Showing 75001 words to 78000 words out of 94974 words

Chapter 26 - ASHE ZAMUGA JUNA COMPLET BY MRS ISHAM.txt

28 Dec 2024

8669

( Yar lelen Jarumai)








*THE WRITER OF 🖋️*
*NIDA PATIENT DINA*




~And now~
*🌹ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*






📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️




__________________________________
Page 25&26




"Saghar kai ta part dina,kafin a gama shirin yi mata aikin"dagata ya yi cak i zuwa part Hajiya babba din,bin bayansu Sabriyah take kokarin yi,ta ji muryan Ammi na cewa"karki damu ze dubata"ba don ta so ba haka ta tsaya,murna ya koma ciki,da ta ga Asmita ta farfaɗo ta yi tunanin matsalar su yazo karshe,yanzu ga maganar aikin da za'a mata.
Rike hannunta anty amarya ta yi suka tafi part dinta.
Kiran asibitin ya yi ya sanar dasu da komai ya zama cikin shiri zasu zo dan gabatar da aiki.


Dawuwa falon Saghar ya yi bayan ya kai ta part din Hajiya babba kamar yanda ta umarce shi da ya yi.


"Uncle yau ne za'a mata aikin!?"cewar Dawood,"eh yau ne yanzu ma kuwa,ku fara yin gaba da ita banason Sabriyah ta fito ta samu baku tafi ba,dan zata ce dole se ta bi mu,so you have to hurry"a tausashe Dawood ya sa'ke cewa" Saghar ku tashi muje" "Ammi ba se kunzo ku ba, duk ku zauna a gida daga zaran aiki ya yi kyau an kammala lafiya se mu sanar daku,ku zo ku duba ta,in ba haka ba in Sabriyah ta fito taga bakwa nan zata fara zargin wani abu dan yanzu haka ma jikinta ya yi sanyi"uncle Hameed ya yi maganar yana miƙewa,ya fice a cikin Mansion.


Wannan karon Hajiya babba da Ammi ne suka fito da Asmita a ka sa ta a motar.su kuma suka wuce asibiti.koma wa ciki sukayi suna addu'a Allah yasa aiki ya yi kyau.


Yana part dinsa,system ne a gaban shi yana video call da general cikin turancin da ya zauna a bakin shi kamar yarensa,ya ke sanar da general ya samu memory sede ba ya son kowa ya ji abinda ake ciki har se an kammala operation din da suke yi na kama Italian Mafia,domin ya gano kan cewa akwai munafiki a cikin su yana sanar da shugaban Italian Mafia duk wani motsin su.jinjina masa general ya yi ya kuma dau masa alkawarin baze sanar da kowa abinda ya ke faruwa ba.


Shigowa major Marry ta yi ta zauna a kan kujerar dake facing dinsa hannunta sanye cikin jakan da ake sa hannu in an samu wani rauni, sosai ta samu lafiya hannun ne kawai ya rage ta yi recovery.


"LTG i heard that, you have the memory with you!?" ..
"Yes!how are you feeling now?",ya tambayeta yana rufe system din.
"Am quite well buh I have important information to share with you"kallon ta ya yi alamar go ahead.
"i already sent it to you through your email"




Duba wayarsa ya yi kafin ya ɗago ya kalle ta.
"Are you sure this information isn't wrong!?"
"Am hundred percent sure LTG"


Umarnin tafiya ya bata, sannan ya tashi ya yi wanka, ya sa uniform.
yana saka takalmin sa ne Khalifa ya shigo,nan LTG ya sanar dashi da su shirya zasu shiga daji operation,sara mishi ya yi kafin ya fita da sauri nan take ya sanar wa sojojin dake gidan,shiryawa sukayi cikin ka'kin uniform din sojoji,ko wanne ka gani da bindiga a jikinsa,ga motocin da ke fake yana jiransu dan fita daji.




Suna shiga part din, anty amarya tasa ta ta yi wanka a toilet dinta,ta fito mata da riga da skirt na Atamfa super wax ya sha dinki ya yi kyau sosai, tunda telan ta ya kawo mata su ta fahimci kayan baze shigeta ba yasa bata sake bi ta kansu ba se yau din nan.ajiye su ta yi akan gado.


Fitowa ta yi daga wankan sanye da dogon hijab din da anty amarya ta bata ta saka, towel na daure a ta ciki.bakaramin kyau hajab din ya mata ba, kyakyawar fuskarta ya fito ya yi kyau.


"Anty amarya na fito ina mai in shafa"ɓata fuska anty amarya ta yi, daga gani bata ji dadin sunan da Sabriyah ta kira ta dashi ba hakan ya sa ta, cewa "Sabriyah ba ki dauke ni a matsayin uwa bane yasa ba ki kirani da mommy ko mama ba!?"cikin jin kunya ta ce "kiyi hakuri mommy bazan ƙara ba" "yawwa daughter na!,hijab din nan ya Miki kyau sosai"murmushi kawai ta yi,ita saukin kan anty amarya da rahanta yana burgeta har cikin rai takejinta kamar ita ce mahaifiyarta saboda yanda take nuna mata soyayya.


Zaunar da ita ta yi akan kujera gaban mirror ta shafa mai kafin anty amarya ta mata light make up ,ta bata kayan ta ce ta je ta saka a cikin dress room.


Kallon kayan ta yi tana tunanin ta ina zata fara sakawa,ita sam ba ta taɓa saka irin wannan kayan ba,daga riga da wando se riga,sune kadai iya kayan da take sawa,yanke shawara ta yi ta dauki skirt ta fara sawa,kayan tab ya kamata Kamar telan da ya dinka ya gwada ta, ta sa rigar.masha Allah ita kanta seda ta ji sauyi a jikinta,gaban madubin da ke cikin dressing room din taje ta tsaya tana kallon kanta,seda ta ja baya tana mamakin kanta,gani take yi kamar ba ita ba gaba daya kayan sauya mata kamani ya yi, tsananin kyaun da kayan ya mata ya sa ta fara juyawa tana karewa kanta kallo kamar ba ita ba,gashinta dake zube a bayanta ta fara kokarin daure su waje daya,dakyar ta iya daurewa,ta dau dankwalin kayan ta fito,tun da anty amarya ta daura idonta akan Sabriyah ta gagara daukewa kallon fuskar yar karamar ƴarta da ta rabu da ita take yi a fuskarta, fuskar Asrah take gani lokacin da tana karama a fuskarta,ta kasa janye idonta akanta bata ma san ta iso kusa da ita ba tana mata magana amma ina hankalinta ya yi nisa.


"Mommy ki daura mini dankwalin ban iya ba"shiru anty amarya ta yi tana kallonta, taɓa hannunta ta yi tana sa'ke cewa"mommy ki daura min"se sannan ne ta dawo tunaninta,da sauri ta ce"sure kawo in daura miki "miƙa mata ta yi batare da ta yi tunanin komai a ranta ba.


Daurin dankwali me kyau ta mata ta saka mata sarka da ɗan kunnen gold me kyau simple design,ji ta yi kayan yana muskulinta tasa hannu zata dan ja zip kasa kadan,rike hannunta ta yi tana tambayarta "meye zakiyi haka"shagwabe fuska ta yi da iya gaskiyarta ta ce "mommy Wallahi muskulina yakeyi"dama ta yi tunanin za'a yi haka duba da babu irin wannan kayan a rayuwarsu bama su taba sawa ba.
"Karki cire ki daure kidinga sakawa a s haka zaki saɓa,ke bakiga yanda kika yi kyau a cikin kayan bane,kamar wata amarya"tsadadden murmushinta dake ƙara mata kyau ta sakarwa anty amarya"mommy dagaske na yi kyau sosai!?"ta tambayeta with excited face,kai ta gyada mata alamar ta yi kyau sosai,itama da murmushi akan fuskarta nan ne dimples dinta suka bayyana,dan yatsa ta saka a ciki ta taɓa kamar wata karamar yarinya ta langwabar da kanta gefe tana kallon kyakyawar fuskarta anty amarya da za'a iya cewa photo copy dinta ce.
"Laaah mommy kema kina da dimple guda biyu iri daya da nawa,kuma ma a waje daya suke"hararan wasa ta mata"ke dama baki taɓa gani bane se yau".
"Allah ban taba lura ba,se yau.mommy kin san meye!?"girgiza kai ta yi kawai ba ta ce komai ba.
"Mommy ke kyakyawa ce sosai ko fa murmushi kikayi se kin ƙara kyau,kalli idanunki Wallahi kamar akwai wani abu kamar man gyada_man gyada a cikin su"rike haba ta yi tana kallon Sabriyah da mamakin ta,kenan itama surutacciya ce rashin sabo da kuma rashin wanda zaka zauna ka sa'ke dashi har ka ta yi masa surutun ne ta rasa shisa a ke mata kallon bata wani magana sosai.
Yanzu da ta samu anty amarya kuma ta dauketa tamkar uwa shisa take ta mata surutu.kuma ita ta ji dadin hakan sosai yanda ta ji free da ita babu wani shuru_shuru ko kuma wani kunya,ta fito tana ta mata surutu da shagwaba hankalinta kwance.
Tunawa ta yi da Asrah,duk lokacin da ta yi kwalliya se ta shafa fuskarta ta ce "mommy kinyi kyau sosai, you're so beautiful mom".


Ruko hannun Sabriyah ta yi "Tom Nagode babyn mommy, yanzu kije palour,in kije ki gaishesu daya bayan daya bawai yanda kika saba yi ba"gyada kai ta yi ta mike da niyar tafiya.
"Sabriyah zo nan"dawuwa ta yi,ta tsaya,dauko gyalen shantali ta yi ta yafa ma,akai.


Fita ta yi a part din ta nufo main part da tabar su.
A hankali take taka stairs da takalmi me madaidaicin tudu,kamar wata hawainiya take tafiya kai kace tsoron taka kasan takeyi,ita kuma ji takeyi in ta yi tafiya da sauri to skirt dinta ze rabe gida biyu duk da kamatan da ya yi ba sosai bane kawai rashin sabo da irin kayan ne yasa takejin wannan sabon a al'amarin.
Jin ƙaran takun takalmi ne yasa suka maida idon su wajen dan ganin waye haka.
In badan sun santa ba to babu abinda ze hanasu cewa wata shuwa arab mix with Hausa ce,yanda ta atamfar ya yi fitting din jikinta se ya zamana kamar tun asali shine suturanta.
Saukowa downstairs ta yi idanunsu duk a kanta musamman su Umaisha da su Ashman,kallonta suke yi babu ko kyaftawa.
Yanda anty amarya ta sanar ita hakan ta yi wajen Abbie ta fara zuwa ta gaisheshi.
"Abbie ina wuni!?".
"Lafiya klau Sabriyah,ya mommy ki!?".
A hankali ta ce
"Mommy na lafiya"
Ta je wajen Abbu shima ta gaisheshi.
"Abbu in wuni!?".
"Lafiya klau alhmdllh yarinyar kirki"
A marairace Jaleelah ta ce "Abbu mu ba yaran kirki bane!?".
Gwalo Sabriyah ta musu
"Eh din,kun ji haushi ne?"
Hararan wasa Rameesa ta mata ta mike ta dawo wajen abbu ta zauna cikin shagwaba ta ce
"Abbu mu ma ai yaran kirki ne ai ko?".
Dariya abin na su yaba kowa wai kishi suke yi,gyada kai Abbu ya yi kafin ya samu damar cewa
"Dukkan ku yaran kirki dan Allah ku barni haka"sa'ke kwashewa da dariya sukayi harda Sabriyah dake tsaye kusa da Ammi.
Seda ta gaisar da duk wa'yanda suka girmeta a falon,kafin ta lura akwai wa'yanda basa nan. Hajjatiye ma ba ta nan, uncle Hameed, saghar, Dawood,sun tafi da Asmita asibiti.se kuma LTG da tun lokacin da ya tashi be sa'ke dawuwa ba.


Jan hannun Parsa ta yi tana"masoyiya zo muje ki rakani part din Hajiya babba in ga my Jerry"ta kira Parsa da masoyiya kamar yanda ta ji kowa na gidan yana kiranta.


Kame_kame suka fara mata sun rasa ta wani hanya ne zasu hanata zuwa part din Hajiya babba.
Abbie ya ce "Sabriyah bari in ta tashi daga bacci se kije gudun kar ki tasheta"
Murmushi ta yi,cikin farin cikin da bata taba tsintar kanta a ciki ba ta ce "Abbie ka yarda dani,ko motsi na bazata ji, kallonta kawai zan yi in fito".
Ta faɗa tana kuma jan hannun Parsa din.
"Sabriyah bazaki samu ganinta yanzu ba"Sahil ya faɗa yana kallon su.
Kallon tuhuma ta fara binsu dashi jikinta ne ya fara bata akwai wani abu da suke boye mata.
Slowly ta ce "meyasa ka faɗi haka ya Sahil akwai abinda kuke boye mini ne!?"ta tambayashi tana kallon su gaba daya.


Daga bayanta ta ji muryarsa yana faɗin.
"Bazaki samu ganinta yanzu ba kamar yanda Sahil ya faɗa miki saboda yanzu keda su anty Sameera zaku fita siyayya ita kuma Asmita,ba ta tashi ba tukun nan bana son musu"ta kasan ido take watsa mishi harara,yana sanye cikin ka'kin uniform dinsa da ya sake fito zallan madaran kyawunsa.


Sarai ya ga hararan da ta yi mishi amma dake yana da important issues da yakamata ya yi clearing dinsu ya sa be bi ta kanta ba,saboda yasan tunda ya ce bazata shiga ba to,babu yanda za'a yi ta shiga sede in taurin kan nata yana kusa.komawa sukayi daga ita har Parsa suka zauna.shi ma zaman ya yi akan kujerar dake facing na Abbie.
Ganin shi cikin uniform ne yasa Hajiya babba cewa"Tajuddeen ina zuwa haka".
"Zamu je wani dan karamin aiki ne".
Ta ce "Allah ya taimaka"ya amsa mata da"Ameen".
Kallon Ammi ya yi yaga idonta na kansa.
"Ammi zan fita".
"Allah ya taimaka yabaka nasara".
Har cikin ransa ya ji dadin wannan addu'ar da Ammin sa ta mishi,.ya amsa da"Ameen".


Kallon yan matan anty Sameera ta yi ta ce" to maza duk ku tashi muje a yi shopping,Sahil da Sudais ku tashi muje ku zaku kaimu".


Hajjatiye da fitowarta kenan ta ji tattaunawar da suke yi ta ce"kayya! dan Allah kwashesu kaf ki tafi dasu ni dama sun isheni,gwara su je su dede ta kansu a yi tuwona mai na".


Yar dariya kowa ya yi, Sahil ya ce"Tabb waya gaya miki Hajjatiye ni zan yi auren gida!?,ai ina da budurwata a kano to kuma me ze sanya ni in yi auren gida ". "Ah ah babu kam se ka kawo mana ita ai mu ganta"cewar Hajiya babba tana dariya domin duk sun fahimci ya yi hakan ne dan raha.


Tunda ya furta wannan maganar murmushi da walwalar dake kan fuskar Parsa ya dauke cak, idanunta suka cika da hawaye,zufa ya fara tsatssafowa wuyanta da goshinta, sunkuyar da kanta kasa ta yi bata san kowa ya fahimci halin da take ciki.ji tayi komai ya dena mata dad'i,kenan dama duk dakon soyayyan ya'yan nata da ta jima tana yi yana da budurwa ba ta sani ba?,duk da tasan ita kadai take san shi,be ma san tana yi ba shi kallon kanwa ya keyi mata,kuma babu wanda ya fahimci hakan a gaba daya ilahirin gidan se Salim,shine ya fahimci ta fadawa soyayyan dan uwanshi amma ko da ya fahimci hakan be sa ya nuna mata kan cewa yasan wani abu ba.


A duk lokacin da ta yanke shawarar taje ta samesa ta sanar dashi irin son da take mishi ko da Allah ze sa ta samu waje a cikin zuciyarsa,amma kunya da gwarjinin da yake mata se ya hanata tabuka komai.ga shi yau kunnenta ya jiyo mata abinda bata taɓa tunanin jin sa ba a wajensa,ashe ita haukanta kawai take yi.(hmmmm,ni ko nace matsalar soyayyar bari daya kenan ".


Salim da ya lura da yanda mood dinta ya sauya ne yasa ya ji wani iri a ransa, yarinyar da babu wanda ze ce ya taba ganinta a cikin wannan ɓacin ran,ko da yaushe murmushi dauke akan fuskarta se gashi yau ta kan abinda ya kasance ba gaskiya ba,ta shiga wani yanayi,yanke shawara ya yi ze samu Sahil din ya sanar da shi Parsa na matukar kaunar domin shi yafi kowa sanin babu wata mace a cikin rayuwa Sahil kawai yanxu ma ya faɗa ne saboda rashin sani da kuma raha.




LTG dake jin hiran na su ne ya ɗan yi tsaki,shi gani yake yi ja musu reni za'a a wajen wa'yannan kananun yaran.


"Ku tashi mu tafi ko,kar yamma ya yi, Sakeena zakije ne!?"ta tambayi anty sakeena dake magana da Hajjatiye,se kus_kus suke yi.
"No sekun dawo kawai"
Ta faɗa mata haka sannan suka ci gaba da maganar su.


"To Allah ya tsare ya kuma kare ku da karewarsa"can kasan makoshi ya amsa addu'ar da Abbie ya musu sannan ya mike ya fice,yana fitowa yaga rundunar sojojin sa shi kadai suke jira,duk a tare suka sara masa gyada musu kai ya yi Khalifa ya buɗe mishi ya shiga yana kokarin rufe motar major Marry ta fito ita ma cikin shirinta tana sanye da uniform.
Dasauri ta iso tana kokarin shiga.


Kallon ta ya yi irin kallon me kike kokarin yi din nan.
Ta fahimci abinda yake nufi hakan yasa ta ce "Please LTG I want go along with you".
Cikin harshen turanci ya ce mata bazata je ko ina ba,se jikinta ya gama yin sauki.
Babu yanda ta iya tunda bazata tsaya jayayya da lieutenant general ba uban gidanta.
Ta na ganin su suka fita a gidan ko kadan ba ta ji dadi ba,raunin hannunta nan ne ya kwafsa mata saboda tana son ta ganta a bottle field ana fafatawa da ita.


Komawa ciki ta yi babu yanda ta iya haka take ta kwanta.


Fitowa packing space sukayi, Jawan, Sudais, Sahil suka fito da motocin su dan kai su kasuwa.
Jaleelah ce ta yi hanzarin zama a gaban motar tana murguɗawa Iftisan baƙi.
Kallonta Jawan ya yi,ya kuma ga hararan da Iftisan take yi mata.
"In kin gama neman tsokanar seki fito min a motar"tura baƙi ta yi can kasa _kasa ta ce "baza'a fito din ba".
"Rike kugu Jawan ya yi yana mamaki wato wannan rashin kunyan da ya sansu da shi musamman ma ita Jaleelah da tafi Iftisan sangarcewa yana nan.


Hannu yasa ya buge bakinta.kuka tasa ka tana kama bakinta, karasowa bakin motar anty Sameera ta yi jin kukan Jaleelah,kallon Jawan da kukan nata ko ajikinshi ta yi ta ce "meye kayi mata Jawan!?".
"Zagina ta yi shine na buge bakin"ya bata amsa yana yiwa Umaisha alamar ta zo da hannu.
Cikin kuka ta ce "Wallahi anty Sameera ni ban zage shi ba sharri ya min"hannu yasa ze sa'ke buge bakin anty Sameera ta yi saurin rikesa.
"Yi hakuri,kidena kukan.kai kuma Jawan ka kyaleta please".
Bude murfin motar ta yi ta ce "kuma,ma na fasa tafiyan".
Galla mata harara ya yi,ta shige da gudu tana kuka.
Dariya Iftisan ta yi taji dadin yanda Jawan ya yiwa bakin rashin kunyar Jaleelah.
Sabriyah motar Jawan ta shiga ita da anty Sameera da kuma Iftisan din.
Yayinda Umaisha,Zoya, Rameesa suka shiga motar Sudais.
Baya Iklas ta shiga,Parsa dake tsaye a bakin motar bata ma da niyar shiga,fuska a ɗan haɗe.
Kallonta Sahil ya yi "masoyiya zo shigo Mu tafi".
Maƙe kafada ta yi, ta ce "Iklas ki dawo gaba ni abaya zan zauna"with full surprise a fuskarsa yake kallonta,gani ya yi Kamar ba Masoyiya Parsa ba,da duk lokacin da zasu fita inde har dashi tofa tana gaban motar amma yau ita ce take yin tayin zaman gaban motar.
"Yau kuma!,nikam get in don't waste my time"sa'ke maƙe masa kafada ta yi a karo na biyu.
Da ya fuskanci dagaske ta ke ne yasa ya haɗa rai ya daka mata tsawa da yasa ta shige babu shiri.
"Za ki wuce ki shigo ne ko sena shigo dake da kaina!"zama ta yi fuskarta babu walwala,shima da yaga yanda ta yi kicin_kicin da rai ne yasa shima be bi ta kanta ba,duk da yana mamakin meye haka ya samu Parsa da yau ya ganta a haka.
Shi da Iklas ne suke ta hiransu,ita kam ko tari bata yi ba tunda ta shiga motar.


A motar Sudais ma su na nan suna ta surutu gaba daya sun cika wa Sudais kunne, musamman Umaisha an fi jin muryarta.
Juyowa da kansa ya yi ya watsa musu harara,ai babu shiri duk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login