Showing 69001 words to 72000 words out of 94974 words

Chapter 24 - ASHE ZAMUGA JUNA COMPLET BY MRS ISHAM.txt

28 Dec 2024

8668

sukaji tana musu magana ."Sabriyah kuzo ku nan dama ku nake nema"karasawa wajenta sukayi ,kallon Asmita Ammi ta yi kafin ta maida kallon ta kan Sabriyah "tun dazun!,su Rameesa suke neman ku,Abbie yabada naku tsaraban abaku,ki dena yawo da wannan kayan sun matse miki jiki sosai Zoya ta faɗa mini cewa duk kayan da aka kai miki rage su kikeyi.nasan baki saba sa irin wa'yannan kayan ba amma ki daure ki dinga sawa ke macece,mace kuma an santa da kamun kai da kunya ,suturta jikinta"shuru Sabriyah ta yi,jikinta ya yi sanyi ba'a taba tsayar da ita an faɗa mata haka ba.


Murmushi karfin hali ta yi wanda kana gani kasan cewa be kai zuciya ba"Ammi!,na taso ne a inda babu me ce mini dede nakeyi ko kuma akasin haka, wa'yannan kaya masu nauyi kuma ban saba da su ba bana iya samun nutsuwa a cikinsu.Ammi yanda nake rayuwata bazance inajin dad'i ba kuma ba zance banajin dad'i ba".sosai Ammi take kallon idon Sabriyah domin iya gaskiyar ta take gani, tabbas an yiwa rayuwar yaran nan illa me muni ma kuwa.


"Bakomai Nasan in kina tare damu duk za ki saɓa da hakan"gyada kai kawai ta yi,ta ja hannun Asmita dake wasa da flowers din kan table.da tun tsayawar da Sabriyah ta yi wajen Ammi ita kuma ta tsuguna ta fara wasanta.




Suna haurawa stairs Asmita ta ce "my Tom" "uhmm"
"Ni banga me kyau ba ina yaje,nayi lilo shi be yi ba"bata amsa mata ba, suna ci gaba da tafiya ne ta ce"yau yana aiyuka sosai,ba zaki samu ganinsa ba"bata rai ta yi da alamu bata ji dadin maganar Sabriyah ba,ita tana son ganin me kyau suje su yi lilo kuma ya bata chocolate.
Har suka shiga daki bata sake magana ba se da Sabriyah ta ce "my Jerry ki dena fita batare da nasani ba,kina tsorata ni in naga bakya nan,kinji ko"gyada mata kai ta yi alamar "to".


Wanka ta shiga tayi yau duk bata samu ta sake yin wani wankan ba,tun na safe da ta yi ga shi yanzu har yamma ya yi.


Bayan ta fito daga wanka ta bude wardrobe din kayan kallon kayan da aka saka musu, ita da Asmita zuba musu ido ta yi tana tunanin wanne zata ɗauka,ga maganar Ammi da taji yana mata yawo a tsakar ka.


Runtse ido ta yi tasa hannu ta dauko wando falazo da riga.sakawa ta yi ta gyara gashinta kawai ko mai bata shafa ba.


Hawa gadon ta yi wajen Asmita da ta kwanta kamar me bacci amma idon ta biyu ta zubawa bango ido.
"My Jerry tashi kiyi wanka"maƙe kafada ta yi,"yi hakuri shalelena tashi kiyi wanka kinga dare ya kusan yi, sa'ke make kafadar ta yi.
Dafa goshi ta yi"haba my Tom ki tashi mana meyasa kike da taurin kai ne ?,"da karfi ta ce"banason wankan banaso "ta yi maganar tana bubbuga ƙafafunta akan gado,tuna maganar da Saghar ya gaya mata yasa ta kyaleta domin ya ce bata da buƙatar a dinga takura mata, lallabata yakamata a dinga yi.






Ya Abbas suna falon Abbie ana hira, matansu kuma suna wajen su Ammi suma.


"Tajuddeen be san mun dawo bane?"Abbie ya tambayi Sudais dake zaune kusa dashi.
"Ehh gaskiya ba lallai ne yasan kun dawo ba"ya basa amsa.
"Shikenan ni zanje ai in same shi".
Se da aka kira sunan Tajuddeen ne ma Saghar ya tuna da ya sanar dashi cewa yana son ganin sa da, Sudais da kuma Jawan.


Taɓa Jawan ya yi "kaga na manta ko, LTG ya ce yana son magana da mu, da ya Sudais".
"Shikenan se dare se muje "cewar Sudais.
Abbie yana matukar son ganin Tajuddeen se zuba ido yake yi ko ze zo amma shuru babu ko alamar sa,ana hirar ma shuru kawai ya yi burinsa kawai yaga Tajuddeen yazo masa sannu da zuwa ya rungumesa,amma tunda yaga har zuwa yanzu be zo ba tofa baze zo din ba.


"Yawwa nikam Hameed yarinyar waye naganku tare dazun!?"Abbu da ya kasa hakuri ya sa'ke tambayar uncle Hameed.
"Ita ce wannan yarinyar da Tajuddeen ya kawota gidan nan yana bincike akanta".
"Ikon Allah, lokacin da kuka tsaya tare se tayi kamar ƴarka"abbu sake faɗa domin shi yaga kamar Sabriyah da uncle Hameed.
Dariya kawai suka yi. Saghar da ya manta da allurar Asmita da zeje ya mata, seda a ka kira sunan Sabriyah ne ya tuna da ze mata allura.
Gyaran murya Abbie ya yi sannan ya soma magana "gobe Hajjatiye zata zo,kun san Allah wanin ku ya kuskura ya ɓatawa uwarmu rai tofa ba babu ruwana da girman da kukayi jikin ku ze baku labarin shekaru sha daya da yawuce tam"yar darawa sukayi, Ahmed ya ce"duk sanda Hajjatiye zata zo se anyi mana warning yanzu fa mun girma yakamata a dena maimaita mana Abbie ".
Cikin harshen shuwa abbu yace"da yafi muku".
Yaron ya Hafiz ne ya shigo dan shekara biyar hannunsa rike da bindigar wasa,ya zauna a kusa da Abbie"ah ah Ameer kar de mu za'a harbe da bindigar nan"Abbie ya tambaye sa cikin wasa, maganar cike da gwaranci irin na yara ya ce "nooo!terrost za'a halbe ko kaka"dukkansu dariya sukayi,"naga alama babanninka Tajuddeen ko Sudais ko kuma Jawan zaka ga'do "uncle Hameed ya faɗa yana shafo kan Ameer dake wasa shi da bindiga.


Sosai suka sha hira,ganin har lokacin LTG be shigo bane yasa Sudais ya kirasa,3missed calls ya mishi amma beyi picking ba daga karshe ya turo mishi da text,bude sakon da LTG ya turo masa ya yi.
"Bro!call you back,am in important meeting right now can't talk".
Murmushi Sudais ya yi,shi dama yasan zeyi wuya in LTG na gidan.
Shima ya rubuta mishi message kamar haka.
"Okay,Kayi sauri ka dawo Abbie is eager to see you".
Har bayan 5mint bayi mishi reply,yasan yaga message din.
"Abbie LTG baya gida yana meeting shisa ka ji shi shuru"Sudais ya faɗa masa,se yanxu yaji sanyi a ranshi,domin tunda suka dawo yakeson ganin sa it has been a while rabon da ya gansa.




"Ammi Tajuddeen fa tunda nazo ban ganshi ba"Anty Sameera ta tambaya,anty sakeena dake sawa karamin ɗanta pampas ta ce"Nima abinda nakeson tambaya kenan,ko baya nan ne" "ehh ya fita,nikam bazaku koma gidajenku bane dare fa yanayi"Ammi ta tambayesu ,tana bin ko wacce su da kallo dariya Anty amarya ta yi "haba Ammi yakike korasu ne"hararanta ta yi ta ce "to ai naga dare ya fara ne ai,kuma banga alamar zasu tafi ba, ko kuna nufin haka zaku bar mazajen naku su kadai a gida!?", marairace mata suka yi "ayyah Ammi dan Allah ki bar mu mu kwana, Wallahi seda muka sanar musu zamu kwana kafin muka taho kuma sun yarda"cewar anty sakeena.
"Se kuma kuyi ai,yanzu nan ko wacce ta shirya ta wuce gidanta,babu wacce zata kwana",Hajiya babba tana zaune tana jinsu bata sa musu baki ba.
"Ammi kiyi hakuri ki barsu tunda sun tambayi mazajen nasu,kuma kinga Hajjatiye da Rumanatu duk gobe zasu zo,su Abbas ma duk anan zasu kwana"anty amarya ta roki alfarma..
"Shikenan Allah yakaimu "suka amsa da Amin.




Yau su Umaisha ana wajen Abbie da Abbu,a wajensu suka tare se surutu suke musu,rabonsu da part dinsu tun karfe biyu basu sake komawa ba.


Sabriyah bata sake jin d'uriyarsu ba,kuma hakan be dame ta ba,tana tare da Asmita suna ta shirmensu, knocking aka yi ta ce "a shigo".
Saghar ne ya shigo hannunsa rike da kwalin chocolate din da yace ze bada a kawowa Asmita ya manta.
Tana jin muryar sa ta mike ta tsaya akan gadon tana ihun"me kyau!me kyau!me kyau"murmushi ya mata,tana daga kan katifa ta rungumoshi a jikinta kamar wani ɗanta,wani shock ya ji tundaga tafin ƙafar sa har cikin kwakwalwarsa da sauri ya raba jikinsa da nata beyi taba kawo tsammanin zata rungumesa ba.
Tura masa baki ta yi"me kyau na hau lilo babu kai"se ta nutsuwarsa ya yi kafin ya ja hannunta ya kaita gaban mirror ta zauna Sabriyah na zaune tana kallonsu,komawa ya yi wajen da ya ajiye kwalin ya bude ya fito mata da chocolate ya kawo.
Buɗe mata chocolate din ya yi,yabata raba chocolate din gida biyu ta yi tabashi rabin girgiza mata kai ya yi alamar bazesha ba.
Fara sha ta yi idonta akanshi,kawar da kansa ya yi, ya haɗa allurar ya mata cikin dabara,se da ya gama ze tafi tukun ta ce baze tafi ba se yasha chocolate din,karba ya yi gudun kar tayi kuka,yasha ya ce "shikenan!?", "Ehh".


Sabriyah ta ce "my Jerry ni baza'a ban chocolate din ba?",sake raba chocolate din ta yi tasa mata abaki.


Fita Saghar ya yi adakin yana dariya.abincin darensu Fatime ta kawo musu fuska a sa'ke suka gaisa.




Bude kofar bedroom din ya yi yaje ya zauna akan gadon Abbie yana jiransa,daga wanka ya fito beyi tunanin zega mutum a ciki ba,da mamaki yake kallon LTG dake zaune akan gadonsa.


Miƙewa ya yi yaje ya rungume Abbie yana faɗin "i missed you so much Abbie" "nayi missing dinka nima sojana "zama sukayi akan gado.
"Nayi tunanin bazaka zo ka ga Abbie dinka ba"LTG ya ce"nope ina meeting ne sorry for the delay".
"Is okay ya aiki,banyi zanton dawuwanka nan kusa ba se gashi ka dawo, amma Jawan ya sanar min bincike ne ya dawo dakai", gyadawa Abbie kai ya yi.
Sun bata kusan two hours tare suna hira,kafin ya yiwa Abbie se da safe.


Yana shiga part din sa ya tarar da Jawan, Saghar, Sudais suna jiransa.
"Very good guys,na ɗauka baku zo ba ai"ya faɗa yana wucewa dakin binciken,bin bayansa sukayi ciki suna shiga kofar ya rufe.


Suna zaune suna kallonsa ya fito da memory card din ya jona a babban system, connecting ya yi sannan ya dawo ya zauna suka fara kallo.


Fuska Barrister Lameer ne ya fara bayyana ajikin video din.yana magana murya kasa_kasa da alamu yana tsoron kar wani ya ji shine.


"Sunana Barrister Lameer muktar.ni mazaunin garin Kano ne,na samu sakon sirrine kan cewa wasu mugaye kuma hatsabibai yan ta'adda sun shigo kasar Nigeriya,wanda kasashen waje ma basu iya kawo karshen ta'adda cin su ba.sun shigo Nigeria ne da nufin kashe rayuwaka masu dimbin yawa.
Wannan dalilin yasa nasa rayuwata a cikin hatsari domin haɗa bayanai akansu nasan ba lallai in rayu ba,rayuwata dakyar ne in zan iya fita daga sharrinsu amma Allah ya fisu".
Yana gama wannan jawabin duhu ya bayyana akan screen din,duk shuru sukayi hankalinsu yana kan screen din, musamman LTG yana son yaga abinda suke shiryawa.


Mutane ne kusan su goma sha biyar zazzaune akan kujera ga tarin makamai,da bindigu,a gaban su ba iya bakaken fata bane harda turawa a cikin su.
Ogan dake zaune akan kujerar tsakiya fuskansa na sanye da mask baki irin wanda barayi suke sawa,in zasu je fashi.


Magana ya fara da turanci"babban abinda nake muradi shine zubar jini,ko da wasa wani acikin ku ya bata mana aikin da mukayi watanni goma muna shiryawa to dashi da familynsa makomarsu lahira ne,asibitoci guda ashirin ne acikin Nigeria wanda zamu dasawa boma_bomai,da Masallatai,da kuma churchs, kasuwanni,makarantu,ko ina za'a dasa bom,bayan nan kuma zamu kwashe samari mu karasu akan dakarun mu,zamu yaƙi sansanin sojaji da yan sanda,babu wa'yanda zamu kyale da rai.yan mata ɗari da daya zamuyi garkuwa dasu duk wanda yazo kawo fansar su a kasheshi,yara matan kuma zamu maida su namu,ta border za'a shigo mana da manyan makamai,da kuma sauran mutanen mu duk ta jirgin ruwa zasu zo".cikin jinjina wa da girmamawa suka fara zuba mishi tafi,hannu ya daga musu ɗan su dakata.cak suka tsaya.
"Ku tabbatar da a cikin ku duk wanda ya bata mana aiki komin muƙaminsa a cikin Italian Mafia dole ze mutu,mutuwa kuma mara dadi".
A tare suka mike tsaye sunawa kansu kirarin ƙungiya su.
"we are the mafias!, blood shed blood!,we stand with our words!,the world is ours!,we choose who to live, and we choose who to die!, mafias are the most strongest union".suna gama anthem dinsu suka fara shan giya ana shagali.
Barrister Lameer ya ce"innalillahi wainna'ilaihi rajuun,to kunji abinda wa'yannan azzaluman suke shiryawa.sunan location din da suke shine,okir......."buge wani karfen ya yi ya fadi a ƙasa yabada sauti da seda suka ji.
Da karfi" sukace waye a wajen" ku duba ko waye sannan ku kashe shi,nan take Barrister Lameer ya fara salati domin yasan tunda suka ganshi kam na shi yazo karshe.fita a inda ya buya ya yi ya fara gudu yana son barin wajen,yana cikin gudun ya cire memory cikin wayar ya jefasa cikin bakinsa.nan ne video din ya dauke gaba daya.


Ransu ya matukar ɓaci lokaci daya kuma ya tashi,suna son kashe rayuwakan al'umma da basu ji ba ,basu gani ba.
Da Karfi LTG ya daki table din gabanshi da karfi ,idon sa ya yi jajir.
Furzar da iska me zafin gaske ya yi daga bakinsa.
Sudais shafa gashin kansa ya ce"wa'yannan sun riga da sun gama shirin su,babban abin takaici shine bamu san ya kamanin sabon shugaban nasu yake ba, yana da wayo yaƙi yarda a san fuskar sa,ba musan a wani lokaci ne zasu tayar da bom din ba yakamata mu dakatar da su".
"Duk wayon sa baze taɓa kaucewa tarkona ba,koma wanene shi se na kamosa na mishi hukunci dede da Abinda yake aikatawa"LTG ya faɗa yana miƙewa tsaye.yana kallonsu"Sudais dakai zan fara, suna kokarin shigo da mutanen su da mugayen mukamai ta border,you're comptroller General,nauyin dakatar dasu ya rataya a wuyanka kabada umarni duk wani abinda za'a tsallakar dashi border daga yanzu zuwa end of this month, ka sa a rufe border babu abinda za'a shigo dashi har se da sa hannunka,saboda you're comptroller General Sudais"jinjina kai Sudais ya yi.
Maida kallonsa kan Jawan ya yi "kai mataimakin commissioner of police ne,ka zuba jami'o'i ta ko ina bama iya garin nan ba da duk sauran state. communicate with your co assistant commissioner of police".


Gyada masa kai Jawan ya yi.pointing din Saghar da hannu ya yi"Saghar make sure ku ankara a hospital daga zarran kaga wa'yanda baka yarda dasu ba don't hesitate to inform me".


Yaci gaba da magana"bana son kowa yasan da shirin da muke yi so becarefull".


"In sha Allah LTG,zamuyi nasara akan su" "very good,nasanku bakwa wasa da aikin ku, rayuwakan al'umma shine muka shiga wannan aikin akai with any cost we have to save their life's"ya ƙarishe maganar yana rike kansa dake sara mishi.yana jin kan ya fara ciwo,amma bayanin da zeyi yana da matukar muhimmanci hakan yasa yaci gaba da maganar ba tare da ya dakata ba,amma shi kadai yasan yanda yake ji,abun a jininsa yake rashin dogon magana in ba ya zama dole ba,baya dogon magana.


Kallo ɗaya suka mishi suka fahimci kansa ya fara mishi ciwo.hannu Saghar ya sa a aljihunsa ya fito da maganin ciwon kai ya basa karba ya yi ya jefa abaki ya haɗiye.


"LTG!,make sure you drink water saboda maganin ya yi melting "hararansa ya yi"ba zan sha din ba,kufa doctor's din nan ko..."ya yi shuru yana zama,dariya sukayi Jawan da Saghar suka tafa.
"Ku de anyi yan air,yanzu de kunji maganar da LTG ya yi so concentrate"
"In sha Allah ".


karfe goma na dare kafin suka bar part din nasa cike da tunanin yanda zasu kawo karshen Italian Mafia.


Se 11:00pm suka baro wajen abbu nan ma seda Hajiya babba ta korasu,kafin suka tafi.


Basu shiga bedrooms din su ba suka
shigo nasu Sabriyah suna kwance suna bacci.
"Ayyah yau nasan sun yi missing din mu"gobe se mu haɗu.
Suka faɗa yana barin dakin, Parsa kashe musu wuta ta yi kafin ta bi bayan yan uwanta.




Washe gari bayan sun karya babu wanda ya fita aiki saboda su mom Rumanatu ana hanya sun kusan sauka.


Duk wani abinda ya dace da za'a karbesu an yi sa.


Karfe sha biyu na rana suka shigo gidan,bayan yan gaisa ne suka wuce masaukinsu, Ashman da Dawood a part din Sudais suka sauka.jaleelah da Iftisan part din su parsa suka sauka.


Sauka sukayi sukayi sallah sannan suka huta,bayan sun gama cin abinci ne aka dawo falo ana hira.
Hajjatiye da a jirgi tazo ba'a motar ba amma se bala'in ta gaji takeyi,su Hajiya babba suna mata sannu,Ammuh dake hakimce akan kujera tunda suka zo sannu da zuwa ta yi musu ba ta sake ce musu komai.


"Bak'ar annamimiya,dama nasan tsinannen bakin halinki be ze bari kice mini sannu,yau da zan faɗi in mutu da kin fi kowa murna,ke kam khareema kin yi asarar rayuwa.babu yanda kika iya dani nan gidan ƴa'ƴa nane se in sa ya sake ki inga tsiyar tsinantakar da ze faru,ni maye ma haka yaganni ya barni,bare kuma ke yar adama,mara mutunci kawai". shuru wajen ya yi babu wanda ya isa yace ta yi hakuri ta hakura, mutum na sa baki zata dawo kansa.
Su Ammi de ido suka zuba musu,tun lokacin da Abbie ya auro Hajiya khareema haka kurum basa shiri saboda girman kan Hajiya khareema.shisa Hajjatiye bata santa.


"Hajjatiye wai Ni kadai kika tsana a gidan nan ne!?,duk lokacin da kika zo se kin kwashemin albarka meye na miki da zafi haka ga su hamdiyya da Badeeya,ga Abida su baƙi tsane su ba se ni!?", Bude baƙi Hajjatiye ta yi alamar mamaki"lahaula wala quwata illabilah!, khareema yanzu zagina kike yi saboda ni ba uwarki bace shine zaki za ge kina zagina ko, tabbas Mubarak yau ni matarka take zagi saboda lalacewa yakai lalacewa"ta fashe da kuka,abinda suke gudu kenan da ace Ammuh ta yi shuru batace mata komai ba da Hajjatiye shuru zatayi in ta gaji dan kanta.
Dawuwa kujerar da take zaune Abbie ya yi ya hau bata hakuri,mom Rumanatu da abbu, uncle Hameed suka sa baƙi suka bata hakuri, dakyar ta yi shuru.
Ta goge fuskarta da gefen gyallenta ta ce "nadawo kanku,yanzu meye abinda kuka ribantu dashi da kuka bar yaran nan zabga_zabga dasu babu aure cikin su babu wanda baze iya yiwa matarsa ciki ba, ɓalle a ce basu kai aure ba,dubi yan matan. duk kun haɗa yara kun barsu a gantale se anyi magana a ce wannan soja ne, wannan likita,wannan kustam,wannan police, wannan yan kasuwa,yara duk sun kosa amma kunki aurar dasu se an kawo muku jarirai daga waje a ce wani ya dirkawa wata ciki ko"duk se da sukaji kamar su nitse kasa tsabar kunya, miƙewa da sauri Hajiya babba da Ammi sukayi.
"To Ku kuma ina zakuje,anyi maganar ku aurar da yara kun wani miƙe zaku gudu,wato kun fi so ku gansu jere da ku a rasa waye uwar waye yar,to dawo ku zauna "simi_simi suka dawo suka zauna,babu yanda suka iya amma kunya kam sun sha shi.
Masifar Hajjatiye kam sun sha,ta yi hatta gaji ta yi shiru,se kuma aka dawo hirar Sudan da ita kamar ba ita ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login