Showing 27001 words to 30000 words out of 134612 words

Chapter 10 - Bakar Aya writing by Sadi Saknah.txt

16 Dec 2024

8690

kunji kun tsira"
Tana maganar tana fita cikin murya kaman ba tata ba,sannan kuma tanayi tana wata irin dariyah kaman shaiɗaniya.
Kallon sule tayi wanda tun ɗazu ya jefar da bulalar take hannunsa ta dukan Bombee ɗin.
"Ka tahomin da jakata gida,sannan duk wanda yakeda niyyar ɗaukar mataki akaina shima kada ya fasa"
Daga haka ta bar lungun ta nufi gidansu.














🖤 Sadi-Sakhna ce🖤
ƴar mutan jama'are


















____****🖤🖤****_____




🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤




🖤 _BOOK1_ 🖤






Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama'are_ ]












*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03


*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna


______________****_______________














Page 🖤18🖤










Wulgawar Bombee innayi tagani tana cin abinci, yaukuma ta dawo da wuri.innayin tafaɗa a ranta,kullum sai yamma liƙis take dawowa idan ta tafi makaranta,wani lokacinma sai dare yayi tukunna.Sau uku mlm Ahmadu yana kamata yana dukanta,amma ko kuka batayi,sannan kuma bata faɗi inda take zuwa ba,sannan kuma bata fasa kaiwa daren ba.
"Inna Daneji Addah Bombee tadawo tana ɗakinmu"
"Yauɗin kotaji magana babannku kai,amma a wanne yanayi tashigo"
"Uhm hannun duk jini har ya bata mata uniform ɗin jikinta"
Innayi ta faɗa a hankali,cikin sigar gulma,saboda kar addar tata tajiyo ta,aikuwa Alƙalamin ya ƙarye,dan duk maganar da takeyi a kunnenta sarai.
"Jini kuma wanne iri,yauni kuwa mai zangani a duniyar nan,hadda jini"
"Ahh toh Bombee ai tazama abinda tazama sai du'a'i,ke kuma ban hanaki shiga harkarta ba ne,sai tazo tana dukanki koh"
Inna laari tafaɗa tareda zabgawa innayi harara,yanzu kowa yasan inna laari haushin Bombee takeji,saboda a rana idan ta duka innayi yafi a ƙirga,wani lokacin ma wai dan kawai ta kalleta,a wajen kwanciya kuwa wajibine saita yi mata na bacci. In abun bai zo ba kuwa saitayi sati bata kulata ba.
Hanyar ɗakinnsu Daneji ta nufah tareda tsayawa akan Bombee,wacce take zaune a tsakiyar gadon ta bawa ƙofah baya.
Zaro ido Daneji tayi data kalli yatsun Bombee,dan dama su tazo gani domin da ta tabbatar da zancen innayi,aikuwa hakane farcenta zaƙo zaƙo duk jini a jikimsu tamkar faratun mayu,yaushe ta tara wannan faratun haka babu wanda yasani.
"Bombee menene haka a hannunki kaman jini,na wanene?"
"Jinin bello ne,yatareni zai ɗau fansar abinda nayiwa ƙanwarsa,nikuma na yanka masa fuska da farcena"
"Yanzu dan yazo ɗaukar fansa saiki yanka masa fuska,bazaki kawo ƙara ba gida,kinkuwa san hukuncin hakan"
"Nasani kuma babu abinda ya isa yayi daga shi har iyayensa,idan aka sake nima zan sake,batun nakawo ƙara kuma menene amfaninsa,shin tunda nake an taba ramamin idan wani ya zalunceni,saidai a bani haƙuri zancen ya wuce,dan haka ni gaskiya bazan sake yarda da wanannan tsarin ba,dole na kawo nawa tsarin nima".
Dan takaici Daneji bata sake cewa komai ba,saima fita da tayi tabar ɗakin,abin yafi ƙarfinta yanzu kam.
Fitowa tayi daga ɗakin tana miƙa tareda yin hamma,ruwa ta ɗiba a bokiti tashiga banɗaki tayi wanka. Lokacin data fito innayi tashiryah cikin kayan islamiyyarsu da jakarta a hannu.
"Ke wato ina jinki kina gulamata ɗazu koh,idan kin dawo daga makarantar ki wankemin kayana,idan basu fitaba kuwa........hmmmmm bazan ƙarisa ba"
"Bazata wanke ba idan ke kika haifamin ita,ko wankin kayanta banfara bata,amma ke kin fara bata naki dan mugunta"
"To karta wanke,wannan bai dameni ba,tunda na riga na faɗa mata shikenan"
Da sauri innayi tayi magana cikin muryar kuka kafim inna laari tasake cewa wani abun.
"Ahah inna zan wanke mata kayan idan nadawo daga islamiyya,na iya wanki fah"
Cikin takaici babu yadda zatayi ta jijjiga kai.
Riga da wando tasaka irinna pakistan,wanda mlm Ahmadu yasiyo musu a taraba dayaje kasuwanci,hula da saka kanta kawai,babu hijabi tayi hanyar waje.
"Ke ina zakije haka babu hijabi,dama ba islamiyyah zakije ba naga kinyi wanka"
Daneji ta faɗa,tun dazu sai yanzu tayi magana,dan tasan idan tayi ma aikin banza tayi,an doki kashi.
"Wancan Alwasun yace karna ƙarayin kusada makarantarsa satin daya wuce,nice dama nacigaba da zuwa,saboda akwai abinda nakesom ƙarisawa,yamzu kuwa na gama.
Yawo zanje kawai cikin jeji idan wani abune a aika innayi takirani,tasan inda nake.
A bakin ƙofar gidan sukaci laro da gaji,aikuwa caraf tariƙe kunnen Bombee suka shigo gidan tare.
"Dan bantan ubanki mai kikayi wa bello a fuska,dan tsabar abinnaki yawuce gona da iyaka shine kika yimasa yanka da wuƙa a fuska ko,da nayi haƙuri,amma yanzu kam bazaja sabu ba,kotu zan yi kararku a zo a daureki,abun ai yayi yawa shege da hauka,gabaɗaya a kwanaki kaɗan kin dasawa ƴaƴan anguwa tsagwaron tsoronki?"
Tunkuɗa Bombee tayi a ƙasa a gaban Daneji,har sannan bata bar masifa ba ita ƙarfinta.
Zagi takeyi da uwa ta uba,inda tashiga batanan take fitaba,bakinta har kumfah yakeyi dan masifah.
"Wallahi bazan yarda ba,ku jirayi sammaci a gobe,ƙara zan kai gobe,bama a cikin garinnan ba can Sardauna zan kaiku ƙara kuma da kuɗin tara mai yawa.
Har ina da wannan abun,yaro yana can fuska tayi sumtum idon wajen ko gani bayayi tashi,jiki ya dau zafin zazzabin wahala kamar motace ta bugeshi.
Kuma a goben saita fadawa Alƙali mai tayi masa,daga nafara maganar ɗaukar mataki jikinsa zai fara rawa,yarinya ƙarama tasakashi a cikin asirinta,dolen uwarki ma idan kikaji wahala zaki kunceshi da kanki"
A haka tagama faɗan ta son ranta tafita ta bar Daneji ta sharar ƙwallar baƙinciki,hararar Bombee tayi wacce zaune a ƙasa idonta a soye kaman faɗan ba'a kanta akayi shiba.
Ɗakinta tashige tafara ribzar kuka kozata samu ta huce da suyar da zuciyarta take mata.
"Mtswww ji yanda ta batamin kaya kuma tasaka innata kuka,aradu zanyi maganinki ne,bar ganin ki tuleliya bai dameni ba"
A hankali tayi maganar tana tura baki,kafin tajuyah tabar gidan,ta nufi inda tayi niyyar zuwa tun farkon barinta gidan.


Sallama Daneji tayi a gidan gaji da sassafe washagari,dan dama sunyi magana da mlm Ahmadu da daddare akan zataje sasanto gaji kan abinda yafaru.
Wata ƙatuwar tukunyace akan murhu ann ɗumame yara zasuci su tafi makaranta.
Ga gidannan duk tarkacen kayan wanke wanke.
Faɗa gaji take rabawa tsakanin Zulaiha da yayarta akan kunun wai,fa'izah taɗau Zulaiha bayan itace na ashirin ta siyo bana talatin ba.
Sallama Daneji ta cigaba ta kwararawa amma har yanzu gaji bata jitaba,saida wani yaro yakirata tukunna kafin tajuyo takalli danejin.
Ɗan alamar tsorone akan fuskarta amma tayi saurin kawar dashi tareda ƙaƙalo murmushin dole.
"Ahhh Daneji kece sannu daxuwa,ga kujera zoki zauna a zubo miki ɗumame"
"Ahh nagode ma,an tashi lafiyah ya gidan"
"Gida kalau,lafiya naganki da sassafe haka,hala dai mutane gidan kalau"
Abinne yabawa Daneji mamaki har takasa boye mamakin nata akan fuskarta.
"Uhm gaji nace ba,akan zancen kaiwa kararnan nazo,dan Allah a ƙara haƙuri,a sansanta cikin rufin asiri,kaiwa kotun bashida daɗi.
Mlmn ne ya turoni nasake baku haƙuri,sannan za'a biya kuɗin maganin inyaso".
"Laah karki damu bakomai fah,faɗan yarane dabaka iyarmusu,babu komai yawuce bazai sake faruwaba,ki faɗawa mlm Ahmadu bakomai ya wuce baza'a sake ba"
Kasa jure tantamarta tayi,hakan yasa ta tambayi gaji mai yafaru.
"Amma gaji dan Allah mai ya faru naga kin sanja daga iya jiya,ina fatan dai hakan bayada nasaba da Bombee koh"
"Uhm Daneji kibar zancennan dai kawai,amma tunda kin matsa saƙo daya nakeso ki kaimata,dan Allah ya kice mata ƴaƴana bazasu sake shiga harkarta ba,itama ta taimaka tafita daga rayuwar mu,kowa hadu da daidan sa a yanzu"
Baki sake cikeda mamaki Daneji ta baro gidan gaji,a hanya babu sakar jakin da batayiba akan shin mai Bombee tayiwa gaji da ƴaƴan ta kuwa,kodai zancen mutane dagaskene kai,kai anya kuwa,in akwai wanda yasanta to bayana ne ai,kuma a sanina da ita bata tsafi bare nace shi tayi musu,to mai yake faruwa?
Tana cikin hakanne ta isa gida,zuwa lokacin rana ta fito yara sunata tafiyah makaranta,suma su Bombee sun shirya zasu tafi makaranta.
Daneji bata 'baata lokaci ba takama hijabin Bombee tareda janta cikin ɗaki.
"Maza maza ina jinki yimin bayani mai kikayiwa gaji naga ta sanja a dare guda?"
Ɗan murmushin dama nasan haka zata faru tayi,kafin ta jijjiga kai.
"Ni babu abinda nayi musu mai zanyi musu"
"Bombee ki faɗamin gaskiya mai kikayiwa gaji take haka,tabbas akwai wani abu,kuma kece kikayi ba kowa ba"
"Inna baki yarda dani ba ne?"
"A da kenan,amma vanda yanzu dakika sauya daga yanda kike"
"Eh to ba wani abu bane babba,kawai dai na ɗan leƙa gidansu ne da daddare nayi musu gagarɗi"
"Gargadin me,ke ƙarama dake zaki iya bawa wannan ƙatuwar matar gargaɗi,ai koni ban isa yimata kashedi ballantana ke,ki faɗamin mai kikayi musu Bombee,ni yanzu kin fara bani tsoro da halayyarki"








............Daren jiya..........




Karfa labari ya gundureku kunga an tsaya a waje guda ɗaya,komai da sannu ake warwareshi.
Dafatan zakuyimin hakuri dai....😏😊😊😊.











🖤 Sadi-Sakhna ce🖤
ƴar mutan jama'are








____****🖤🖤****_____




🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤




🖤 _BOOK1_ 🖤






Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama'are_ ]










*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03


*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna


______________****_______________










Page 🖤19🖤










A zaure mlm ya hadu da Bombee tashigo gidannasu,shikuma zai fita sallahr magriba.
Kallonta yayi na ɗan sakanni kana ya jijjiga kai,inda duka da faɗa suna yin aiki,da sunyiwa Bombee a ƴan watanninan,amma abinnata gaba gaba ma yakeyi kaman ana watsawa wuta fetur.
Shuru tayi taji mai zaice,saidai ga mamakin ta,waucewa yayi batareda yace mata komai ba,sauƙyƙyƙyiyar ajiyar zuciya tasaki,dan dama hakan takeso kada yayi mata maganar.
Kao tsaye ɗakinsi ta wuce tacire kayan jikinta,ta canza wasu daban,sallah tayi kafin tafito wajen cin abinci..
Ƙwanon nata abincin ta ɗauka a gaban Daneji wacce take zuba miya akan tuwon dawar da sukayi.
"Hmmm wai ke bana mijiba,amma saiki saka kai kifice daga gida sai magriba ki dawo,idan kika saka masa ciwon zuciya ya mutu ai saiki nemi wani uban koh?"
"Inna daga yau bazan sake fita da yamman ba,nagama fitan yamman dama yau"
"Ohh duk maganar da akayi baki dainaba saida kikaga dama tukunna,kenan bama bacin raina ne ba yanaki fitar,gama fitar kikayi?"
Shuru tayi bata amsawa innartata maganarta ba,inda wani ne dai da yanzu ya karbi amsa.
Cikin dare can misalin ƙarfe sha ɗayah Bombee ta tashi innayi wacce tayi nisa cikin Bombee.
"Ke dallah tashi ki rufe ƙofah ta ciki zan fita"
"Amma addah in baba yakamaki watarana kina fitar darennan fah,ko shiyasa kikace kin daina fitar yamma kin dawo ta dare?"
"Ina ruwanki toh,sauran naji ko wani zance mai kamada shi,saina babballaki a gidannan"
Gadon Bombee innayi ta kalla,inda ta haɗa tsummokara kaman itace akai a kwance,saboda ko baba zai iya leƙosu cikin dare.
Tashi tayi tabi bayan Bombee ta rufe ƙofar bayan ta fita.
Baƙaƙen kayane a jikin ta riga da wando sai hula,rufe idonta tayi kafin ta buɗe su a duhun gidannasu,ga gari yayi baƙiƙƙirin abinda da damuna.
Dan murmushi tayi ganin idonnata yamayar mata duhun zuwa haske,tarau take gani kaman safiya.
Kama katangar gefen ɗakinsu tayi ta ɗale kaman biri.
Kai tsaye gidan su bello ta nufah,nan kam bata tsaya bata ƙarfinta wajen hawa katanga ba,ta ƙofa tayi shigowarta,kasancewar ba ƙyaurene dasu ba,wani ɗan buhu kawai aka saka a bakin ƙofar gidan.
Tumaki suna kwance a tsaƙar gidan ta tsallekesu ta wuce ɗakin gaji.
Ƙyauren ta tura a hankali,tayi sa'a kuwa babu sakata,dan tsabar rashin tsoro duk barayin da ake fama dasu a garin amma ko sakata basu da ita a jikin gidansu.
Gaji ce a kwance ita malm idi akan gadon,ƙasansu kuma ƴaƴane guda uku anyi musu shimfiɗi suna bacci.
Babu abinda yake tashi a cikin ɗakin sai ƙarar gwartin gaji da kuma idi,ƙaremusu kallo Bombee tayi a duhun ɗakin,tareda yamutsa fuska tana toshe hanci,hamamin damuna da warin fitsari ya haɗu da ƙarnin jikinsu,da kuma warin bakinsu da miyar kuka yabada wani irin mummunan wari mai tada zuciya.
Kai barina gama abinda yakawoni nabar ɗakinan,irin wannan wari haka?"
Tsallaka wa tayi kansu tareda hawa kan ruwan cikin gaji,wacce take ɗaya bangaren akan gadon.
Cikin bacci gaji jin an hau ruwan cikinta tafara cewa.
"Kaifah mlm tsiyata dakai kenan,banda jaraba bakada aiki,yaushe ma kayine dazaka sake dawowa,so kake saika tsamamin jiki nakasa sana'ar gobe koh"
"Ba mlm ɗin bane buɗe i donki kiga waye"
Ihu gaji taso kurmawa lokacin data buɗe ido taga Bombee akan a zaune.
Kafin tace wani abu ta tura mata zanin data ɗauka a tsakar ɗakin.
Wuƙar Daneji ta zaro a kunkuminta ta mannawa gaji ita a wuyanta,wacce dama tun jiyan take kaifata,tayi kaifi sosai sai ƙyalli takeyi.
Wani yawun tashin hankali gaji ta haɗiye muƙutt tana zazzare ido.
"Tashi mijinki yanzu nan,sonake nayi muku kashedi kiji shima ya ji,kuma idan kikayi ihu saina girba miki wukar nan a wuyah,zanga dawane kan zaki dafa abincin siyarwar gobe"
"Dan Allah karki girbamin wannan wuƙar,ki bari tsaya yanxunnan na tasheshi,m...alllammm malam ka tashi"
"Uhn menene kike tashina ne,banace miki idan akayi ruwa bazani masallaci ba,ki bari da safe zanyi sallahr"
"Dallah ba sallah bace,in sallah ce ina ruwana dakai,kabarinmu ɗaya,sanda lawakiri yake tafkarka mai ya dameni,wannan rayuwata ce,katashi ka gani ni lusari kawai"
Idonsa ya buɗe yana rarraba ido,tareda lalumo fitila gefensa ya kunna.
Wani madoki ya ɗakko a gefensa tareda buge Bombee dashi saida ta faɗa ƙasan gadon.
sai a lokacinne gaji ta tashi ta zauna tana maida numfashi,.
"Ahh mlm ashe kai jarumine bansani ba,yaudai kayi abin kai,kullum ina cewa kadaina kawomin madoki ɗaki,ashe dai zayyi amfani"
"Me yarinyar nan take a ɗakinna da wannan dare haka"
"Ina zansani nikuma,yanda ka ganta nima haka na bude ido na ganta a kaina ta saka min wuƙa a wuyah"
"Wuƙa kuma mekika mata haka"
"Ina zan sani,inaga danna yiwa innarta kashedin zamukai ƙarane shiyasa,da Alama kasheni tazoyi"
Suna cikin maganar ne Bombee ta tashi ta tsayah tana jujjuya wuyah inda mlm idi ya ɗan sameta.
Hasketa yayi da fitilar hannunsa,take kuwa idonta yakama hasken fitilar,lokaci ɗaya shima yakoma tamkar fitilar dan haske.
Murmushi Bombee tayi jin yanda suke bada sautin mamakin abinda suka gani,amafani tayi da hakan ta wafce fitilar da take hannun mlm idin.
Maida hasken tayi kansu tana enjoying tsoron dayake kan fuskarsu,wanda yake sauƙar mata da nishadin a cikin ranta.
"Hhhhhhh daga kallon idona harkun razana dayawa haka,ohh dama duk gulmar da kuke yaɗawa akan idonnawa na mayune,bakuma gama saninsa ba.
Wani abun dazai ƙara baku mamakin shine,bakwa tunanin yaakayi na fito daga gidanmu da wannan duhun har nazo nan batareda fitila ba......saboda inagani a duhu tamkar rana.
Mai zai faru idan na kashe fitilar ni ina gani ku kuma bakwa gani,sannan kuma ga wuƙa a hannuna?"
Tana gama fadin hakan kuwa ta kashe fitilar ƙitt,duhu ya gwauraye ɗakin,wani irin ɗurar ruwa cikin gaji yayi,sai karkarwa take tana hada gumi.
"Hmm baban Zulaiha ka ajiye wannan itace takake saitawa,ohhh baka yarda dani ba danace ina kallonka,ko na fara faɗamaka a duk lokacin daka motsa,ko kuma idonka ya ƙifta?"
"Wannan ƴa kekuwa mutum ce?"
"Nima ban tabbatar ba tukunna,saidai ku kunriga kun yanke hukunci ai,cewa ni mayyace ina koh?"
"To ina wani abu kike,meyasa kika tsallake gidaje dayawa kika shigo mana nan,mai muka miki,sannan mai kike nema"
"Hhhhh abu daya kuka min sannan abu biyu nake nema.
Innar Zulaiha taje har gida taciwa innata mutunci,dan kawai narama abinda ɗanka bello yayimin,har tana cewa zatakai kotu.
Abinda nakeso shine ta fasa kaiwa ƙarar nan,sannan kuma babu ita babu gidanmu,idan su bello sukayimin abu kuwa babu mai hanani ramawa.
Wannan shine abinda nake nema,inkuma naga sabanin abinda na nema,zan dawo watarana,inna dawo kuwa duk ɗakinnan sai yankaku kuna bacci baku sani ba,kuma bazan bar shaidar ninayi ba,ko an kamani ma kukam kun tafi ai"
Ta karisa maganar tana dariyah.
"Munji hakan ma bazata faruba aniyarki tabiki,dan Allah kuma ki ƙyaleni nida ƴaƴana,yau na yarda ke wacece kam"
"Yarjejeniya ta ɗauru,ni barina tafi gida kar a gane bana nan"
Tana faɗin hakan ta fita daga ɗakin,hankalin ta kwance aikin ta ya kammala.




An dawo labari.........




Tunda wanann abin yafaru babu yaran dayasake tsayawa a hanyar Bombee,komai ta fadawa yaro da sauri yake yi babu bata lokaci. A da itace ke shan azaba a wajen yara,amma yanzu tashi ɗaya ya juyah itake zaluntarsu,idan yayanka ya daketa tasake kamaka ta dakaka,haka za'ai tayi har sai kahana yayannaka da kanka,uwar ɗa ma idan taga abin yaƙi dole ta zubawa sarautar Allah ido.
A makaranta kuwa tana shiga aji zayyi tsit,lokacin da takejin yin magana haka zata saka su suna bata labari,idan bataga dama ba babu wanda ya isa ko motsin kirki yayi a ajin.
Ta daina jarrabawa,karatu kam da su jinga ba'a magana,bata komai saidai tazo ta zuba tantirancinta ta tafi gida.
Bata cikin prifect ɗin makarntar,amma hatta head boy saitaga dama yayi abu.
An sha kaita office ɗin head master za'a koreta. Haka zata ce idan aka koreta saita bunkawa office ɗinnasa wuta da daddare,haka dole suka rabu da ita,a samu a tama gama kowa ya huta.
Shiyasa maganin hakan kowa ya daina shiga harkarta,take cin karenta babu babbaka.
Shirye shiryen fara exam ɗin common akeyi a makarantar su,tun waccan shekarar tayi da ƴan ajinsu bata ciba,hakanne yasa mlm Ahmadu sakata akan tasake jarrabawar,yayi niyyar makarantar kwana zai kaita kowa ya huta,shima ya huta da karbar ƙararta,dan abin ƴar tasa yazama sai zubawa sarautar Allah ido. Suje can suyita mata horo kowa ya huta.






Forseen




........"kee Bombee yanzu dan zabar baki ɗaukeni da daraja ba,ashe dana sakaki kije ki zana jarrabawar bakiyi ba,kika cemin kuma kinyi?"
"Danajene an gama shiyasa"
"Hmm to shikenan,ki rubuta ki ajiye,aure zan miki kawai na huta dake,tunda kinƙi karatu saiki tafi gidan miji?"
Ƴar dariyar tayi irin bata ɗauki maganar da ɗumi ba kafin tace.
"Aure kuma baba wai niɗin?".


😁😁ya kukace toh mutanen bombee?😁😁










____****🖤🖤****_____




🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤




🖤 _BOOK1_ 🖤






Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama'are_ ]










*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03


*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna


______________****_______________










Page 🖤20🖤












"Nayi wa headmaster ɗinku magana,kan cewar zakije kosake rubuta common,tunda wancan din sun bata miki ita saboda tantirancinki,na roƙeshi ya yarda,dan haka ki shiryah kije ki rubuta,idan kinci zan turaki makarantar kwana"
"Baba waini bokonnan dolene ne,duniyar ma fah takusan tashi kowa yasan inda zai shiga"
"Yanzu duk abinda nayi haka kika ce,wai tukunna ma kinji mai nacene.
Idan duniyar ta tashi ai irin bakwa cikin rabo,ki faɗamin wane abin arziƙi kikeyi guda ɗaya da za'a shaideki da ita"
Yamutsa fuska Bombee tayi tareda tashi daga tabarmar mlm Ahmadu.
"To shikenan baba zanje nayi jarrabawar tunda haka kakeso,babu matsala"
"Yawwa uwata kin kyauta,gwanda kiyi karatu hakan zaifi kyau"
Tundaga wannan zancen mlm Ahmadu yayiwa headmaster maganar jarrabawar tata,ranar daza'a yi kuwa ta shiryah tasaka uniforma ɗin da mlm Ahmadu ya ɗinka mata,dan cewa tayi fafur bazata saka tsoho ba wanda aka aro mata a anguwa.
Dole sai sabon akayi mata,idan tasaka saita bawa innayi shi.
Fitowa tayi daga ɗakinnasu ranar jarabawar,tasha sabon uniform da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login