Showing 3001 words to 6000 words out of 94974 words

Chapter 2 - ASHE ZAMUGA JUNA COMPLET BY MRS ISHAM.txt

28 Dec 2024

8654

my baby girl meyasameki mukaji ihunki " da fa anty amarya Asrah tayi tace " mom there's nothing wrong with me my tajuju ne yayi drawing dina am so happy and excited" tafada cike da yarinta tana nuna musu zanen ,dafe goshi Ammi tayi anty amarya kuma tasaki baƙi tana kallon yar tata, duk sun ƙasa magana jin abinda Asrah ta faɗa musu wai saboda kawai anyi drawing dinta ne yasata wannan ihun da ya matukar daga musu hankali duk sunyi zaton mugun abune yasameta shisa cikin gaggawa suka nufo part din Taj din amma with their surprise babu abinda yasameta sema samunta dasukayi tana farin ciki da nishadi , sake jinjina ƙiriniya dakuma sangarcewar Asrah sukayi , girgiza kai kawai sukayi Ammi dakyar tasamu bakin cewa " Asrah you're unbelievable yanzu just because akan zane yasa kike wannan ihun " ta tambayeta tana karasowa kusa dasu gyada mata kai Asrah tayi ta ce " yes Ammi my tajuju made it for me" satan kallon Tajuddin Ammi tayi ta kasan ido dake zaune abakin gado yana danna wayarsa kamar besan da ruwan alamarsu a dakin ba ɗan ko kallon inda sukema beyi ba tun shigowarsu, yar murmushi anty amarya ta yi ta ce " Allah ya shirya min ke " kafin tasa hannu ta dauketa taname mayarda kallonta kan Tajuddin " Taj ina cikin yi maka favorite dinka kawai naji ihun wannan sarkin rigimar zakazo kaci ne ko in kawo maka shi!? koɗe in bawa Ammin ka zakazo kaci a part dinta ?" ta fadi hakan tanameson jin abinda zece zuciyarta a karye , Ammi ka war da kanta gefe tayi kamar batasan akanme suke magana ba .


Dakatawa da danna wayar da Tajuddin yakeyi ya yi ya dago ahankali da shanyayyun idanunshi da se yanzu ne cikinsu suka samu damar fitowa saboda maida facing cap din kanshi baya dayayi manyan idanunshi da eyeballs din suka kasance golden color ne yasaukesu akan anty amarya yafi tsawon minti biyu yana kallonta batare da yace wani abu ba sema lumshe idon da ya yi kafin da narƙekkiyar muryanshi ya ce " anty amarya koda danni kika dafa bazanci ba ki dauka kibawa yar uwarki kawai , and please zaki iya ce mata tafita min a part dina" wannan kalmar da Tajuddin yayi bakaramin girgiza zuciyar anty amarya yayi ba jin yanda Tajuddin yake furta magana kamar Ammi ba ita ce ta haifeshi ba , dukda ba wannan ce rana ta farko ba kuma irin wa'yannan kalaman sun saba dajinsa abakin Tajuddin amma hakan be mata dadi ba, ammi kam dakyar ta iya danne kuncin zuciyarta tafice tabar musu part din bin bayanta Asrah tayi tana " Ammi ki daukeni " tsayawa tayi ta dauki Asrah din suka fice a part din nashi .


Zama kusa dashi anty amarya tayi kamar yanda ta saba ta kalleshi dakyau ta bude baki zatayi magana kenan ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu yana " Please anty amarya not again na gaji da jin wa'yannan kalaman naki akan yar uwarki bana bukatar ji " ajiyar zuciya anty amarya tasauke sannan tace " Taj dole sena fada maka gaskiya abinda kakeyi sam be dace ba duk abinda yahaɗaka da Ammi karka manta fa ita ce ta haife ka ko bakomai taci darajan mahaifiya domin ita ce sanadiyyar zuwanka duniya! wallahi Ammi na sanka dan Allah kamanta da komai kadena daurawa kanka damuwa tun kana ɗan karamin ka dakai Please my Taj " tunda tafara magana yake gyada kai kamar wanda yayi na'am da maganar nata jin tayi shuru ne yasa ya ce " kaina ciwo yakeyi i need to rest " yana gama fadar haka kuwa ya kwanta abinshi yabarta a zaune tana binshi da ido, mikewa ta yi ta fita adakin ɗan ta lura bayason ana dauko mishi maganar Ammi kwata_kwata amma itade bazata taba hakura ba seta shirya tsakanin yar uwarta da ɗanta.


Seda ya tabbatar da tafice a part din gaba daya sannan ya mike zaune yana jingina jikinshi a makeken gadonshi , shi da zasu gane da sun dena shiga harkanshi ɗan ba son magana yake yi dasu ba, shisa yake son yasamu addimission din nan yafito yatafi yayi nesa dasu ko zesamu nutsuwa baya kaunar yanda suke dauko mishi maganar Ammi , yafison yanda yadauko rayuwar shi yakare ta ahaka. haka yadinga tunani iri_iri dayan zuciyarshi ta ce mishi to inka tafi ya kake tunanin Asrah zataji ? ahankali yafurta ko ɗan ita zandawo bayan shekara goma zandawo in aureta sannan indauketa muje muyi rayuwar batare da sun addabi rayuwata .




Ammi dakyar ta iya kawo kanta babban falo ta zauna zuciyar ta na radadi hade da ɗaci ,danasani fal acikin zuciyarta abinda yafaru shekaru sha bakwai ne yafara dawo mata ƙwaƙwalwarta datasan hakan ze dawo mata babban firgice da ta rungumi ƙaddararta da tasan zata haifi abin cikin nata kuma tazo tana mugun kaunarsa dabatayi wannan kuskuren ba. tunani tafara tayanda zata shawo kan Tajuddin ya yafe mata se wata zuciyar ta ce mata karfa ki manta bawai laifi daya ne kikayiwa Tajuddin ba ,manyan laifi guda biyu kikayi mishi ta ina za ki fara neman afuwarsa? Sosai jikin Ammi yayi sanyi se saƙa da warwara takeyi , shigowa falon Hajiya badiyya tayi tundaga nesa data hangi Ammi tasan akwai abinda ke damunta zama tayi kusa da ita,tsabar yanda Ammi tayi nisa cikin tunani batasan ta shigo falon ba, taɓata Hajiya badiyya tayi ta ce " Hajiya hamdiyya lafiya naganki cikin damuwa? ko dayake nasan be wuce tsakanin ki da Tajuddin ba " kallonta Ammi tayi ta ce " Hajiya babba wallahi bansan yazanyi in shawo kan Tajuddin ba, abu ne me matukar wuya " ta kare maganar tana zare medicated glass din idonta tana fuskantar kishiyarta ta, ɗan nisawa Hajiya badiyya tayi ta ce " kuskure an rigada anyishi amma duk da hakan kema danaki laifin duk wani ɗa yana bukatar mahaifiyar shi ta jawoshi ajikinta amma Tajuddin be samu haka daga gareki ba ga laifin da kikaso tabkawa tun kafin yazo duniya bayan wannan kinsake yin wani laifin da haryanzu Taj dashi yake kallon ki. Hajiya hamdiyya ke Mahaifiyarsa ce haryanzu kinada damar da zakije ki neme afuwarshi nasan Taj yanada zuciya me kyau idan kikayi mishi bayanin komai dakuma dalilin haka nasan ze fahimceki , kiduba kiga yaron nan tunyanzu yanaso yarikoɗe yakoma boss wannan dalilin ne yasa Abbie dinsu yake tsoron zuwanshi makarantar sojoji domin a yanzu ma ya'ya? Ya muka ƙare da Taj inaga yatafi yaje yayi shekara goma yana daukan horon sojoji. tun kafin yasa ƙafa yabar kasar nan Yakamata muyi kokarin sassauto mishi da zuciyar shi yayi sanyi yasan kedin uwarshi ce bawai maƙiyarshi bace domin khareema tarigada data gama poisoning zuciyarshi da tsanarmu , har kullum cigaba da cusa mishi ƙiyayyar yan uwanshi da iyayenshi takeyi " tunda Hajiya badiyya tafara magana Ammi ta mayar da hankalinta gaba daya kanta domin maganar ta hakane dolene tasan hanyar da zata ƙwato ɗanta daga sharrin Hajiya khareema domin tanason juyawa Taj ne tunaninshi akansu bude baki tayi zatayi magana sega Hajiya khareema tafito tana nufo inda suke, tsayawa tayi akansu ta riƙe kugu ta ce " naji kamar gulmata kukeyi to adeji tsoron Allah adena gulma da munafurci in an girma asan an girma , duk wani kulle_kullen dakuke kullawa agidan nan ina sane daku yanzu muka fara muzuba mugani kaff senayi maganin ku" tana magana tana kallon Asrah dake wasa acan gefen su mugun kallo ta watsa mata cike da tsananin tsana , Hajiya babba da Ammi de acikinsu babu wanda ya kulata balle tacigaba dayi musu rashin kunya hakan yasa taja doguwar tsaki tayi gaba tana kokarin shiga part din Taj.
Girgiza kai kawai Ammi da Hajiya babba sukayi kafin sukaci gaba da tattaunawar dasukeyi.


Tana daf da zata shiga part din Taj ta hango anty amarya tafito malalacin murmushi ta sake da ita kadai tasan ma'anarshi , ka war da kai anty amarya tayi kamar bata gantaba , bangaje anty amarya Hajiya khareema tayi dayasa saura kadan ta fadi , sannan tayi gaba abinta kamar babu abinda tayi .
afusace anty amarya tabi bayanta tasa hannu ta jawo hannun rigarta ta dawo baya sannan itama ta hankaɗeta ta fadi ƙasa warwas kafin ta nunata da yatsa " wallahi khareema ki shiga taitayinki dani acikin gidan nan karki ga idan kinayiwa su yaya suna ƙyaleki ni to bazanyi shuru kice za ki takani ba , ah ah baki isa ba munafukar banza munafukar hofi" yanda anty amarya take magana ranta amatukar ɓace ya isa yanuna kancewa tabbas akwai babbar yar tsama a tsakaninsu.dafa kujeran dake kusa da ita tayi ta mike ta ce....






Comments, like and share for more...




*🌹🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹🌹*






*_Story & written_*



By


*MRS🌹ISHAM🌹*
( Yar lelen Jarumai)








*THE WRITER OF 🖋️*
*NIDA PATIENT DINA*




~And now~
*🌹ASHE ZAMUGA JUNA 🌹*






📚📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATED 📚📚🖋️






Page 03




Da fa kujerar dake gefenta ta yi ta mike ta ce " Abida kenan , duk wani kule_kulen munafurcin da kuke yi dake da wancan munafukar ya'yar ta ki Hajiya hamdiyya dakuma ɗayar munafukar taku Hajiya badeeya ina sane daku kuma nafi karfinku , karkuyi tunanin zan zuba muku ido , ina nan ina bin duk wani takun ku !" Magana takeyiwa anty amarya hade da makirar murmushi dauke akan fuskarta,anty amarya kuwa binta kawai takeyi da kallon tsana saboda duk duniya babu irin mutumin da ta tsana sama da munafiki kuma makiri.
Batare da anty amarya ta ce mata komai ba ta juya tana kokarin barin wurin riko hannunta Hajiya khareema tayi tazo dede kunnenta tafurta mata " hankalina baze taba kwanciya ba sena raba ku da Tajuddeen sannan kuma in mai dashi karkashin ikona se yanda nayi dashi bayan hakan ya faru kuma zan raba shi da farin cikin rayuwa . wannan alkawari ne dani Hajiya khareema na daukawa kaina " tana gama fadin hakan tasaki hannun anty amarya ta wuce tabarta awajan ta shige part din Tajuddeen, kamar wacce aka shuka awajen anty amarya ta ka sa koda kwakkwaran motsi kirjinta se bugawa yakeyi da karfi domin kuwa ba ta raba dayan biyu tasan abinda Hajiya khareema ta faɗa tabbas zata aikata, saboda tun farko ita ce ainihin musabbabin cusa ƙiyayyar kowa acikin zuciyar Tajuddeen aciki kuwa harda Ammi.
"Ya Allah ka shiga tsakaninmu da wannan makirar baiwar ta ka da ta shigo rayuwarmu da muguwar nufi , Allah karka ba ta Sa'a akanmu ." Anty amarya ta yi maganar azuciyarta jiki asanyaye.
ji ta yi an rike hannunta tasan ba kowa bace fa ce Asrah , kai dubanta ta yi zuwa kanta , ƙakulo murmushin dole ta yi ta sawa fuskanta ta tsuguna agaban Asrah ta ce " Asrah din mommynta ya akayi har kingama wasan naki ne ?" Ganin ta tsuguna ne yasa Asrah zagayawa ta hau bayan anty amarya,
ta ce" mommyna ki goyeni muje gun daddy " tashi anty amarya ta yi da Asrah din dauke a gadon bayanta suka isa falo anan ta iske Ammi ( Hajiya hamdiyya ) da kuma Hajiya babba ( Hajiya badeeya ) suna tattaunawa.


Tun kafin anty amarya ta karaso Hajiya babba take watsawa Asrah dake goye abaya hararan wasa tana fadin " gaskiya Asrah kinji kunya, shame on you ahakan kikeso in aura miki ɗana Tajuddeen? Kin girma bakinsan kin girma ba no!no bazeyu ba , jibeki katuwa dake abayan mamanki gaskiya bazaki auri Tajuddeen ba" dariya Ammi da anty amarya sukayi banda Hajiya babba da ta danne nata dariyar ta koma serious face dan tasan yanzu zasu ɗibi adashen tsiya ita da Asrah.
Kokarin sauka tafarayi abayan anty amarya ta name kwabe fuska jin abinda Hajiya babba ta faɗa, sauketa ƙasa anty amarya tayi . Wajan Hajiya babba Asrah taje ta tsaya ajikin kujerar datake zaune, ido tabb da hawaye ta ce " adiya babba dan auri tajuju ko " girgiza mata kai ta yi ta ce" no bazaki aureshi ba ,cos he don't loves you" da karfi ta ce" he loves me " ta faɗa tana goge guntun hawayen idonta sannan ta ƙara da fadin " kuma ! Kuma seya aureni din " ta karishe maganar tana murguda dan karamin bakinta , tabe baki Hajiya babba ta yi ta ce" to ai se ya aurekin mugani " anty amarya de da Ammi yan kallo suka zama domin kuwa sun san mudin Asrah ta shaqa tofa gidan nan yau ba zaman lafiya dan rigimarta ma kadai seya hanasu bacci , saboda tasan me ake nufi da kalmar love duk da kananun shekarunta , tunda tashin turai ce. yara tun suna ƙanana zakaga wai sun san meye soyayya,shisaka duk ranar da akace Tajuddeen baya sonta ko kuma baze aureta ba tofa ranar akwai chakwakiya agidan.
Kuka tafarayi a hankali tana " tajuju loves me and we will get married tomorrow" bakaramin dariya Maganar ta yabasu ba hakan yasa suka sa dariya dukkan su harda Hajiya babba dake tsokanar nata , dariyar da taga sukeyi mata ne yasa ta sake hassala ta fashe da kuka da karfi .


Tun bayan rabuwar ta da anty amarya ta shiga part din Tajuddeen bude kofar bedroom din ta yi ta zuba mishi ido , yana kwance yabawa kofar baya.
idanunshi a rufe amma jikinshi yabashi ana kallon shi , murmushin mugunta Hajiya khareema ta yi aranta ta ce " Tajuddeen Mubarak Bishara kaida samun farin ciki arayuwarka sede bayan na mutu amma mudin ina raye , sena rabaka da kowa " cikin kissa da kisisina ta shigo bedroom din ta zauna a bakin gadon shi tasa hannu ta yaye bargon dayake rufe dashi " my son bacci kakeji ne ? gaskiya bazan barka ka kwanta haka ba, tashi ka zauna bari in sa akawo maka abinci ka ji?" tana magana hade da kallon fuskarshi da babu walwala a cikinta ,mikewa ya yi ya zauna yana facing dinta, riko hannunta ya yi murya akarye ya ce " Ammuh duk faɗin gidan nan ke kadaice kika damu dani kuma kika damu da damuwata, duk da ci miki mutunci da ake yi akaina amma hakan besa kindena sona ba" yana magana yana sauke ajiyar zuciya saboda be saba magana me tsayi ba , murmushin samun nasara ta yi kafin ta koma kalar tausayi kamar wata mutumiyar kirki ta ce" ɗana Tajuddeen, banida burin da yawuce inga yan uwanka da iyayenka sun fara sonka narasa wace iriyar tsana sukayi maka , karkaga laifina idan nace hakan yasamo asali ne daga wajan Amminka , ɗan da ace ta nuna maka soyayya dakuma janka ajikinta tofa da kowa ze so ka, amma ah ah ta fifita sauran yan uwanka akanka , kullum kokarina shine inga na nunawa Hajiya hamdiyya abinda takeyi bata kyautawa ita da Hajiya babba amma daga nafara faɗa musu gaskiya sesu fara zagina da cin mutuncin hade da faɗin ina ruwana dakai , nikuma wallahi Tajuddeen bazan iya juya baya akan rayuwarka ba. Allah ya samun sanka tun daga ranar da kazo duniya na mayar dakai ɗana" ta karishe magana tana hawayen munafurci tasaka gefen gyallenta ta goge hawayen, kallonta yakeyi cike da tausayawa saboda Tajuddeen shi gani yakeyi ita kadaice masoyiyarshi acikin gidan daga ita se anty amarya se kuma Asrah da ya mayar da ita wani bangare na rayuwarshi.
Ci gaba ta yi da magana tana nuna mishi hannunta da ya gurje lokacin da anty amarya ta hankaɗata ta fa di ƙasa ashe ta gurje a hannu , yana fitar da jini kadan_kadan dake farar macece se wajan yayi jawur " kaduba ka ga abinda Amminka dakuma Abida suka aikata agareni" rai abace ya ce " Ammi ce tayi miki haka ita da anty amarya?" Cikin salon makirci ta ce" su sukamin haka Tajuddeen saboda naje nasamesu inayi musu magana akanka ,shine sukamin koran kare danaƙi tafiya kuma shine su biyun suka tureni nafadi aƙasa.
Amma bawai na faɗa maka hakan ɗan in tayar maka da hankali bane kokuma in shiga tsakaninka dasu ba kayi hakuri karka musu magana ,in sha Allah wata rana se labari komai ze wuce ." Tana magana ne hade da satan kallonshi ta ƙasan ido .


Tunda ta fara magana yake kallonta jikinshi duk ya yi sanyi jin wai ta dalilinshi akayi mata hakan lumshe idanunshi yayi ya makasa cewa komai saboda shi ba ma'abocin so da kuma yin dogon magana bane,shisa yarasa wata kalma zeyi amfani wajan bata hakuri akan abinda Ammi da anty amarya suka mata , kamar yanda ta faɗa .


Mikewa ya yi slowly yanufi toilet ze dauko first aidbox domin yayi mata treatment din ciwon da taji . Ya riko first aidbox Yana kokarin fitowa yaji kamar kukan Asrah dinshi, ka sa kunne ya yi dan ya tabbatar shin dagaske ita ce din take kuka ko kuwa, sake ji yayi hakan ya tabbatar mishi da antabo mishi Asrah fitowa yayi daga toilet din da sauri batare da ya dauko first aidbox din ba ɗan hankalinshi ya koma kan Asrah da take kuka , be ko kalli inda Hajiya khareema ke zaune ba yanufi hanyar barin bedroom din.
da mamaki take binshi da kallo ganin irin saurin da ya keyi kamar wanda ze tashi sama ,yana daff da barin bedroom din ya tsinkayo muryanta ,tana fadin " son saurin me kake yi haka " amsa yabata da" kukan Asrah naji shine zanje in daukota " beko jira abinda zata faɗi ba ya fice , afusace ta ce " bazeyuba dole in fara ka war da Asrah domin ita ce zata hanani cika burina akan wannan yaro saboda ba karamin so yake mata ba ,in banyi wasa bama zata iya wargaza min aikina danayi shekara da shekaru inayi . Dole indau mataki akanta" ta faɗa tana huci.








Comments, share and like 🥰🥰


Share fisabilillahi






🌹🌹 ASHE ZAMUGA JUNA 🌹🌹






*Story & written*


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login