Showing 45001 words to 48000 words out of 85666 words
Chapter 16 - BAZAWARA CE ITA COMPLETEHAUSA NOVELS BY .txt
d'in Yana kammalawa yahaye sama.
Washegari
JUHAIFAH Saida tagama baccin ta kafin tafito lokacin har karfe 11 tayi,tafito batareda tajire rigar baccin jikin taba,can tahangoshi zaune cikin parlour yatasa laptop gaba.
Asannu tazo tawuce shi tashiga kiching,tafara had'a afunda za'tayi break dashi,can tafito Liti dake mopin in steps yy saurin durkusawa daga inda yake yace "inakwana hajiya."
Tace "lfy Lau Liti."
Tawuce takoma bedroom,
zuwacan takuma fita lokacin Liti yagama mopin yasauko Yana rufe kufar toilet daya wanke bai rufeba.
Yana ganinta yace "hajiya zanshiga nayi gyaran d'akinki."
Tace "ok zomujema nanuna maka inda drink yazuba jiya kashare balallai bane ka'iya ganin gurin Dan lungune."
Yace "to. tareda bin bayanta.
Wata uwar tsawa MAHFUS yabugawa Liti Wanda yasa hanjin cikin Liti kad'awa bashi kad'aiba harda JUHAIFAH tada d'aura hannu kan handle tana kokarin bud'e kofar,bashiri tasaki handle d'in tajuyo jikinta nacirawa.
Cikin tsananin bacin Rai MAHFUS yace wa Liti "zonan!."
Yanuna gabansa,
Jikin Liti nacirawa yayazo yazube gabansa, yamike tsaye yashiga nunasa da yatsa yafara magana' kamar zai rufesa da duka cikin kakkausar murya yace
"Daga yau idan kashigo kaga mutane acikin parlourn Nan banyarda kayi aikinba harsai mutanen sunbar ciki kafin,kokuma karika zuwa da sassafe kanayin aikin naka,haka aikin Rana da yamma sai ka tabbatar da Babu kowa kafin kashigo."
Liti yarika gyad'a kansa cikin matsananin cin tsoro yana fad'in "insha Allah Alhj za'a kiyaye."
Cikin tsawa MAHFUS yakuma cewa "Kai nasauke aikin d'akinta akanka daga yau! Idan bazatayi da kantaba tabari!, tashi kayi gaggawar b'acemin dagani!."
Dasauri Liti yamike yy hanyar waje haryana cinkaro.
Yajuyo inda JUHAIFAH take yakuma tamke fuskarsa cikin d'aga murya yace "wannan iskancin ba'agidan Nanba idan zakiyishi kije can wani gun Amma ba acikin gidanaba,Kuma daga yau idan nakuma ganinnki da irin wad'annan kayan sainayi mugun tsab'a Miki!meye tunanin ki nakiransa cikin d'aki?."
Binsa da kallon mamaki take sai gaba d'aya ranta yamaci "cikeda tsiwa tace "duk abunda kk tunani acikin ranka to Nima shi natunano."
Tafad'a tareda murgud'a Masa Baki da waro manyan idanunta.
Yace "Ok to bazan sake ganin kaxanta nabiyu acikin gidanaba saidai kutafi can kan titi kamar yadda yafaru, wlh nadai fad'a Miki duk sanda nasake ganinki da wad'annan kayan Hmm."
Yy kwafa tareda komawa yazauna,
Murgud'a Masa Baki takumayi tawuce cikin bedroom.
Taje tayi wanka tafito tashirya cikin riga da sket,
Harta zauna tanuno ashefa tazuba dankali cikin mai,"watakimaya yakone."
Tafad'a tareda mikewa dasauri tafito,tana bud'e kofa yad'ago kansa yakalleta,niyyarsa idan Kuma fitowa da kayan tayi wlh irin bugun dazai Mata yau sai Allah yasani,Koda yaganta dawasu kayan daban sai yamaida idonsa kan abunda yake,
Aransa Kuma Yana fad'in "shima wannan in bashida banbanci Dana d'azu yarinya kamar 'yar Tasha."
Tawuceshi tashege kiching dasauri Koda tashiga kiching in tadadda Dan kalin yasoyu
sosai Amma bai koneba takwashe, tasoya kwai tahad'a tea tad'ebesu tafito tawuce bedroom inta,
tsaki MAHFUS yaja yamike yahaye sama.
★★★
Bayan kwana bakwai
Duk kwana kinnan MAHFUS haka yayisu batareda yasa wani kwakw kwaran Abu acikinsa ba, ruwan tea kad'ai yakesha,koyaje hotel da zummar cin abinci saiya tuno lokacinda yasami gashi cikin abincin dayasiya, saiya fasa siyan abincin yadawo gida yasha tea insa yakwanta.
dan yasan koyaje gidan Mommy ma babasa zatayiba Dan yaje har sau biyu bayan zuwansa nafarko amma tace Bata bashi yakoma gida yaci agidansa tunda yanada Mata.
Shikuwa yace dayaci abin cinta gara yacigaba da rayuwa da tea.
Shirye-shiryen barin kasar yashiga yima gabad'aya batareda Daddy yasaniba,
Yashirya komai karfe 10 nadare jirginsu zata tashi,
karfe 9 yagama duk abunda zaiyi,yad'au makullin matarsa yauko kasa,Yana Isa tsakiyar parlourn tana fita daga cikin kicking suka had'e atsakiyar parlourn,
Sanye take da rigar bacci riga da wando rigar da wandon duk tsawonsu d'aya d'an kasan guiwarta kad'an yatsaya mata,gashi sunbi sun lafe ajikinta.
Kokarin wuceshi take yadakatar da'ita tahanyar fad'in "bance kada nakuma ganinki da irin wad'annan kayanba?."
Yafad'a fuskarsa ad'aure,
Cigaba da tafiyarta tayi tana fad'in "shikenan inzan kwanta bazansa kayan bacci ba saidai nakwanta da kayan Dana saka tuntuni kenan,nigaskiya ban sababa."
azafafe yanufota tareda fincikota tagaru da kirjinsa,d'ankwalin kanta yafad'i kasa gashin ta dake atsefe yabazu yarufe fuskarta,d'an Kara tasake tana fad'in "menamaka Ina ruwanka dani?."
Hannu yasaka yadamke gashin kanta dakarfi yasaka kafarsa kan kafarta kamar yadda yasaba yimaba yamurkushe kafar nata,Kara takuma fasawa tarirrike rigarsa da hannayenta biyu tana juyakai cikin Jin azaba.
Kamar maiyin rad'a yakawo bakinsa saitin kunnenta yace "idan nakuma ganinki dashi saina had'a dakeda kayan nayagaku duka."
Yana kaiwa Nan yasaketa' tareda tureta ajikinsa yasakai yafice.
Zub'ewa tayi agun tarike kafarta tana kuka cikin muryar kuka tace "Allah ya'isa mugu soyake yaciremin yatsu shiyasa kullum yake takemin kafa."
Tasha kukanta azaune agun daga bisani tamike tagashiga bedroom inta.
MAHFUS kuwa nafita yakira Tanimu Mai baiwa fulawa ruwa kasancewar ya'iya tuki yace yazo suje yadawo da motar.
Suna isa airport yabawa Tanimu keyn motar yajuyo gida shikuma yashige jirgi.........
08034690723
Mommyn To ce
🅿️16
Washegari Koda JUHAIFAH tafito parlour Bata ganshiba sai tayi tunanin bai fitobane,tawuce kicking tanafad'in "fitinanne dama yacigaba dazama ad'akin."
tagama duk abunda za'tayi har Takoma bedroom Bata ganahiba,
Yau kwana uku duk sanda tafito Bata ganinshi,hakan kuwa bakaramin dad'i yamataba Dan tahuta' da takurarsa,Saida duk sanda dare yy takanji tsoro idan tatuna cewa ita kad'aice acikin part d'in, dukda cewa Mai gadi nacan bakin get sauran ma'aikatan gidan suna nasu part d'in, Amma hakan baya hanata Jin tsoro.
Anayin sallar Isha zata kule d'aki bazata Kuma fitowaba sai gari yawaye.
Zaune take a parlour tad'au wayarta dake gefenta talalub'o numbern Ya Al'ameen tadanna Kira,Ya Al'ameen nad'agawa yace "Shalele karkice komai gobe insha Allah zakiganmu agidan ki."
Cikin muryar shagwab'a tace "katabbata?indanfa bahakaba Allah saina zo gida."
Ya Al'ameen yace "insha Allah gobekam bafashi."
JUHAIFAH tace "to Allah yakaimu,yauwa Dan Allah kuzomun dasu Hassan wlh har mafarkinsu nake."
Ya Al'ameen yace "suma kullum sai sunce akaisu gunki."
Cikin marai raicewa tace "shine ba'akawo sunba?Allah sarki My baby's kutaho harda kayansu."
Ya Al'ameen yace "to makaran tafa?saidai suzo sukwana goben tunda gube asabarce ranar lahadi sukoma da yamma."
Tace "ayya Ya Al'ameen ataho musu da uniform insu sai surika tafiya makarantar daga Nan Allah tsoro nakeji idan dare yy."
Ya Al'ameen yace "tsoro Kuma ked'ayace agidan ko mijin naki yy tafiyane?."
Aranta tace "oho Masa Koma Ina yaje shiyasani yayitazama can inda yaje in ma ni yafimin."
Afili Kuma cewa tayi "Eh."
Ya Al'ameen yace "to zamuzo dasu inyaso idan mijin naki yadawo saisu dawo gida."
Ta'amsa da "tom. Cikeda murna.
Washegari da sassafe tayi gyaran bedroom inta Wanda yanzu ita takeyi dakanta kamar yanda MAHFUS yafad'a,tana gamawa taje tad'aura girki cikin kankanin lokaci tahad'a lafiyayyen girki tana kammalawa taje tayi wanka tayi kwalliyarta tazauna zaman jiran isowarsu Ya Al'ameen.
Ganin tad'an jima dazama har lokacin bataga isowarsu ba saita d'auki waya takira numbern Ya Al'ameen,har wayar tagama ringing ba'a d'agaba, takuma danna Kira nabiyu shima harya katse ba'a d'aganba,saitayi wurgi dawayan akan gado tatura Baki gaba.
Karar bud'e get datajine yasata mikewa dasauri tazo jikin window tayaye labule tareda zuge glass in window, hango motar Ya Al'ameen tayi yashigo cikin gidan,dasauri tasaki labulen taruga aguje tayi waje,
Ya Al'ameen yadaidaita parking suka fito,takaraso inda suke dagudu tana fad'in " oyoyo Hassan oyoyo Hussain."
Yaranma dagudu suka taho suka rungume juna, tarika d'agasu tana cillasu sama suna dariya.
Aunty Rukayya tace "ku ya'isa haka, waisu kad'ai kika ganine kam?."
Dariya tayi tareda sauke Hussain data d'agoshi, taruko hannun Aunty Rukayya da Ya Al'ameen tace "Allah dukanku naganku,oyoyo Aunty Rukayya oyoyo Ya Al'ameen."
Dariya sukayi duka,
Saikuma taturo Baki gaba tanafad'an "Allah nayi missing in yarannan sosai."
Aunty Rukayya tace "to ai gaki gasu yanzu."
Dariya tayi tasaki hannunsu taruko hannun Hassan da Hussain,tajuyo inda Ya Al'ameen yake tace "inasu Ya Mujaheed in suke."
Ya Al'ameen yace "an kirasu Jabeer ne cikin gaggawa shine suka tafi Amma sunce zasu dawo musamman domin ki."
Kai tagirgiza tareda fad'en "ai badamuwa tunda yanzu sundaina Sona."
Tawani marairaice fuska kamar za'tayi kuka,
Ya Al'ameen yace "idan basu zo gidankiba basai kifasa tarawa Jabeer kayan lefen nasaba."
Tace "yauwa ai haka zan fad'a mishima anjima,
Kuzo kujenku ciki."
Tana rikeda hannun yaran suka shiga cikin parlour suka zazzauna, JUHAIFAH dai bakinta yakasa rufuwa Dan tsabar murnar ganinsu.
Sai wasa suke dayaran duk suka yayyar da pillown kujera kasa suna wurgin junansu dashi, Aunty Rukayya tadubesu tanafad'in "oh ni JUHAIFAH koyauahene Zaki girma dubi yadda kuka hargitsa cikin parlourn Nan yanzunna."
rike pillown da Hassan yawurgo Mata tayi tana fad'in "saikin Kuma haifomana 'yan uku kafin nagirma."
Aunty Rukayya tawaro ido tana fad'in " 'yan uku ai saidai kigani akanki Amma kam baniba,to biyunma yanakare bare uku,Allah yasadai dake akayi rainon kema kin tab'a kinji."
JUHAIFAH tamike tsaye tana fad'in "Babu wani wahala kedai kawai kihaifo Mana ko Ya Al'ameen?."
Ya Al'ameen yagyad'a Mata Kai Yana dariya,
Itakuma tasuce kicking.
Aunty Rukayya tajuyo takalli Ya Al'ameen ganin Yana dariya kasa-kasa,tace "um ta d'auka haihuwar wasace za'tayi bayani itama Nan gaba."
Ya Al'ameen yace "babu waninna yarinya tafad'a Miki gaskiya."
Tace "um indai irin wanna gaskiyarce banaso.
JUHAIFAH tafito d'aukeda abincin data shirya musu tadireshi sakiyar parlourn,tazubawa Ya Al'ameen Tamika mishi tazubawa Aunty Rukayya ma tamika mata,sai tazuba wani a plt daban tacewa yaran susauko suci,tare sukaci itada yaran,suna gamawa takwashi kayakin tamaidasu kicking,tadawo sukaci gaba da wasan dasuke.
Har lokacin sallar azahar yy Ya Al'ameen yatafi masallacin dake kofar gidan, JUHAIFAH da Aunty Rukayya suka shiga bedroom sukayi sallarsu.
Koda aka idar da sallar Ya Al'ameen yashigo gidan yace wa Aunty Rukayya sutashi sutafi, JUHAIFAH tace "ayya Ya Al'ameen kubari sai anjima mana."
Ya Al'ameen yace "Shalele unguwa zamu wuce daga Nan,sai wani karon kawai idan munsake zuwa."
Tace "tom.
Batawani damuba saboda tasan za'abar mata su Hassan,
Har mota JUHAIFAH tarakasu daga gun tad'auko kayan su Husain dake cikin motar,sukuma suka shige motar suka bar gidan tana d'aga musu hannnu.
Bayan fitarsu Ya Al'ameen su JUHAIFAH
Suka koma ciki, a parlourn suka yada zangonsu.
Koda dare yy JUHAIFAH yau batayi bacci da wuriba Hira da wasa sukarikayi da yaran
Saican dare sukayi bacci.
Tun zuwan yaran JUHAIFAH tasake harji take kamar agida take,gashi Mai takura matan bayanan Dan haka tadad'a samun guri suka baje hajarsu.
Kamar yadda MAHFUS yashinfid'awa Liti sabbin tsaruka na aikin gidan kuwa haka yake gudanar dasu,idan aikin safene da sassafe zaishigo kafin JUHAIFAH tafito zai kammala komai yatafi,haka aikin ranama sai ya tabbatar dabata parlourn sanna zaishigo yagyara ko Ina yakoma,haka na yamma shima yakeyi.
Ranar Monday
Da sassafe tatashi tashiga kicking tafara had'amusu kayan break,tana kammalawa tazuba musu Wanda zasuci yanzu takuma zuba musu Wanda zasutafi dashi School, takomo bedroom tatada yaran taje tayimu wanka,Koda tagama musu suka fito tashiryasu cikin uniform insu,taruko hannunsu suka fito parlour,tazaunar dasu sukayi break,
Suna gamawa takamo hannunsu suka fito waje.
Can tahango Liti sunkuye Yana wanke bakinsa,daga inda take tsaye takwad'a Masa Kira,dasauri Liti yamike yataho inda take yadurkusa gefe da'ita,
Yana fad'in "gani hajiya."
Tace "Liti ka iya motane ne?."
Liti yace "a'a hajiya ban'iya tukiba,ammadai Tanimu shi ya'iya."
Tace "ok Ina Tanimun yake?."
Yamike dasauri taredafad'in "Bari nakirawo sa Yana ciki,yashige part insu bajimawa suka fito shida Tanimu,durkusawa Tanimu yy yagaisheta ta amsa, yy saurin sa hannu a aljihu yaciro key yamika Mata yanafad'in "Hajiya ga key in motar Alhj kwata-kwata nagama mancewane bankawo Miki makullin motarba."
Tace "ok karike kad'au yarannan kakaisu makaranta."
Yace "to wace makaran tace?."
Tafad'a Masa sunan makarantar, dasauri yamike yaje yafito da motar yazo dashi kusa dasu tabud'e sit d'in baya tasakasu,tana d'aga musu hannnu Tanimu yaja motar suka bargidan itakuma takoma ciki.
Idan sukatafi tun 6 nasafe sai 6 nayamma suke dawowa,
Kafin sudawo tashirya musu duk abunda suke bukata,
Koda lokacin tashin nasu yy kusa tafita tacewa Tanimu yaje yad'aukosu.
JUHAIFAH tacigaba da rayuwarta dayaran acikin gidan ranar Saturday and Sunday suyita bidirinsu agidan.
Ab'angaren su Mommy kuwa, ganin MAHFUS yadaina zuwa gidan saitayi tunanin yanzu yanutsar da kansa guri guda kenan yahakura yanacin abincin matar tasa, saidai takan d'an damu ganin yad'au lokaci baizo gidan nasuba,wata sashi nazuciyarta kuwa takan kawo Mata tunanin cewa nutsar da kansa dayayine yasashi rashin zuwa kwana biyun.
Daddy ne tafe cikin shirinsa nazuwa Office Mommy na biye dashi tana yimasa rakiya hargun mota takaishi tayimasa Allah yatsare, tajuya zata koma Daddy yy saurin dakatar da ita tahanyar fad'in "am wainikam rabon yaronnan dazuwa gidannan yau sati nawa?koyana zuwa abayanane?."
Mommy tace "ai yakai sati uku rabonsa da gidannan."
Daddy yy murmushi Yana fad'in "Son kenan Dan anyi Mata Kuma sai agujemu ni ko awayanma yanzu baya kirana,Bari ni nakira shi tunda yamance damu."
Yasaka hannu a aljihu yazaro wayarsa yashiga yalalub'o numbern sa, number ne harguda goma nakasashe daban-daban masu d'auke da sunansa,
Kan numbern sa na Nigeria yatsaya tareda danna Kira yakai wayar kunnensa,jiyayi ana fad'in Masa wayar tana kashe, yad'ago wayar akunnensa yakuma Danna d'ayan numbern nasa,shima kuwa akayi rashin sa'ar arufe take,da mamaki Mommy keduban Daddy dayaketa faman dannan numbern sa na Nigeria,haka kawai jikinta yabata cewa baya kasar tun Kiran layinsa nafarko da Daddy yy,
Mommy tace "Alhj kadaina Kiran layinsa na Nigeria kakira nawata kasar dai."
Tunkan Mommy takarasa maganar yadanna numbern sa na kasar UK Dan yafi tunanin Yana can d'in, ga mamakinsa kuwa saiji yy numbern tana ringing, Daddy yagyara tsayuwarsa dakyau Yana zaman jiran aukar kiran. wayar har takusa tsinkewa kafin aka d'aga,muryar MAHFUS yasinkayo tacikin wayar Yana sallam.
Da mamaki Daddy ya'amsa sallamar' tasa, MAHFUS yace "barka darana Daddy."
Daddy yace "mu bamukaiga ranan ba tukun."
Yace "sorry Daddy namance ne."
Daddy yace "Son banace hutun wata biyu nabakaba?shine zaka zame jiki katafi batareda nasaba."
MAHFUS yace "sorry Daddy idan nacigaba dazama har natsawon wata biyu Allah ayyuka zasuyimin yawa har narasa yadda zanyi,nazone in d'an rarrage ayyukan sai indawo."
Daddy yace "to shikena Amma dai kadawo dawuri kada ashiga hakkin yarinyarnan."
MAHFUS yace "to acikin satinnan ma zan dawo."
Daddy yace to "Allah yataimaka."
Yace "Amin."
Sukayi sallama Daddy yasauke wayar,
Mommy tayi saurin cewa "lallai yaronnan ma bashida hankali yaushe-yaushe ne akayi bikin dahar zai sakafa ya tafi, fisabilillahi yanzu ita kad'ai yabarta agidan?."
Daddy yace "ai yace zaidawo acikin satinnan so inaga ai bawata damuwa bace."
Mommy dai girgiza Kai kawai tayi Dan tasan saranar MAHFUS saidai kawai randa Allah yy.
Daddy yashige mota driver yaja sukabar gidan,
Mommy Kuma takoma ciki.
Tana shiga d'akin' Zahra tashiga tasameta kwance Mommy takaraso cikin d'akin tadubi Zahra tace "taso kije gidan Yayan ki kiduba JUHAIFAH tana lfy dai ko."
Zahra tace "tom tareda mikewa tasauko daga kan gadon,
Tace "Mommy wani abunne yasami Aunty JUHAIFAH'n?."
Mommy tace "sonake nasan halin datake ciki saboda Yayan ki baya kasar."
Zahra tace "ok.
Kasan cewar akimtse take gyalenta kawai tad'auka tafita, driver yakaita gidan.
Koda suka iso gidan tafito a motar tanufi ciki dasallma tashiga parlour,su JUHAIFAH suna zaune cikin parlourn JUHAIFAH naganinta tayi murmushi tareda fad'in "um Zahra saiyau?." tafad'a tareda rike hab'arta,
Zahra tayi dariya tereda karasowa ciki tazauna saman kujera,
Tana fad'in "kibari kawai Aunty JUHAIFAH School ce kawai yake hanani zuwa ko'ina."
JUHAIFAH tace "har ranar Saturday and Sunday ma duk zuwa School in kk?."
Zahra tace "inazuwa islamiya aranakun ai."
JUHAIFAH tagirgiza Kai tace "kwana kk amakarantar?."
Zahra tayi dariya tareda fad'in "Kai Aunty JUHAIFAH duk inda mutum yabi saikin taroshi,todai ayimin afwa."
JUHAIFAH tace "ai Daman nasan bakida wata hujja."
Zahra tayi dariya,
JUHAIFAH tamike taje tawako Mata abun Sha,
Hira sosai sukayi sai yamma lis Zahra takoma gida.
Koda ta'iso gidan d'akin' Mommy tashige direct,Mommy nazaune takaraso cikin d'akin' tazauna kusa da ita,
Mommy tadubi Zahra tace "sai yanzu?."
Zahra tace "Eh Mommy."
Tace "to yakika Sami JUHAIFAH'n?."
Zahra tace "wlh lfy Lau nasameta,nasametama tareda Twins innan dasuka kwana tare anan."
Mommy tace "to madallah ai su yaranma zasu iya d'ebe Mata kewa dai-dai Dan naga sun shaku sosai."
Mommy tad'au wayarta tana cigaba dafad'in "barima nadad'a tabbatar da dawowan nasa."
Zahra tamike tayi d'akinta.
★★★★★★★★★★★★★★★★
2 month later
Tun tsawon lokutannan JUHAIFAH suna tareda Hassan da Husain,tamance dawani MAHFUS Dan Dama baya gabanta.
duk sanda Ya Al'ameen yakirata akan cewa za'azo ad'auke su sai tasakamasa kuka tace to saidai in zasu koma gida tare.saiyace a'a suzauna Amma dasharad'i idan mijinta yadawo za'azo ad'ebesu,tace tayarda.
Ba Mommy kad'aiba yanzu harda Daddy lamarin MAHFUS yafara damu,kusan kullum sai Daddy yakirasa akan yadawo Amma saiya ce Masa zaidawo acikin satinnan,an Kuma shafe sati nawa Amma bashi ba labarinsa.
Yaukam Daddy gabad'aya ransa ab'ace yake lalub'o numbern MAHFUS in yy yadannan Masa Kira, Yana d'agawa Daddy yace "Kai MAHFUS me kakeson maidamune kam? aure sati d'aya katafi kabar matar har kakai kimanin watanni biyu bakanan,arabo yarinya da gidansu a'kaimaka ita gidanka a aje,katafi kabarta koshin maigadi ce ita,
To wlh Ina Mai tabbatar maka dagayau zuwa gobe idan baka dawoba zan sakata ajirgi taje inda kake d'in...............
08034690723
Mommyn Twins ce
🅿️17
Zunbur MAHFUS yamike zaune Jin abunda Daddy yafad'a,
Allah yasawake yabari tazo shi yayarda zaidawo Nigerian ko ma menene sukare acan,Amma bai amince dazuwan nataba.
dasauri yace "Daddy basai an turo taba gobe insha Allah Ina hanya"
Daddy yace "nidai nafad'a maka idan bakazoba zan sata ajirgi taje inda kk."
Daddy yakashe wayarsa,
MAHFUS yabi wayar da kallo cikeda kunar Rai waishi meyasa akeson takurawa rayuwarsane Kuma yalura duk abubuwan da ake Masa akantane ake takurashin Nan Wanda da ba'ayi Masa hakan.
Yy kwafa tareda taunar lips insa.
Wayarsa yad'auka yy dilling wata number ana d'agawa yace "ashiryamin zuwa Nigeria gobe nakeson Isa idan Allah yakaimu."
bai jira amsar Wanda
yakiranba yakashe wayar,mikewa yy tsaye Dan gabad'aya saiyaji kwanciyar ma ta'isheshi,yazauna bakin gadon sai girgiza kafa yake kasar zuciyarsa kuwa bakin cikin JUHAIFAH ce falciki.
Washegari yahayo jirgi yanufo Nigeria.
Ab'angaren JUHAIFAH ko kasan cewar yau Sunday ne Hassan da Hussain suna gida, tunda sukayi wanka sukayi break suka kule d'aki,Gem suke bugawa a wayarta idan wanna yayi yafad'i sai aba wanna shima yayi haka sukarikayi sunayi suna ihu da salle,
Mikewa tayi tasauko daga kangadon saboda Jin fitsarin datake tabarwa yaran wayar a hannunsu tanufi bathroom,
Tana shiga Husain yafizge wayar ahannun Hassan yanafad'in "nijan buga yanju."
Hassan yace "bakai bane nine Jan buga."
Yafad'a nakokarin karb'ar wayar ahannunsa,dagudu Hussain yasauko agadon yabud'e kofa yafita Hassan yarufa Masa baya aguje sukayi cikin parlour,sukarika zaga cikin parlourn Hussain narike dawayan kem, Hassan nabinsa yanafad'in sai yabaahi ai shine da bugu.
Ahankali yaturo kofa yashigo,harya karaso cikin parlourn basusan dashigowar Saba, tsayuwa yy Yana bin yaran da kallo, can Hassan ya ankaro dashi agun dagudu yazo yarun gumeshi yanafad'in "oyoyo uncle"
Jin haka Hussain yasaida gudun dayake ganin Hassan ya tukuikuyeshi yanata faman fad'in oyoyo uncle shima dagudu yataho ya rungume shi suna tsalle suna fad'in oyoyo uncle,da mamaki yake bin yaran da kallo,ganin yanda suketa faman rirrikeshi suna tsalle ajikinshi sunakuma fad'in oyoyo uncle,
Saiya d'an ja jikinsa yazauna kan kujera,
Aiko dasauri suka d'ale kan kafarshi sunata murna kamar wanda dama sun tab'a saninsa,
Hussain daya sakalo hannushi a wuyansa yace "uncle kakawo Mana chocolate?."
Hassan yatureshi yace "hum taci anan