Showing 39001 words to 42000 words out of 94974 words
comments dinku yawan read more din da zan yi muku,infact ma in bakwayin comment Wallahi hutu zan tafi in yaso in kun shirya yin comments din se muci gaba amma bazeyu ina muku posting ace wai comment ya gagara ba.
Comment,like and share 🖋️🖋️
*🌹🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹🌹*
Page 15
*_Story & written_*
By
*MRS🌹ISHAM🌹*
( Yar lelen Jarumai)
*THE WRITER OF 🖋️*
*NIDA PATIENT DINA*
~And now~
*🌹ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*
📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️
Page 15
Haka suka gama cin abinci kowa ka kalla zakaga fuskar shi da alamar damuwa, uncle Hameed ne ya kalli Saghar da Sudais ya ce"ina son magana daku biyun"mikewa su Zoya sukayi suka bar dinning din Jawan da Sahil,Salim suma suka tashi sukayi.saura daga uncle Hameed din se Hajiya babba, Ammi,Anty amarya se su wa'yanda akace su tsayan wato Saghar da Sudais.
Maida hankalinshi uncle Hameed ya yi kansu sannan ya fara magana"meyasa kuke haka Saghar, yanzu ga shi tabar dinning din batare da ta kammala cin abinci ba!, ka bata mata rai. ba ko da yaushe zaku dinga titsiyeta akan yawan fitan da takeyi ba kamata ya yi kuje ku sameta cikin lallama da kuma daɗin baƙi ku nuna mata yawan fitan da takeyin nan ba kwa so tun kuna yara ake abu daya ga shi har kun girma kun mallaki hankalin kanku you're all matured enough.kai doctor ne shi kuma Sudais custom,babu wanda yakamata yasan matsalar mahaifiyar ku sama da ku din nan kunga de Zoya da Parsa bawani girma sukayi ba,ni se nake gani kamar akwai wani abinda yake damunta wanda bataso kowa ya sani tabbas tana cikin damuwa,kallon mintuna biyu nayi mata na nazarci hakan a tattare da ita,so please take good care of your mother mahaƙurci,mawadaci".
Sun matuƙar gamsu da maganar uncle Hameed dama su abinda yake bata musu rai shine yawan fitan da takeyin ne,kuma har yau babu wanda ya san ina take zuwa.
Sudais ya ce"in sha Allah zamuyi yanda kace uncle Hameed duk da bamu san menene matsalar ba,ni bawai yini nakeyi a gida ba in na fita 10:00am na safe bana dawuwa se yamma kuma duk da hakan bazan samu ummah a gida ba abin na sosa mini rai matuka."
Haka Hajiya babba da su Ammi suka sake musu nasiha akan kulawa da mahaifiya,kafin daga bisani suka watse sudais ne kaɗai ya yi saura akan dinning din yana zaune yana danna wayarsa, buɗe sakonnin da suke shigowa ya keyi.kusan awan shi ɗaya a wajan masu aiki suka gama kwashe komai aka gyara duk yana zaune.
Fitowa Umaisha ta yi daga ita se riga da wando na bacci masu kauri black color kanta babu dankwali bare hula. saboda batayi tunanin zata hadu da kowa a ko ina ba shisa ta fito haka kanta tsaye ko ajikinta.
Saukowa ta yi dinning ba ta ga kowa ba sakamakon kashe wutan da Sudais ya cewa fatime ta yi hakan yasa bata ga mutum awajan ba ta shiga kitchen dan daukan ruwa da snacks dama abinda ya fito da ita kenan,tun shigowar ta ya hangota girgiza kai ya yi a hankali ya furta "yaran nan ba sa jin magana" gently ya mike ya nufi kitchen din ya tsaya a kofar ya harde hannunshi a kirjinsa yana kallonta rai abace.daukan abinda zata ɗauka ta yi ta juya domin barin kitchen din haɗa ido sukayi nan take tsoro ya kamata batasan lokacin da ta zubar da abubuwan hannun nata ba saboda tasan yau bazata kwana da gashinta ba tunda har ya yi mata warning akan hakan tasan yau shikenan malu Sudais ze yi mata.
Daura hannu aka ta yi ta fara w'iwi da hawaye ta riƙe gashin nata ta soma magana kamar wata zararra"ya Sudais ka yiwa Allah ka yi hakuri bazan sake ba, karka rabani da gashina, wayyo Allah shikenan gashina.ya Sudais daga yau inka sake ganina ba hula kamin duk hukuncin da zakamin, amma dan Allah karka rabani da gashina kaga kowa na dashi su Rameesa zasu mini dariya "tana magana tana yarfa hannunta.tama ƙasa nutsuwa ta yi magana,matsowa kusa da ita ya yi ya sa hannunshi daya ya cire hannun da ta rike gashinta da shi,da hannu daya ya haɗe hannayenta duka biyu ya riƙe su gam.sannan yasa hannu a bayan aljihun shi ya fito da wuka yar karama se sheki yakeyi kamar ba'a taɓa amfani da ita ba ya kalli fuskar Umaisha yaga yanda ta zaro manyan idonta waje ga hawayen da takeyi har lokacin,a tsorace ta ce"innalillahi wainna'ilaihi rajuun!ya Sudais dan Allah kayi hakuri ka rufamin asiri kaga ni yarinya ce dan Allah karka rabani da gashina Wallahi bazan sake yawo ba hula ba, i promise you.in kaaaaaaaaa...aske mini gashi na miji zan koma me malu dan Allah ka yi hakuri".
Ko kallonta be yi ba yasa hannu ya haɗe gashin waje daya ya ce"da na ke ce miki banason ku dinga yawo haka kam ba kun renawa mutane wayo ba!? kullum sekinyi alkawari bazaki sa'ke fitowa ba hula ba yau kam dole fa sena aske gashin nan sede in mutuwa zakiyi amma for sure zan aske".ga nin tabbas dagaske ya keyi askin ze mata yasa ta faɗa jikinshi sannan ta rike hannayenshi da ke rike da wukar tana kuka"ya Sudais bazan sake ba ka ji!?kayi hakuri". Da sauri ya rabata da jikinshi yana watsa mata harara ya ce"munafuka duk senayi maganin ku daya bayan daya tunda kunce ku bakwa jin magana da ƙaton kanki kamar randa, ki wuce ki bani wa..."be ma kammala magana ba ta sa gudu. taku biyu me kyau ya yi, ya riko hannunta ya ce"wa kika barwa kayan nan da kika zubar a ƙasa?!" Jiki na rawa ta fara kwashewa Allah _Allah takeyi tabar wajan gudun kar ya canza ra'ayi,maida snacks din ta yi ta ajiye ta ɗauki iya ruwan kawai ta fice da gudu, murmushi ya yi yabi bayanta da kallo koma wa dinning table din ya yi yadau wayarsa ya koma part din shi.
Rameesa da iklas sune suka rage idon su biyu sauran kam duk sun yi bacci a dakin nasu dama haka sukeyi zasu zo dakin Rameesa da iklas su yi hira. suma su koma dakin su duk da a haɗe yake kofa ce kawai ya raba su,yaran matan part din su daban. babban falo ne da two bedrooms komai na jin dadi akwai aciki duk inda suka gadama suna kwana kuma kowa ni bedroom akwai manya_manyan gadaje har guda uku.some times a daki ɗaya suke kwana dukkansu.yau ma haka bayan sun baro dinning suka shigo dakin su Rameesa suna cikin hira umaisha ta ce zataje ta dauko musu ruwa da snacks, kafin ta dawo ne Parsa da Zoya suka yi bacci ya rage saura Rameesa da iklas ne idon su biyu.
Shigowa ta yi tana kuka harda shesheka tasowa sukayi suka je suka rike hannunta suka zauna abakin gado suna tambayar ta me ya faru dakyar ta iya faɗa musu abinda ya faru tsakaninta da Sudais,jikin su ne ya yi sanyi jin saura kadan yau Sudais yayiwa umaisha aski da wuka,sosai suka dinga bata hakuri har ta yi shuru sannan suka kwanta bacci.
A bangaren Sudais kuwa yana shiga part din shi ya tarar da Jawan da Saghar aciki da mamaki yake kallon su kafin ya shigo ya zauna yana faɗin "wai ku bakwajin bacci ne?"kallon shi sukayi a tare Jawan ya ce"ya Sudais wannan ɗan renin hankalin na biyo ya faɗa mini yaushe ze dauki hutu muje wajan hajjatiye, dan Wallahi muka bari tazo mu ba muje ba mun shiga uku tunda abbu da Abbie ma kafin suyi tafiya seda suka ƙara jaddada mana akan zuwan namu amma Saghar kam ya yi burus da zancen"rufe laptop din gabanshi Saghar ya yi ya ce"ya Sudais shi baze gane bane aiki ya mini yawa amma nan da next week se mu shirya mu tafi"shi de Sudais bece musu komai ba se binsu da ido da yake yi, saboda yasan sarai su Abbie suka dawo suka ji basu je ba ransu ne ze ɓaci,yana kokarin musu magana kira ya shigo wayarsa picking ya yi yasa a kunne.
Wata tausassan murya me zakin gaske da kuma amo yana da kauri irin muryan jaruman maza da suke cike da izza,isa,gadara,haɗe da kuma umarni ne ya sauka a kunnen Sudais,ya ce "sa wayar a handsfree "yanayin yanda ya yi maganar kadai ma ya isa ya kwadaitawa mutum yaso ganin wanene mamallakin wannan murya,domin yanda ya ke fitar da maganar ma kadai abin burgewa ne.
Kamar yanda ya faɗa haka kuwa Sudais ya yi yana murmushin mugunta ya saka wayar a handsfree din,kallon Sudais suke yi suna jira suji waye ze yi magana har kusan minti biyar kafin ya futar"ku shirya gobe ku tafi"iya abinda ya furta kenan 'kitt' ya kashe wayar dariya Sudais ya yi dan yasan yanzu kam tunda ya basu umarni yasan dole su je kuma a gobe_goben domin basa jayayya da maganar shi kallon Sudais Saghar ya yi ya ce"ya Sudais meyasa kafadawa LTG.Taj maganar tafiyan!?" dariya me yar sauti Sudais ya yi ya ce "ko kadan Ni banyi wannan maganar dashi ba,duk wani motsin ku yana kallon kowa, kaff gidan nan akwai cameran tsaro, part biyar ne kawai babu daga part din Ammi, Ammuh, Hajiya babba,Anty amarya,ummah.nan ne kawai babu a part din iyayenmu mata ne kawai babu CCTV camera" dariya Jawan da Saghar sukayi.
"Yanzu de zuwa Sudan ya kamamu gobe wajan hajjatiye,amma su ya Sahil sun sani kuwa!?"cewar Saghar "malam kowa fa yasani kude kuyi booking tickets kawai"Sudais ya faɗa yana nufan bedroom din shi.hira sukaci gaba da yi se around 12:00 na dare kafin kowa ya nufi inda yake kwana.
LAGOS ORIENTAL HOTEL
Bayan sun iso hotel din da yake suna ciki an kawo musu lafiyayyun abinci sukaci,nan ya zauna yana jan su dan hira saboda su sa'ke dashi, aikuwa hakane yafaru domin yanda yake musu kamar ya daɗe da sanin su,lokaci daya suka saba dashi,duk wani motsin Sabriyah yana kan idonshi ji ya yi yafasa abinda ya yi niyar aikatawa da ita saboda kallon mata a gareshi ya fara mata duk wani abinda tayi burgeshi takeyi baya gajiyawa da kallonta, Asmita ce ta mike zata fita Sabriyah ta ce "my Jerry ina zakije!?"se da ta bude kofar kafin ta ce "zan leka cikin hotel din ne in dawo!"ta fice, dawuwa kusa da Sabriyah ya yi ya zauna cikin nutsuwa yafara mata magana.
"Sabriyah nasan kinsan dalilin da yasa na dauko ki!?nayi ne saboda in samu wacce zata biya mini bukatata, but bansan meyasa ba tunda na daura idona akan ki se naji bana bukatar yin mu'amalar banza dake,ni bazan boye miki ba kullum sena kwanta da mace amma yanzu da ina tare dake se naji bana bukatar hakan! lokaci daya soyayyar ki ya kama zuciyata yanda bakya tunani.bansan ta ya'ya zan miki bayani yanda za ki fahimta ba,ji nakeyi akwai wata alaƙa me karfi tsakanina dake tunda jimawa wani irin lamari me karfi nakeji a tattare da ke Sabriyah. ki bani damar nuna miki soyayya ta har ki zamo mallaki na."kamar wani mutum mutumi haka Sabriyah ke kallon shi ko kyafta ido batayi ji tayi maganar nashi wani bankwarakwai ta ma rasa wani irin amsa zata bashi saboda ta fahimci he's a good guy amma bazata iya bashi damar soyayya ba saboda akwai sarkinta acikin zuciyarta duk da bata sa rai akan zata ganshi a rayuwarta ba amma ji takeyi intayi soyayya da wani ɗa namiji kamar taci amanar tajuju ne.
"Meyasa kakeson yin soyayya dani?shin babu wata mace a rayuwarka ne!?"ta yi mishi wa'yannan tambayoyin tana kallon cikin ƙwayar idon shi, murmushi ya yi se da ya yi jim kaɗan kafin ya ce"akwai wata acikin rayuwata wacce a ko da yaushe nemana akanta yake, nemanta nakeyi acikin wannan duniyar ba dare ba rana.zan iyayin komai domin in samota zan ka war da duk wanda ya zaɓi ya shiga tsakanina da ita,ban taɓa tunanin zan so wata ya mace bayan ita ba se kuma ga shi bayan ganin ki da nayi se zuciyata ta kamu da sonki,kin san ance zuciya batada ƙa shi,zan aure ki duk sanda na sameta sannan itama in aureta." Ƙayitatciyar dariya Sabriyah ta yi wanda se da ya yi sanadiyar lotsewar kumatunta da suke dauke da dimple kyawunta ya sake fitowa, kallonta yakeyi kamar wani tsohon maye duk abinda tayi burgeshi takeyi, yarinyar she's so simple and dam beautiful.
Dakyar ta iya dakatawa da dariyar renin hankalin da takeyi ta ce "ya ma sunanka dan Allah!?"ya ce "FU'AD na ke" "yawwa Fu'ad Wallahi kabani dariya dakace wai zaka auremu mu biyun,ni ina da wanda nake matukar kauna a rayuwata duk da bansan aina ne zan sameshi ba. amma, ina fatan haɗuwa dashi ko da ranata na ƙarshe a duniya ne ruhina ze samu sallama a duk sanda na hadu dashi."duk da ta faɗa mishi wannan maganar amma har lokacin murmushin kan fuskar shi be kau ba se ma ƙa ru wa da ya yi,ya ce" amma ya sunan shi saurayin da kikeso din!?"langwabe kanta gefe ta yi ta lumshe idanunta ta ce"sunanshi ta..."ba ta karasa ba a sakamakon kiran waya da ya shigo wayar Fu'ad ya ce mata "bani minti biyu bari inyi picking call"gyada mishi kai ta yi,fita a dakin gaba daya ya yi yana waya.dawo da kallonta kan kujerar dake dakin ta yi taga tarkacen laptops kusan biyar ga wayoyi da suka kai goma zuciyarta ne ya biya mata da son kallon abubuwan da suke ciki,mikewa ta yi ta isa har gaban kujerar tana kallonsu mamaki ne Yakamata tafara tambayan kanta to me Fu'ad yakeyi da wayan nan wayoyi da laptops masu yawa haka?, wani kofi ta gani na glass sims ne aciki masu yawan gaske wanda zasu iya kaiwa ɗari,sun cika kofin ga wani farar leda cike da cocaine wato fodar ibilis,duk da shi cocaine din bata san menene ba sa hannu ta yi ta dauki leda daya tana jujjuyawa,cike da karambani irin na Sabriyah yasa takai shi dede hancin ta tana kokarin shaƙa saboda tasan meye aciki,daga bayanta taji ya daka mata tsawa "Sabriyah"da sauri ta ajiye ta juyo tana kallon shi karasowa wajanta ya yi ya ce "me kikeyi anan!?"kallon su laptop din da suke jibge akan kujerar ta yi babu ko shakka ta ce "Fu'ad meye kakeyi da laptops masu yawa ga wayoyi ma,kalli sims masu uban yawa har cika kofi sukayi ,sannan kuma meye wannan a farar ledar nan!?"ta yi maganar tana nuna mishi su ɗaya bayan ɗaya.
Shafa gashin kanshi ya yi,ya yi mata wani irin kallo ta kasan ido sannan ya riƙo hannunta suka koma kan gado suka zauna ya ce "babu kyau taɓa abinda ba'a baka izini ba akai, sannan kuma babu kyau dogon bincike!nidin me siyar da kayan wayoyine dasu laptops ina da babban shaguna a Maiduguri Sannan kuma ina gyaran su. wa'yannan mutane da yawa ne suka bani domin inyi musu gyara sims din kuma in na cire acikine nake ajiye musu."gyada kai ta yi alamar ta yarda da abinda ya faɗa mata ta ce" okay nagane!to shi kuma wancan farin garin fa me kama da foda "kallon cocaine din ya yi ya ce "wannan kuma abin wanke toilet ne" "okay"ta faɗa ta kwanta akan gadon,ta kasan ido yake kallonta yana kokarin danne fushinsa domin yau badan Sabriyah ɓace ta yi mishi wannan abun to da ya daɗe da kashe mutum amma da yake ita yana santa hakan yasa ya shanye mikewa ya yi, toilet ya shiga ya kunna shower, batare da ya cire kayan jikinshi ba ya sakarwa kanshi ruwa yana jiƙa shi hannu yasa yana dukan gefen kanshi da karfi kamar wani mahaukaci yana cikin dukan kan nashi kuma se ya dakata ya kalli yamma da kudu sannan yasa hannu a cikin aljihu ya fito da wata ledar cocaine ya zuba a bayan hannunshi sannan ya ka fa kanshi akan hannun ya shaƙa da karfi,ɗago kan ya yi ya jijiga shi sosai sannan ya samu ya dawo dede.
Tana kwance tana tunanin ina kuma Asmita ta tafi da haryanzu bata dawo ta ji ya bude kofar toilet din ya fito ya canza kayan jikinshi da ya jika zuwa brown color din jallabiya kamar ba shine ya gama hauka acikin toilet ba se sakar mata murmushi ya keyi itama ta mayar mishi da martani ta ce "Fu'ad nikam bari in duba my Jerry a waje har yanzu bata dawo ba!" gaban mirror ya je ya tsaya ya ce "karki damu yanzu zata zo ba ta yi nisa ba"suna cikin maganar ta ta shigo,a rude jikinta har rawa yakeyi tazo ta rungume Sabriyah tana sauke ajiyar zuciya,ganin yanda ta shigo ne bata cikin nutsuwarta yasa Sabriyah ta ce "my Jerry meyafaru na ganki haka!?"numfashinta na fita dakyar ta iya cewa "my Tommmmmm,ina wannan din nannnnnn!?"magana take son faɗa mata amma tashin hankali da kiɗimewa ya hanata se jan maganar takeyi numfashinta na kokarin yanke.
Tunda Sabriyah taga haka tasan tofa abinda Asmita ta gani babban abu ne hakan yasa tasake rungumeta tana shafa bayanta duk dan tasamu nutsuwa.
Duk abinda suke yi yana kallonsu ta cikin mirror be ko waigo ba balle yace musu komai.
Dakyar nutsuwar Asmita ya dawo ta tashi ajikin Sabriyah ta ce "my Tom yau naga abinda ya tayar mini da hankali,ina wannan Umar din nan da suka je afafa shi da wannan!?"ta faɗa tana nuna Fu'ad dake zaune a gaban mirror.gyada mata kai Sabriyah ta yi alamar ta ci gaba da maganar.
Ta ce "yanzu aka fito da gawar shi acikin dustbin din hotel din anyi mishi kisan gilla seda aka sassara shi sannan aka jefa shi cikin dustbin."zaro ido waje Sabriyah ta yi tana me tuna lokacin da aka fito da ita daga dakin horo tare ta gansu shida Fu'ad a zaune.
"Allah sarki bawan Allah ko waye ya mishi wannan kisan gillan oho, gaskiya yanzu duniya abin tsoro ne"ta cikin mudubi yake kallonsu yana sakin murmushin da shi kadai yasan ma'anarta a ranshi ya ce "shi ya jawa kanshi mutuwa,babu wanda yake Sanin abu akaina kuma in barshi yaci gaba da rayuwa"yana