Showing 81001 words to 84000 words out of 94974 words

Chapter 28 - ASHE ZAMUGA JUNA COMPLET BY MRS ISHAM.txt

28 Dec 2024

8676

ki dinga sanar da ni,ki shiga jikinsa sosai ta yanda zamu dau fansar mu akansa.bincike za ki mana sosai akansa Kinga ke ce kuke gida daya,duk wani shirinsa daga zaran kin gano ki sanar dani".
With full confidence ta ce"na maka alkawarin aiwatar da hakan Fu'ad".ji ta yi kamar motsi yasa ta kashe wayar.ta ajiye agefe.


Jin bata sake jin motsin bane ya sa ta,kwanta tunani fal ranta, gaskiya ne maganar da Fu'ad ya faɗa mata shi mugu bashi da kama.




Se juyi takeyi amma bacci ya gagara daukar ta har karfe hudu na dare idonta biyu.




Yawancin ku baku san two pages nake haɗa muku ba, wanda hakan na nufin in an yi update yau, baza'a yi gobe ba se jibi.


*🌹🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹🌹*




Page 27




*_Story & written_*



By


*MRS🌹ISHAM🌹*
( Yar lelen Jarumai)








*THE WRITER OF 🖋️*
*NIDA PATIENT DINA*




~And now~
*🌹ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*






📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️




____________________________


Page 27


Se da aka fara kiraye _kirayen sallah asuba ne bacci ya ɗauke ta.tasha kukanta san ranta hatta gaji.


Anty amarya ta tasheta ta hanyar kwankwasa kofar dakin da take kwance,tashi ta yi ta bude mata.
"Sabriyah lokacin ya yi" to "ta ce ta dauko hijab tabi anty amarya zuwa bedroom nata.


Bayan sun idar da Sallah nan ne anty amarya take sanar da ita yau malamin islamiyya ze zo yake koyar da su, boko ma gobe zasu fara zuwa.


Godiya ta yi mata Sannan ta hau kan gado ta kwanta dan kuwa ba ta gaji da yin bacci ba.ita ma kwanciya ta yi kusa da ita tana kallon yanda take bacci.
Karfe tara suka farka bacci,wanka sukayi suka shirya zuwa dinning ita de Sabriyah hijab ta saka dan yanzu dadinsa takeji.


Bedroom din uncle Hameed anty amarya ta nuna mata kafin su fita.


Shiga ta yi ta sameshi yana zaune akan sallaya da alamu tunda suka dawo daga masallaci be koma bacci ba.
Zama ta yi a kasan carpet tana gaisheshi.
"Ina kwana daddy"
Sunan da ta kirasa dashi, ya ji dadi sosai,tun bayan ɓatar Asrah ba'a sake kiransa da daddy ba.
"Lafiya klau sab,ya mommy ki!?"
"Tana Lfy lau, lokacin karyawa ya yi"murmushi ya yi, ya ce "to muje ko!?"
Ya mike suka fito a tare suka samu anty amarya tana tsaye inda ta barta.


Dinning suka shigo suka samu an gama serving din breakfast,kowa na wajen da murmushi suke kallonsu sun yi kyau gwanin sha'awa family.


Zama suka yi,ana cikin cin abinci Hajjatiye ta soma magana.
"Nikam meye ya hana, khareema da Huraira zuwa cin abinci cikin mutane sun maƙale a part din su kamar wasu munafukai,ko har yanzu khareema na nan da ba ƙin halinta nakin zuwa a ci abinci da ita"ta yi maganar tana tsare Abbie da ido.
Abbie bawan Allah gaba daya ya ma rasa ta ina ze fara sanarwar Hajjatiye da Ammuh bata cin abinci kwata_kwata da kowa,ba dan ya so ba ya mata karya ta hanyar faɗin.
"Hajjatiye!, khareema yau da ciwon kai ta tashi"
Dogon tsaki Hajjatiye taja ta ce.
"To waye ya damu da tsiyar tsinantakar ciwon kanta,mu din aka ce mata,wani lafiyar ne garemu ai sede kawai a ce Alhamdulillah,to Wallahi kar ta kuskura a sa'ke zuwa cin abinci ba ta nan ran kowa ze ɓaci".
"In sha Allahu, hakan baze sa'ke faruwa ba".cewar Abbie,dan ya lura Ammuh na son ja mishi magana ne a wajen Hajjatiye.dole ya taka wa rashin fitowarta burki.
Ta maida kallonta kan Abbu,kafin ma ta yi magana ya ce.
"Hurairah bansan me ya hana ta zuwa cin abinci ba".
Tabe baki ta yi,
"To ai dama iyayin su daya,ita da khareemar".
Su de sauran cin abincinsu suke yi suna saurarar abinda ke faruwa.


"Kuna gama cin abinci duk za mu tafi asibiti,bana son African time"Hajiya babba ta faɗa tana rufe plate din gabanta, alamar ta kammala cin nata.


Shurun da taga kowa ya yi basu tambayi waye a asibiti ba,yasa ta fara tunanin to waye ba lafiya.
Se kuma ta yi tunanin ko LTG aka kai asibiti tunda jiya bashi da lafiya.
Tabe bakinta ta yi, acikin zuciyarta ta yi maganar amma bata san cewa ya fito fili ba.
"Allah yasa ma shine"kallonta aka yi nan ta fahimci an ji abinda ta faɗa sunkuyar da kanta ƙasa ta yi tana wasa da spoon.


Hajjatiye ta ce "sanariya ke da waye haka". innalillahi ga dariya ga kuma basu isa su yi shi ba yanzu se ran kowa ya kusan ɓaci a wajen,wai sanariya, Sabriyah din ne bata iya faɗa ba take cewa sanariya.


Salim duk yanda ya so rike dariyar sa,abin ya gagara se fa da ya kwashe da wani dan banzan dariya kai kace wani zararre ne.
Cikin basaja ya soma faɗin.
"Haba Fatime taya za ki sakamin ruwan tea da yawa duba kiga duk na shanye,ashe zan iya" maganar yake yi amma dariya ya ci karfinsa.
Kowa na wajen ya gano sa.banda Hajjatiye.
Watsa mishi harara Abbie ya yi,irin zamu haɗu din nan.


Dakyar ya tsagaita da dariyar.
Hajjatiye ta ce"amma yaron nan an yi ja'iri, saboda kawai ruwan shayi ya yi yawa ka shanye ne yasa ka wannan dariyar,to zakaci kwal ubanka dakai da tsiyar tsinantakar ruwan shayin".


Tashi kawai ya yi yabar wajen dan ya lura inde Hajjatiye tana magana tofa baze fasa dariyar ba,har ta gano ita yake yi wa dariya,ga kuma kallon da yaga Abbie na yi masa.


Kammala breakfast din aka yi suka dawo falo suka zauna,anty Sameera na rike da baby a hannunta.
Ta cewa su Zoya.
"Ku din kun shirya ne" "eh a shirye muke"duk suna sanye da hijabs.


Sabriyah de yau ba wani son yin magana take yi ba domin abinda ta ji, jiya dashi ta kwana a ranta,duk tunaninta yanzu ya koma ne ta kan ta ya zata fara sanin menene abinda LTG yake shiryawa.shin taya zata shiga jikinsa yanda zata dinga sanin duk wani abinda yake shirin yi.




"Sanariya!,zo ki kira LTG kice mishi,zamu je asibiti"Sudais ya faɗa,yana tsokanar ta.murmushi ta yi dan ta gane tsokanar ce,wato Hajjatiye de ta sa mata wani suna daban.


Ba dan ranta yaso ba ta mike tana tambayar kanta "dama ba ya Taj bane a asibitin ba!?,to waye ba lafiya haka!?",da wannan tunanin ta shiga part din nashi ,ko sallama ba tayi ba ta kutsa cikin bedroom dinsa.


Baccinsa yakeyi gently,his innocent face looks so cute.
Yana cikin bargo ya rufe ko ina a jikinsa, fuskarsa ne kawai a waje.


"Mtsssw!a kwai kyaun fuska kam,amma babu na zuci.mugu kawai".ta faɗa a ranta.
Karasawa jikin gadon ta yi da niyar tashinsa a bacci da yake yi.wani tunani ta yi.
"Uhmm,yanzu ina tashinsa ze hau ni da faɗa kamar wani ubana,gwara in je in samu ya Sudais in ce masa,ya ce bazeje ba kawai "ta faɗa a hankali.


Tana gama faɗar maganar,ta ji an ja hijab din ta,a tsorace ta kai idonta kan fuskarsa domin ita ta ɗauka ya farka ne ya rike mata hijab,ashe cikin bacci ne ya juya ya daura kansa akan hijab dinta,da bata san ya aka yi ta daurasa kan gado ba.
A hankali ta sa hannuta ta fara kokarin jan hijab din nata yanda baze tashi ba.tana kallon kyakyawar fuskarsa,a lokaci daya kuma tana jan hijab din ta.
A cikin bacci yasa hannu ya riƙo hijab din nata gam a hannunsa ya cigaba da bacci.
Zaro ido ta yi ta bude baki ta ce"na shiga ukuna,yau in ya Taj tashi se ya kasheni"ta yi maganar idonta ya fara raina fata.
Wani irin juyi ya yi da,wanda kafin ta ankara taji ta gaba daya ta faɗo jikinsa.


Ji ta yi kamar zata yi fitsari a wando.ta rasa wata kalma zata yi amfani dashi wajen ceton kanta in LTG ya farka ya gansu a haka.


Jin mutum ya faɗo kansa ne,yasa ya bude manyan rikitattun idanunsa da sukayi ɗan yi ja saboda baccin da be samu a wadace ba, hatta golding eye balls din seda suka ɗan canza kala.


Idanunsu ne ya sarke cikin na juna.bakaramin tsorata ta yi ba da ganin idonsa ga kuma irin kallon da yake mata,babu abinda take tunawa irin rabuwar da sukayi daren jiya ga shi yanzu ta kawo kanta da kanta.
Shi kuma kallon da yake mata,kallon me yakawo ki dakina har kan gado na.


Hannunsa yasa ka ya rike ta gam yanda bazata samu damar guduwa ba,tana kwance akan kirjinsa, fuskarsu na fuskantar na juna.


Bude baki ya yi ze yi magana,tsoron jin abinda ze furta mata ne yasa da sauri,tasa yatsan ta,guda daya ta daura akan libs din sa.tana kallon cikin idanunsa,saukar da idonsa ya yi ya kalli hannunta da ta daura masa akan libs,watsa mata harara ya yi,duk da hakan bata cire ba.


"Ya Taj,an ce ne in zo in tasheka zamu je asibi.....".
Wani mugun kallo ya watsa mata da ya sa ta gagara karasa maganar da take masa.
Hannu yasa ya janye yatsan nata ya maida shi baya ya matse, ƙara ta sa sakamakon zafin da taji ya ziyarci hannunta.
"Kirana kika zo yi shine se kin hau har kan gado na!?"ya tambaye ta murya a narke ba kamar yanda ya saba yin magana ba.
"To ai na baka hakuri"ta faɗa tana murguɗa masa baƙi,tsurawa dan karamin baƙin nata da take murguɗawa ido ya yi,yana jin kamar yasa almakashi ya gimtse sa.
"Tashi a jikina,wato kinga farar fata, mekyau yana shining, shine za ki kwanta akai,yafi na wa'yannan nan kazaman yan iskan samarin naki".tura baƙi ta yi jin abinda ya faɗa.
"Bazaki tashi min a jiki bane,ko se na yi wurgi dake tukun nan!?"ya faɗa yana jefa mata harara.
Kamar zata fashe da kuka dan takaici,ta ce"to ka sa'ke ni mana".
Kura mata ido ya yi,yaga yanda ta ke mutsu_mutsun kwatar kanta.da hannunsa guda daya ya rike ta amma ta gagara kwacewa.


"Meye kike shiryawa!?"kamar saukar aradu haka taji tambayar ya sauka a kunnenta,dago idonta ta yi,cikin tashin hankali,murya na rawa ta ce"bangane abinda kake nufi ba".
Murmushin gefen baki ya yi irin na bakida hankali, ya ce"ina saurayin naki yake!?,ina guje miki yin aikin danasani saboda rashin sanar da ni inda yake dede yake da jefa rayuwar ki, cikin hatsari,ni rayuwata,na ƙasa ta ce,in na mutu nayi shahada,amma ke in mutum daya ya mutu ta dalilin ki,to se Allah yabiwa wannan bawan nasa hakkinsa,je kiyi tunani akai".gaba daya ya kashe mata jiki da maganganunsa,kenan hakan yana nufin ya san tayi waya da Fu'ad kenan?,taya akayi ya san abinda suke shiryawa.
Meye hakan yake nufi to, Fu'ad ya sanar da ita cewa LTG shine yake kokarin zaluntar al'umma,shi kuma LTG ya ce mata,in mutum daya ya mutu ta dalilinta se Allah yabiwa wannan bawan nasa hakkinsa.


Har ya sa'ke ta bata ma sani ba,ta faɗa duniyar tunani.


Ɗagata ya yi a jikinsa ya tashi zaune ya barta akan gadon,miƙewa tsaye ta yi,jiki a mace.


"Kai ma ai zaluntar al'umma ka ke kokarin yi,ka kuma cutar da ni,da yar uwata".
Be kalli inda take tsaye ba ya bata amsa da.
"Ke ba ki kai matsayin da zan tsaya ina miki bayani ba,je ki yi duk yanda kika gadama".


Da gudu ta fice a dakin,tana gudu numfashinta na sauka da sauri sauri,kirjinta ya rike,sun sa ta a tsaka me wuya,yanzu da maganar waye a cikin su tasan zata yi amfani?.


Bayan balcony ta je in da babu wanda ze ganta,ta zube akan guiwowinta tana maida numfarfashi.
Se da ta kusa 20minute a haka kafin ta samu nutsuwa.
"Ko ma me ze faru sede ya faru amma bazan taɓa juyawa Fu'ad baya ba, wannan alfarma ne da ya nema a wajena taya zan watsa mishi kasa a ido in ƙi cika masa burinsa na son ganin al'umma tasamu zaman lafiya".
Ita kadai take magana kamar wata zautacciya.
Se da ta gama samun nutsuwa kafin ta mike ta koma main part Sudais, yana ganinta ya ce"Sabriyah ai na kika tsaya ne!?,ina LTG?"jiki ba kuzari ta ce "ya ce wai baze je ba".
Gyada mata kai ya yi.


Shiga motar sukayi suka wuce asibitin.


shigowar su dakin da aka kwantar da Asmita sun samu ta na jingine da filo.Saghar na gefenta ga kuma fruit agabanta,tasha kadan ta bari,jin sallamar su ne yasa suka maida idonsu baƙin kofar.


Mamaki da al'ajabi lokaci daya ya kama Sabriyah ganin Asmita kwance akan gado ga kanta dake nade da bandage,da gudu ta shigo dakin,ta zauna akan gado, bata gajiya da kallon Asmita da itama din ita take kallo.wato wayo sukayi mata,su ka dinga ce mata Asmita na hutawa,ashe basa son tasan an yi aikin ne.


"My Jerry yaushe akayi miki aikin?,yanzu ya kike jin ki!?,me yake miki ciwo yanzu!?, sannu kinji".ta watso mata tambayoyi ba tare da ta bata damar amsa mata ko daya ba ta sa'ke cewa.
"My Jerry,kanki ba ya Miki ciwo ko!?"murmushi kaɗan Asmita ta yi.
Murya na fita a hankali ta bata amsa da.
"My Tom ina lafiya".
Zata sake yin wata maganar Saghar ya dakatar da ita ta hanyar faɗin.
"Ba'a son ta dinga magana sosai".
Gyada masa kai ta yi tana riƙe hannun Asmita.
Sannu su kayi mata da jiki kafin suka zauna suna.


Har karfe hudu na yamma suna tare a asibiti mazan kuma sun tafi wajen aikinsu.




Kullum se sunje asibiti duba jikin Asmita, Alhamdulillah jikinta yana sauki sosai, Sabriyah ta fara zuwa school an sa ta a jss 2,an samo malamin da yake koya mata karatun addini a gida,kuma ba laifi tana ganewa sosai da sosai.in ta dawo gida kuma su Parsa haka suke haɗuwa su sa'ke koya mata duk wani abinda bata gane ba,sune malaman lessions din ta.




Bayan wata daya, abubuwa da dama sun faru,mom Rumanatu ita da yaranta sun koma katsina.an sallamo Asmita daga asibiti jikinta ya yi sauki,har ta fara maida kibanta,sunci gaba da zuwa makaranta tare da Sabriyah sun yi kyau sosai sunyi fresh sun zama yan gida su ma,duk abinda za'a yiwa su Rameesa tare ake yi musu.kullum se ta yi waya da Fu'ad idan ta tabbatar da kowa ya yi bacci,duk da ta rage alwashin da ta dauka akan LTG domin taga duk tunaninta, LTG ya take ta ya shanye,ita yanzu tsoro ma yake bata,wani abun kamar akan idonshi takeyi hakan yasa ta watsar da mukaman ta,duk da haka Fu'ad be dena in gizata ba.duk da yaga yanzu ita ta karaya.wannan dalilin yasa ya sake sabon mugun shiri.
Daga LTG, Sudais, ACP Jawan duk busy ya musu yawa kullum karfe shida na safiya suke fita,su dawo tara ko goma LTG kam yana kaiwa har karfe daya wata rana ma baya kwana a gidan.aiki ya sha musu kai suna nan suna dakon shugaban kungiyar Italian Mafia,domin any moment ze iya yin abinda yace ze aikata.


Wannan dalilin ne yasa rabon da Sabriyah tasa LTG a idonta hatta manta domin yakai kusan sati biyu rabon da taga ko da gilmawarsa,sede tana yawan ganin major Marry.


Yau Friday tun 12:00 aka tashe su daga makaranta driver yazo ya maida su gida.suna shiga suka ga samarin gidan gaba daya cikin fararen shadda ɗinkin half jumfa bakaramin kyau sukayi ba,sun shirya zuwa masallaci tare da su Abbie da Abbu, uncle Hameed,suna zaune da alama akwai wanda suke jira ya fito.
Tunda suka shigo cikin falon Saghar da Asmita suke satan kallon junansu.uniform din jikinta da ta saka ne yau yasa ya ji kishi yakamasa ransa ya ɓaci ya rasa dalilin da yasa ranshi yabaci dan yaga Asmita da uniform din bayan kuma Sabriyah ma shine a jikinta amma be ji hakan ba,kuma su Rameesa ma makarantar sukayi amma be taɓa jin akwai wani abu dangane da uniform din ba se yau da ya gani a jikin Asmita.
Riga da wandon spot Wear ne wandon yana da fa ɗi,haka rigar ma yana da girma kadan da kauri,irin kayan yan kwallo,sun saka baby hijab.ga school back din su dake rataye a kafadarsu.
Kauda idonsa ya yi daga kanta ya fuske kamar be ganta ba.


Shigowa sukayi wajen su, suka gaishe su cikin girmamawa.


Murmushi Abbie ya yi "sannunku da dawuwa yan boko,kun sha gajiya kam"su ma murmushin suka yi, Asmita ta ce "Abbie ai ba wahala,kawai de zama"dariya sukayi.
ACP Jawan ya ce "to ai babu maraban dambe da faɗa" "tom wannan waya gaya maka Hausa ya ishe ta ɓalle ta san me kake nufi"cikin zolaya Sudais ya faɗi haka.


Shagwabe fuska ta yi "Abbie ka ga ya Sudais ko!?" "Kyaleshi kishi yake yi dan kina zuwa makaranta shi baya zuwa".dariya Sabriyah ta yi jin shirmen Asmita.ga Abbie ma da ya biye mata.


Duk yanda tasan zata yi Saghar ya kalleta ko za ta samu nutsuwa amma abun ya ƙi,tunda ya sunkuyar da kansa kasa yafara danna wayarsa be sa'ke dagowa ba.




Fitowa ya yi falon yana sanye cikin farar danyen shadda half jumfa ,me tsadar gaske,an yi mishi aiki na alfarma,yana sanye da bak'ar takalmi,ga Rolex wrist watch daure a hannunsa.kan sa babu hula se gyararren bakin sumar kanshi da yasha gyara yana sheki da daukar ido.ga baƙin tsadadden sun glass manne a fuskarsa,ya ƙara ƙawatar da fuskar.
Ya yi kyau sosai me matukar nutsuwa da daukan hankali,duk yanda ka kai ga kamewa,idan ka masa kallo ɗaya se ka ji sha'awar sa'ke daura ido a kan sa,ga daddadar Kamshin turaren dake tashi a jikinsa.
Tunda ya shigo falon Sabriyah ta kasa dauke ido akansa,bata taɓa ganin sa da manyan kaya ba se yau,se ta ga manyan kayan ma sunfi mishi kyau da karban sa.


"Tajuddeen manyan kaya suna maka kyau sede bakason sawa"Abbie ya faɗa yana dafa shi.
Kallon Abbie ya yi be ce komai.


Haɗa ido ya yi da Sabriyah dake satan kallon sa, harara ya watsa mata.
Tabe baki ta yi,magana kawai ta yi.ba tare da kowa ya ji ba iya labban bakinta ne yake motsawa yanda iya LTG ne ze ganta ta ce.
"Ko kyau bakayi ba,ka dena wani yanga,kanajin kanka na wani girma".


Hannunsa yasaka a wuyansa ya mata alamar se na yanka ki.


Dariya ma yabata.yanda ya mata alama da ze yankata ne abin yasata dariya.


Tana dariya ta ce"to se kun dawo Allah ya kiyaye hanya, Abbie, Abbu, daddy,amana addu'a " "in sha Allah "suna bata amsa ta haura part din su Asmita ma tabi bayan ta.


Abbie da Sudais su kadai ne suka lura da abinda LTG da Sabriyah sukayi,su kansu abin nasu ma dariya ya basu, wato tsakanin LTG da Sabriyah babu shiri.
Ko wannensu motarsa ya shiga driver yaja su , sojoji da kuma da polisawa da securities ne suka musu taki har masallacin.


Suna shiga dakinsu suka tarar da su parsa a ciki,suna taɗi, hiran wani saurayin da Zoya ta yi jiya sukeyi,suna dariya.


Ɗago kai sukayi dukkansu, dama zaman jiran dawuwar su, sukeyi su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login