenta ne ya mata gizon jin da ta yi saboda a iya sanin ta bata taɓa jin Tajuddeen ya gaisar da kowa ba saboda hatta a makaranta an sha yin wannan case din ɗan kuwa ko mutuwa malami zeyi Tajuddeen baze taɓa gaisheshi ba,har gwara malamin da yakoyar da su a gida dake wannan ya shafi addini yana iya kokarin shi wajan cewa ya uztaz din "barka da zuwa ya hanya"shikenan iya maganar kenan har malamin ya gama koyar da su ya tafi.


Bata gama wannan tunanin ba ta sake tsinkayan muryanshi yana gaisheta. Muryanta na fita da sauri_sauri ta ce" lafiya lau Taj " tundaga nan kuma shuru ne ya biyo baya babu wanda ya sake cewa komai , matsowa kusa dashi Ammi ta yi gabaki ɗaya yanayin ta ya sauya kallo ɗaya za'a mata a fuskanci tana tattare da damuwa.


" Tajuddeen jibi ne tafiyanka banason ka tafi da fushin Amminka aranka , shisa nazo na roki yafiyarka daka yafemin akan abinda na maka , kayi hakuri karka tafi dani aranka wallahi ina azabtuwa da yanda kake kin kulani da kuma sauran yan uwanka nayi maka imani da Allah babu wanda yataba sa'ka tsanarka aranshi duk muna sonka ,kaine kawai ka cire kanka daga cikinmu ban taba jin inason wani abu arayuwata ba irin kai ɗana dan Allah dan Annabi ka yafemin wallahi abinda yafaru awannan lokacin sharrin shaidan ne " folding din hannunta ta yi tana ba shi hakuri ga idonta da ke tsiyayo da ruwan hawaye , be taba tunani akwai ranar da arayuwarsa ze zo ya tsaya ya saurari Ammi ba saboda kullum laifinta yake gani ,ita ya yi holding responsible na rushewar farin cikinsa amma da yake tsakanin ɗa da uwa se Allah yasa ya ji , baze jure shareta ba har iya rayuwarsa dukda kuwa girman laifukan da ta mishi , (duk wani ɗan arziki kuma ɗan halak baze taba kaunar ganin hawayen Mahaifiyarsa ba sede kuma in wannan ɗan bayida albarka saboda duk duniya babu abinda zaka gani ka ji ko kuma ka tuna kana da ita ka ji dadi kamar mahaifiya , sune jigon rayuwarmu sunyi mana komai alokacin da bamuda komai muna naɗe acikin tsumma ta kula da mu ta yi mana duk abinda ze samu farin ciki. ta sadaukar da nata farin cikin aduk saboda inganta rayuwarmu kuma har izuwa girman mu , wallahi duk wanda yakeson gamawa da duniya lafiya to yabi Allah da manzonshi Annabi Muhammad saw sannan kuma yabi mahaifiyarsa sau da kafa domin in karasa ta bazaka taba samun wata kamarta ba har duniya yanaɗe, Allah kabamu ikon ci-gaba da yiwa iyayenmu biyayya , ya Allah kamar yanda suka faranta mana Allah kabamu ikon faranta musu Duniya da lahira .)


Juyawa ya yi rungumeta ya kwantar da kanshi akan kafadarta yana sauke ajiyar zuciya , a iya saninshi tunda yasan kanshi be taɓa jin shi ajikin mahaifiyarsa ba se yau hakan yasa ya ji shi gaba daya wani farin ciki ya mamaye shi gaba dayanshi kamar ba shi ba, Ammi kam se godewa Allah takeyi da ya nuna mata wannan rana da ta kasance tare da ɗanta mafi soyuwa a gareta shafa kanshi ta yi ahankali ta furta " Ubangiji Allah ya yi maka albarka yabaka Sa'a aduk abunda kasaka agabanka ya karemin kai aduk inda zakaje ka " " ameen " kawai ya ce raba jikinsu ta yi ta ce ta ce " tashi muje dinning muyi breakfast na fara jin yunwa " har cikin zuciyar shi baya son zuwa amma bayajin ze iya ja da maganarta ayanzu , mikewa ta yi ta riko hannunshi suka fito .


Duk suna zaune a dinning table anyi saving dinsu breakfast amma babu wanda yaci suna jiran fitowar Ammi ne sufara cin abinci, Hajiya khareema dama ita ba wani hulɗa takeyi da su ba yasa bata fito ba tana part dinta in takaice muku ma ba ta fiya cin abinci tare da su ba.


Ammi suka hango tana saukowa daga stairs hannunta rike da na Tajuddeen ware idanunsu sukayi sosai dan son tabbatarwa shin dagaske Tajuddeen suke gani da Ammi ko de basu gani da kyau ba.idan kuwa dagaske suɗin ne ta yau ranar Sa'a ce agaresu shine abinda suka daɗe suna jiran su ga ranar da zasuga haka yau Allah yanuna musu . Har su Ammi da Tajuddeen suka iso dinning table din basu sani ba suna ta al'ajabi hade da farin ciki zama Ammi da Tajuddeen sukayi Ammi da kanta ta yi saving din Tajuddeen breakfast yafaraci batare da ya kula kowa dake wajen ba , Ammi ta ɗan kalleshi tana ɗan taɓa hannunshi ɗago kai ya yi ya kalleta yanda babu wanda zejita ta yi mishi rada a kunne " baka gaishe da Abbie din ku ba da sauran " shuru ya yi be yi yanda ta ce din ba yaci gaba da cin abincinshi ,sude duk ido suka zuba mishi Abbas, Hafiz, Ahmed se murmushi sukeyi sukansu sunyi farin cikin haka da yafaru saboda duk acikin kannensu sunfi kaunar Tajuddeen kullum basu da burin da yawuce suga suna tare dashi suna hira na farin ciki da annashuwa amma hakan beyuba .
Seda ya kusa cinye breakfast din shi tukun kanshi na akasan be ɗago ba ya ce " ina kwana" gaisuwar ya yi be kira sunan kowa ba murmushi kawai sukayi suka amsa atare , haka sukayi breakfast dinsu yau na musamman duk da Tajuddeen tunda ya yi wannan gaisuwar be sake ce musu komai ba har ya gama ya mike ya yi part din anty amarya dan duba Asrah shi duk a tunaninshi tana can tana bacci bayida masaniya akan yau ta shiga school , yana daff da fara haura upstairs Hafiz ya ce " Asrah fa sun tafi makaranta itama yau ta jonasu" kallon Hafiz ya yi ya ce" okay " yawuce part din shi .


Abbie ne ya kalli Ammi ya ce " alhamdulillah hamdiyya gwara da kika je kika samu kukayi magana dashi naga yafara saukowa yanzu , Allah ya sassauto mana da irin wannan zuciyar ta shi " dukkansu da ameen suka amsa amma banda Hajiya Hurairah da ranta ko kadan be so haka ba Allah_Allah takeyi a watse ta je ta samu Hajiya khareema ta shafa mata labarin abinda yake faruwa , domin hakan barazana ne ga kudirin su .







Tun daga safe har yanzu da ya kasance karfe biyar saura sun kusa tashi , Fu'ad Abubakar daula ya shiga ajinsu Asrah yafi aƙirga dan kawai ya kalleta , su kam sunata murna ankusa tashi su dawo gida .
Lokaci nayi aka buga kararrawar tashi driver's din sune suka zo suka daukesu zuwa gida .






Misalin ƙarfe 5:30pm na yamma malam Mamman yashigo gidanshi hannunsa rike da wata atamfa me saukin kudi dakin Maryam yashiga yasameta suna zaune suna shan shayi da biredi ita da Asmita zama ya yi fuska asake ya ce " yar baba gama kizo muje mukai ɗinkin kayan kin nan dana siya miki " cike da yarinta Asmita ta ce" to baba" kallonshi Maryam ta yi ta ce" malam senaga kamar yamma ta yi da kun bari ko go...... "be bari ta karasa faɗan abinda takenso faɗa ba ya yi saurin ta ran numfashinta ta hanyar faɗin" ah ah Maryamata yau zamu kai dinki dan gobe mukayi da telan ze gama mata kayan " sam hankalinta yaki yarda da fitan da zasuyi amma gudun bacin ranshi yasa ta yi shuru , zuciyarta se sake_sake yake mata ga zuciyarta dake bugawa sosai , ka sa ci gaba da shan shayin ta yi ji tayima ba ya mata dadi ko kadan , Asmita na kammalawa ta ce" baba na gama " " yar baba tashi muje " saka mata hijabi ya yi ya dauketa suka fito har bakin kofar gidan Maryam ta rakosu se bye-bye Asmita take mata da murmushi me ƙayatarwa akan fuskanta har suka bacewa ganinta sannan ta koma cikin gida , ji ta yi abu me sanyi ya sauko mata akan kumatunta da sauri tasa hannu dan jin menene wannan ruwan hawaye ta gani aranta ta ce" to menene yasa idona yake zubar da ruwa ?Allah kadawomin dasu lafiya " ta shiga daki ta zauna.




Napep malam Mamman ya tara suka shiga ciki ya fadmɗawa me napep inda ze kaisu , tafiya suka yi me matukar nisa da seda yasa Asmita ta gaji ta kwanta ajikinshi har bacci ya fara daukanta taji napep din ya tsaya fitowa ya yi da ita ya sallami dan adedeta sahun ya yi tafiyarsa , wata dankareriyar bakar jeep yanufa yana rike da hannun Asmita lokacin da ya iso motar kwankwasa gilashin ya yi aka sauke wasu murɗa_murɗan maza nagani zaune aciki fuskar su babu alamar imani , malam Mamman jiki na rawa ya ce" yawwa ga yarinyar na kawo muku ita seku ban sauran cikon kudin nata " fitowa daya daga cikinsu ya yi. ya karbi Asmita a hannun malam Mamman tirjewa tafarayi tana kallon babanta agaban idonta aka fito da kudin da suka kai kimanin naira dubu dari biyar aka ba shi, wanda yake zaune acikin motar ya ce" da farko mun baka dubu ɗari biyu yanzu ga cikon saura nan du ka yakama ka siyar mana da yarinyar dubu ɗari bakwai kenan " hannu na ɓari yakarbi kudin yana " eh

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login