Showing 78001 words to 81000 words out of 94974 words
sukayi shuru.
Har aka isa shopping mall din babu wanda ya sake cewa komai.
Ciki suka shiga suka bar mazan suna waje suna jiran su.
Sosai sukayi wa Sabriyah da Asmita shopping kaya na ban mamaki masu yawan gaske da kuma tsada,kama daga kan kayan sawa,kayan make up, perfumes, shoes, bags,hijabs,gyale, jewelrys,sari(lufaya), shower items, lotions,duk wani abinda aka san mace zata yi amfani dashi seda aka siya musu,wajen pad suka je,anty Sameera ta fara ɗiba musu tana sawa a basket,daukan guda daya Sabriyah ta yi ta matsa kadan taji da laushi.
"Anty Sameera meye wannan din?, amfani me ake yi dashi?"anty Sameera ta ce mata "wannan din pad ne ,ana amfani dashi ne lokacin period".
Sa'ke je fa mata wata tambayar ta yi domin bata fahimci abinda take nufi da period da kuma pad ba.
"Anty Sameera su din meye su to"se yanzu ne anty Sameera ta kalleta da mamaki,dazun da ta mata tambayar menene pad ko kadan bata yi mamaki ba saboda wasu basa amfani dashi,da tsuma suke amfani shisa bata kawo komai a ranta ba.
Danne mamakinta ta yi,ta ce "idan kina al'ada da me kuke amfani ke da Asmita"nisawa ta yi kadan domin anty Sameera ta sa ta a duhu bata fahimci abinda ta ke nufi ba.
"Ban san me kike nufi ba anty Sameera"kallon yan matan ta yi taga babu wacce hankalinta yake kansu kowa tana ɗaukan abinda take so ne.
Ta jawota gefe kadan ta ce "Sabriyah idan karshen wata yazo,in kuna jinin al'ada da me kuke amfani!?", girgiza mata kai ta yi,kamar wata wawiya ta ce"jini?, karshe wata? ni haryanzu bangane ba jini aina!?",ta jefa mata tambayoyi uku at one time.
Jinjina kai anty Sameera ta yi wato de in ta fahimta Sabriyah na nufin ta ce mata,daga ita har Asmita babu wacce ta taɓa yin period a cikinsu,tunda ga shi bata ma san ni ba,ta yi mamaki sosai.ta ce zasu karasa maganar a gida.
Bangaren wayoyi suka je,nan Anty Sameera ta dauka musu waya iphone 12 normal su biyu ita da Asmita,irin na hannun su Umaisha.
Layi me register suka karba guda biyu.komai sun gama siya,an je wajen bill anty Sameera ta bayarda ATM guda daya.
Duk hankalinsu nakan wajen bill suna hira.
Ji ta yi an rike hannunta an cusa mata takarda a hannu da sauri ta juya dan ganin waye haka, bata iya ganin fuskarsa ba se bayansa yana tafiya harya yi nisa.
Kallon takardar ta yi kafin ta bude,suna ne a jiki da kuma number waya.suna an rubuta Fu'ad.
Amma bata iya karatu ba ɓalle ta fahimci sunan.
Chukuikuye takardar ta yi da niyar ya sarwa,se zuciyarta ta raya mata da ta kira number ta ji waye.sake kankame takardar a hannu ta yi tana mamakin to waye haka,kuma aina ya santa.
Yaran shopping mall din ne suka kwashi kayan suka kai musu zuwa motar.
yanda suka zo haka suka koma, yanzu kamar dazun har suka dawo gida Parsa batayi magana ba.ita kanta Iklas seda ta yi mamaki kowa yasan ba halinta bane wannan amma ta yi shuru kamar me tunani.
Fita a motar Iklas ta yi ta barsu su biyu.kokarin bude motar ta yi taji taki budewa ta fahimci sarai Sahil ya saka lock ne a motar.
"Masoyiya meya sameki gaba daya kika sauya kamar ba ke ba!?"ya tambayeta yana tsareta da idon sa da takejin kunyar kallo.
"Bakomai"ta ba sa amsa a hankali.
"Karya kike, kowa yasan ba haka kike ba so tell me is something wrong?"girgiza mishi kai ta yi.
Haɗe fuska ya yi "kalli idona da kyau"ka sa dagowa ta yi.
Ya sake maimaita mata a karo na biyu.
"Kalli idona Parsa".
Dakyar ta iya masa kallon da be fi na second biyu ba.
"Tom sanar da ni meke faruwa".
Hawaye ne ya gangaro daga fuskarta,ya ɗigo akan hannunta.
Da mamaki ya sa'ke kallonta.
"Bazakiyi magana ba!?".
Tana sheshekar kuka ta ce "to ai ya Sahil kai ne".
"Ni ne meye Parsa"
Share fuskarta ta yi ta ce "to ba kai bane kace kana da budurwa a kano ba,kuma shine baka sanar damu kana da budurwa ba, ko a waya fa baka taɓa haɗa mu da ita ba ɓalle mu san antyn na mu,for God sake hakan ya yi ya Sahil.kasan yanda muke so a sha biki a gidanmu kuwa musamman na aurenka se yafi na kowa dadi,se munyi event goma a matsayin mu na ƙannen ango". lokaci daya ta canza magana domin bata da karfin guiwar da zata iya faɗa masa tana san shi, wannan dalilin yasata sauya maganar kawai.
Tunda ta fara magana yake kallonta,be yarda da Abinda ta faɗa ba,kawai ya ji ta ne, murmushi ya yi ya bude mata kofa yana murmushi.
Ya ce"shikenan yau din nan zan haɗa ku waya da ita".
Yaƙe ta yi ta fice a motar.
Bin bayanta ya yi da kallo har ta shige ciki.
Ajiyar zuciya ya yi, ya ce "nasan abinda yake cikin ranki masoyiya".
Yana fitowa daga motar yaga su Abbu sun fito duk sunyi alwala zasu je masallaci binsu ya yi.
"Saghar sun dawo ne,ya aikin nata?"
Ya tambayi Ashman.
"Alhamdulillah an yi aiki successful.se gobe za'a fara ganinta".
Shima "Alhamdulillah"ya faɗa.
Suna shigowa Sabriyah ta nufi part din Hajiya babba ta ga ko Asmita ta farka daga bacci,sannan ta yi mata albishiri da an siya musu sabbin wayoyi.ga kuma takardar da har lokacin yana rike kam a hannunta.
Haɗuwa da Hajiya babba ta yi a mahayan ƙarshe,ta ce"har kun dawo kenan?!", "Eh mun dawo Hajiya babba zan je in duba Asmita ne "riƙo hannunta ta yi ta ce"ya'yan ku Tajuddeen yace kar abar kowa ta shiga part din se bayan ya dawo".
Ba dan ranta yaso ba haka suka dawo main part da Hajiya babba,
Anty sakeena ta ce "ku je kuyi sallah"miƙewa sukayi banda Sabriyah dake zaune ta saba duk sanda zasu je yin Sallah tana zaune abunta.
Kallon ta anty sakeena ta yi.
"Sabriyah tashi muje muyi sallah" "to"
ta bi bayanta.
Ta ce mata ta shiga ta yi tsarki.bayan ta yi ne,ta koya mata yanda zata yi alwala.itama ta dauro nata alwala.
Sannan ta ce mata duk yanda ta yi a sallah itama ta yi.
Haka sukayi sallah tare suka idar.
Uncle Hameed ya dawo gida.ya sanar da mom Rumanatu da Abbie,an yi nasara a aikin da aka mata,ba za'a jima ba zata farfaɗo shisa Saghar be dawo ba yana can.
Lokacin dinner ma gaba dayansu sun hallara,a dinning an yi saving din kowa abincin da yake so, Ammuh de bata fito ba dama can ita bata cin abincin su akan dinning se lokaci zuwa lokaci da Abbie yaga bata so se be ce lallai dole se tazo ba,haka ummah ma duk da ita tana fitowa amma bako da yaushe ba.
Fatime na gama serving din su takaiwa Ammuh da Ummah nasu part din su.
Ita de Sabriyah ta gama fahimtar akwai wani abu da ake boye mata,ba sa son ta sani,amma tunda LTG ya ce se ya dawo zataga Asmita to ita kuma ko karfe ɗari na dare ze dawo seta jirasa.
Bata wani ci abincin sosai ba,ta cire hannunta ba wani yunwa take ji ba.
"Ya kika cire hannunki"cewar Parsa.
"Masoyiya na koshi Wallahi".
Anty amarya dake gefenta bata ce mata komai ba, tasan dalilin ta be wuce rashin ganin Asmita bane.
Dawood ne ya miko mata wayarta.
"Yawwa ga shi na seta miki komai,daga icloud har updating din wayar na miki.
Wayarki za ki iya fara amfani da ita.akwai kati a ciki sannan data kuma daga zaran kin kunna WiFi shikenan,bakya bukatar data gidan nan kowa WiFi dinsa yake budewa".
"To na gode ya Dawood".
"Don't mention ".
Kallon wayar ta yi.tana Allah_ Allah su watse anan taje ta dauko takardan da ta boye,ta kira taji waye ne.
Hira sukayi kafin Hajjatiye ta ce ita fa surutun ya ishe ta,ta barsu a falo taje ta kwanta.
9:00pm na dare ta fara motsawa alamar zata farka.dakyar ta samu ta daga hannunta da ya yi mata nauyi ta ɗan da fa kanta,ji tayi kan akwai bandeji gaba daya an zagaye sa dashi,ga wani uban ciwo da kan yake mata.
Runtse idonta ta yi,tanaso ta tashi amma jiri ya hanata.
Ta riga da tasan a inda take,domin lokacin da suka iso asibiti ta farfaɗo nan uncle Hameed ya sanar da ita yanzu za'a shiga da ita operation,allura akayi mata na bacci fuskar Saghar shine fuskan wanda ta gani kafin ta faɗa bacci.
Hakan yasa a hankali muryanta baya fita sosai ta soma kiran sunan sa.
"Me kyau!me kyau!me kyau"yana bakin kofa suna magana shida wani doctor ya ji kamar ana magana a cikin dakin.
Shigowa ya yi ya sameta tana kwance idonta abude.
Murmushi ya yi ganin ta farka.
"Sannu ko,yanzu ina ne yake miki ciwo".
Bata ba shi amsar tambayar da ya mata ba ta ce"Sabriyah ta zo ne!?". girgiza kai ya yi.
Murya a hankali ta kuma cewa"meyasa batazo ba to me kyau !?",jin sunan da ta kirasa dashi ne yasa ya kalleta da kyau,wato wancan memoryn yarintar da ta shiga ba duka bane ya gushe ba,tunda ga shi still bayan ta dawo hayyacinta tana kiransa da me kyau.
Ya ce"bata ma san an yi miki aiki ba saboda zata iya tayar da hankalinta amma gobe duk zasu zo dubasu da jiki"gyada masa kai ta yi.
"Kai na!,na mini ciwo sosai kuma ina ganin jiri"zama ya yi a gefen gadon ya ce "ehh wannan normal ne,nan da wasu kwanaki za ki dena jin haka".
Shuru ne ya biyo baya daga ita har shi babu wanda ya sa'ke cewa komai.
"Me kyau ban san sunanka ba"batare da ya kalleta ba,ya amsa mata da "Saghar".
Nan ma shuru ne ya sa'ke ratsawa, miƙewa ya yi ze fice,dan ya rasa meyasa duk lokacin da yake tare da ita se ya ji wani iri.
"Ya Saghar tafiya zakayi ka barni ni ɗaya!?"ya tsinkayi muryarta tana tambayarsa.
juyowa ya yi idonshi ya sauka cikin nata narkakkun idanun ta kafesa dashi tana kallonsa.
Komawa ya yi,ya zauna yana kallonta.
"Asmee dama kema matsoraciya ce!?".
"Ah ah naga zaka tafi ne ai to"
"Ke kuma bakya son in tafi?",sun kuyar da kanta ƙasa ta yi.
"Kina bukatar hutu ne za'a miki allura,za ki yi bacci ba'a son ki dinga magana sosai"gyada masa kai ta yi.
Yanda suke yiwa juna magana duk wanda ya kallesu ze yi tunanin sun daɗe da sanin juna,ko kuma akwai shakuwa sosai.
Se karfe goma ya bar dakin nata se da ya tabbatar da ta yi bacci kafin ya fito.yana kashe mata light.
Tana part din anty amarya idonta biyu ba tayi bacci ba tana jiran dawuwar LTG.
Anty amarya ma idanunta biyu,ita kanta jiran LTG takeyi ya dawo, saboda duk sanda ya fita ya yi dare ita da Ammi in ba sunji dawuwar sa ba tofa basa iya bacci.
Suna zaune tana ta koya mata wasu abubuwa.idanunsu biyu har sha biyu ya gota,nan ma shuru be dawo ba.
Wayarta ta dauka ta kira layinsa sede switch off.hakan yasa anty amarya ta dinga addu'a Allah de yasa lafiya.
Karfe 1:00 na dare motocin suka diro cikin gidan,anty amarya da Ammi da Abbie da suka kasance idon su biyu suna jiran dawuwar su sukayi hamdala.
Dama ya saba duk sanda ya yi dare ita yake kira a kawo masa coffee.
Suna zaune kira ya shigo wayarta ganin shine yasa ta daga.
"Anty amarya coffee please"haka kawai ya ce ya kashe wayar.
Miƙewa ta yi ta shiga kitchen din part dinta,cikin mintuna ƙalilan ta haɗa masa coffee, tunani ta fara zuwa ta tashi fatime ko kaltume,se kuma taga in ta yi haka kamar bata kyauta ba,duba da yanda suke yini suna aiki,dare ne kawai lokacin hutun su.
Kallon Sabriyah dake ɗale akan gado ta yi ta ce"sa hijabi ki zo ki nan"dogon hijab din da ta cire akan gadon ta dauka tasaka har ƙasa yazo mata.
Ba ta tray din coffee din ta yi,"ki kaiwa ya'yan ku Tajuddeen".
"To"har ta kai bakin kofa anty amarya ta ce"karki kuskura ki kirasa da wannan mugun da naji kike kiransa,ya Taj haka su Umaisha suke kiransa"gyada kai ta yi ta fita.
Knocking ta yi,ta ji shuru kusan five minutes tana tsaye can ta yanke shawarar shiga ciki kawai.
Ba kowa a bedroom din da alama yana wanka.
Ajiye coffee din ta yi akan Centre table.ta tsaya tana jiransa dan ta kudurci niyar tambayarsa ganin Asmita.
Idonta ne ya sauka akan wani ƙaramin hotonsa da Asrah a jiye akan bedside locker.
Nufan wajen ta yi tasa hannu ta dauki hoton kenan ta ji alamar mutum daf da ita.a tsorace ta juya,yana tsaye daf da ita distance din dake tsakanin su be fi taku biyu ba kwakkwaran motsi in ta yi jikinsu ze iya haɗuwa,ja da baya ta yi ta manne a jikin bango.
Dan ta tsorata da ganin yanayinsa na yau fuskarsa kamar wanda aka yiwa mutuwa,hannu na rawa ta ajiye hoton a inda ta dauka.
Yana sanye da rigar towel da ya rufe masa jiki kafafunsa ne kawai a waje.
Kallon hoton da ta ajiye ya yi kafin ya kalleta.
"Meye kike yi da wannan hoton!?"ya tambayeta yana matsowa kusa da ita.
"Ya Taj kawai na ji ina son gani ne"
Banzan kallo ya watsa mata kamar ze daketa.
"Fita ki bani guri".
Da sauri ta ce"to!to,ya Taj dan Allah inje in ga Asmita!?".
"Fita ki bani guri"ya sa'ke maimaita mata.
A maimakon ta fita din kamar yanda ya buƙata se ƙara tambayarsa da ta yi akan Asmita.
"Gobe za ki ganta"
Jiki a sanyaye ta ce "to".
"Kina da tabbacin za ki kai goben ne?"cikin rashin fahimta ta ce "bangane ba".
"Da kika ce to kawai,kina da tabbacin za ki kai gobene!?, Allah yakaimu ya kamata ki faɗa".
"Allah ya kaimu".
Ta juya da niyar fita a dakin hannunta ya rike.
Ya ja ta zuwa gaban mirror wani magani me kama da makilin na kashe raɗaɗi, ya bata,ya sa'ke jawo ta zuwa kan gado.
Umarni ya bata da ta hau ta zauna.
Tana dar_dar ta hau jikinta na ɗan rawa,yana ankare da ita,tsaki taja.
"Ubanme kike tunanin zan yi miki,da jikinki yake rawa haka"..
Ita de bata ce mishi komai ba.
Zama ya yi a gabanta ya juya mata baya.
Ita de ta rasa gane me yake kokarin aikatawa,zame rigar towel din jikinsa ya yi.
Zaro manyan idanunta waje ta yi gani ciwuka a bayan sa har waje biyu da alama da wuka aka ji masa su.
Jin bata fara masa komai bane ya ce"ki shafa min mana".
Hannunta na rawa ta matsa ta fara shafa masa kamar me tafiyan tsutsa,ita tsoro take ji karta fame mishi ciwo.
Tana tunanin to aina ya ji wannan ciwo haka.
Yau sun kama kuma sun kashe yan kungiyar Italian Mafia kusan mutane talatin a daji sun yi garkuwa da mutane rai bakwai se yan matan da suka kama,sun kai ashirin,da niyar yi musu fyade da kisan gilla su aikawa iyayensu.
Nan ne major Marry ta samu information akan inda suke shine ta turawa LTG,shine fitan da sukayi shida sojojin sa.
Sun kubutar da mutanen da yan kungiyar Italian Mafia suka kama gaba daya se yarinya daya da already sun yi mata fyade ta mutu.
Bayan sun kashe na kashewa ne sun kama na kamawa sun sa a mota,wani daga cikinsu batare da sun san dashi ba yazo da wuka ta baya da niyar ya kashe LTG, Allah be basa Sa'a ba,ya yanke sa s waje biyu.
Juyowa LTG ya yi ya damkesa,kamar wuyan kaza haka ya murde wuyan sa.
Hankalinta ya yi gaba wajen tunanin ta yanda ya ji ciwo ta taɓa wajen ciwon.
Sautin "ashhh" ya fitar saboda zafin da ya ji.
"Dan Allah ka yi hakuri Wallahi ba da gangan bane".
"Ki kashe ni kawai ki huta!,common shafa abu ne ba ki iya ba se wani shafe ni kike yi kamar wacce ta samu bayan kuliya".
Ya faɗa a faɗace.
Miƙewa ta yi,seda ta zo dede bakin kofa ta ce"tom sannu dama mutane irin ku ba'a musu gwaninta,gobe ko zakuna ne suka ji maka ciwo bazan taimaka maka ba".yi ya yi kamar ze miƙe ai kuwa ah million ta fice a part din.
Kwafa ya yi yaba bayanta da kallo "matsoraciya kawai".
Komawa part din anty amarya ta yi,ta samu ita take jira.bata tambayeta me ya rike taba.
"Kije ki kwanta dare ya yi".
"Seda safe mommy"ta faɗa tana daukar wayarta ta shiga daki na kusa dana anty amarya.key ta murza ta je kasan katifa da ta boye takardar tafito dashi.
Loda number jikin ta yi a wayarta,cikin uku ya yi aka dauka.
"Hello waye ne".
Muryar mutumin daya fara taimakon rayuwarsu ta ji ya sauka a kunnenta,da alamun kuka yake yi.
"My Sabriyah na yi kewarki sosai"hawaye ne ta ji ya taru a idonta.
Under her breath ta iya furta.
"Fu'ad!, da gaske kaine?".
"Ni ne my Sabriyah,ashe zan sake jin muryarki kafin in mutu na dauka se a lahira zamu haɗu,ina Asmita, na yi matukar kewarku"ya faɗa yana kuka.
Ita ma yanda taji yana kuka ne yasa ta fashe da kuka.
"Fu'ad kana ina ne,meye abinda ya faru dakai bayan rabuwar mu,"sune tambayoyin da ta masa.
Sa'ke fashewa da kuka ya yi "my Sabriyah, rayuwata tana cikin halin ha'ulayi.ina cikin masifa.wannan sojan da ya ɗauke ki ne ya kamani ya daureni kullum se an min azaba daban daban,abinda baki sani ba shine yasa aka dauke Asmita saboda yana son wannan memory nan a wajenta.ni kuma ya kashe min mamana da babana dan kawai ya nemi in faɗa masa in da ze same ku ni kuma naki.wannan dalilin yasa ya kashe min kowa nawa ni kuma ya min azaba wanda se da na rokesa da ya kasheni kawai".
Komai ji ta yi ya tsaya mata cak gumi ya fara yanko mata, al'ajabi ya hanata magana,taya hakan ze faru ashe duk tashin hankalin da ta shiga akan Asmita da Fu'ad dama LTG ne ya sace su?,dama abinda yake kullawa kenan,. wannan tambayoyin ta dinga yiwa kanta.
Nan take taji wani irin zazzafar ƙiyayyar lieutenant general Tajuddeen ya mamaye cikin zuciyarta,inda za'a bata wuka ko bindiga a ce ta kashe mutumin da ta tsana yanzu to shine wanda zata aika lahira.
Ganin ta yi shuru ne yasa ya fahimci cewa,ta faɗa tarkonsa,domin ya yi imani da taimakon Sabriyah ze samu damar kashe LTG, muddin in bega bayansa ba tofa babu yanda za'a yi shirin su ya yu, saboda barnan da ya masa yau bana wasa bane,ya kashe masa mutane sosai.
Cikin sheshekar kuka ya ce "my Sabriyah kina jina kuwa?".
"Ina jinka Fu'ad, kawai na ka sa yardan wai ya Taj ze iya aikata hakan ne".
"Sabriyah karki manta mugu bashi da kama,ze iya canza fuska duk yanda ya gadama".
"Hakane kam, Wallahi natsane shi,ban taɓa kawo ze aikata min haka ba".
Murmushi ya yi"yanzu kinsan taimakon da nakeso kimin".
Kamar yana gabanta ta girgiza mishi kai.
"Da taimakon ki zamu ka re mutane da yawa daga muguntarsa.dole ne mun yi hanyar da za'a kamashi yaje ya girbi abinda ya shuka.duk wani motsinsa ina so