Showing 24001 words to 27000 words out of 95354 words
Chapter 9 - BUGUN ZUCIYA Hausa Novels Complete by Fadila Lamido.txt
tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"
Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
Mama dan Allah kice bacci nake, nifa bansan mezance mai ba"
Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"
Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"
Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"
Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"
Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"
Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"
Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"
Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"
Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"
Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...
Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"
Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?
Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"
Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar, kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"
Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"
Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"
Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"
Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"
Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin nashi"
Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"
Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"
Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?
Kanta akasa tace eh"
Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
To me kika ce ? Ya miki ?
Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....
Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda kike so shi zan baki bazan miki auren dole ba da iznin Allah, inason nasan meye azuciyar ki game da jafar ?
Motsa baki tai tayi daker ta iya bude baki tace Abba ni banason shi"
Saboda me ? abba ya tambaya
Abba tsoho ne fah kuma yana da mata"
Murmushi Abba yayi kadan sannan yace ashe jafar ya cinka daidai, toh bakomai amman nayi miki sha,wan shi, dan yaro ne me mutunci da sanin ya kamata, haka iyayen shi mutane ne masu karamci, kuma bawani babba bane mamana, ko zai girmin usman bazai wuce shekara daya ba, amman ba komai tunda kince haka, gabe wani zaizo ki ganshi, kinji ko?
Saida gabanta ya fadi wato abba bazai bar mgn haka ba, da wannan tunanin ta tafi mkrnt ko wa Abba zai sake turo mata oho?
***
Akofar gidan su deeni ta hango samari cike, da alama yaran duna ne kome suke agurin oho, acikin su caka kawai ta sheda yanata fada yana daga hannu saidai har motan su ta wuce bata tsinci abinda suke cewa ba"
Ko a aji batai karatun kirki ba Allah2 take atashi break taje taga me akeyi"
Kawayen ta kallonta kawai sukeyi, domin sun kula akwai abun da ke damunta"
Ana buga kararrawa ta fito ta nufi gidan su deeni saidai yazun babu kowa akofar gidan"
Cikin gidan ta nufa tana tura kofar sukayi ido 4 da deeni, zaune yake kan kujera ummi tsugune agefen shi tana tsuma tsunma aruwa zafi tana dannan me ajikin shi"
Hunnu tasa ta mumtsuke idonta sannan ta sake sauke shi akan deeni, aguje tayi kansu, jinta kawai tayi jikin deeni ya rungume ta yana sumbatan ta"
Cikin sauri ummi ta dauke bokitin ruwan zafinta ta basu guri, jefe2 tana satan kallon su"
Sun dan juma ahaka ahankali asma'u ta zame ta koma gefe sannan ta zubawa deeni ido"
Shedan bulala ne ajikin shi rudu2 wasu guraren hadda ciwo, hawaye taji ya cika mata ido, nan danan suka fara zubowa acikin kuka tace nina jawo maka nasan bakowa bane yayi maka haka sai Jamal dan Allah ka yafe min"
Hannuta ya jawo ya riketa dakyau sannan yace....
Shine Asma'u amman karki damu yanaso ne wai ya nunamin shi Soja ne amman ba jarumi ba, wanna abin daya aikata ya nunamin be kai ba"
Kara karkace baki yayi sama sannan yace.....
Ai nagaya masa dan *uwas* data haife shi, idan yana jin yakai shege, ya goyo *uwassa* abaya, ya fadi ina zamu hadu, daban daban zasu koma gida"
Heart beat
*Mmn Yazeed*
Yayan ki *Jamal*
Mikewa ma'u tayi da sauri sannan tayi jifa da ledan " bantawa tayi tacire wayar acikin kwali dan haka ta dauki kwalin ta buga da kasa" sai lokacin ta kula dan haka ta dauki wayar ta makawa bango"
Ji kake tassss"
Da gudu ta fita ta nufi dakinta ta fada gado tare da saka sabon kuka"
Wato Jamal ne yaje har gida ya kama deeni ? Ko tantama batayi Jamal ne wani sabon tsanan shi taji axuciyarta ji take kamar ta kashe shi"
Tashi tayi ta zauna yanzun meye abinyi ?
Yaya zanyi inkubutar da deeni daga hannun Jamal
Mama ko mamakin hali irin na ma'u tayi sannan ta juya ta kalli bannan da tayi ta girgiza kai, cike da takaici ta fita adakin"
Da misalin karfe biyu da rabi ma'u ta fito cikin shirin tafiya mkrnt yamma, kallonta mama tayi taga idonta duk sun kumbura cikin idonta jawur sun kankance, da alamar ma ko cire kayan makaratar batayi ba tunsafe, dauke idol tayi akanta domin al'amarinta ya fara bawa mama haushi"
Saida ta turu baki tace natafi"
Ko kallonta mama batayi ba tace adawo lfy"
Kaitsaye gidan su deeni ta shiga, ummi nazaune ta tasa abinci agaba ta kasa ci"
Gabata ma'u ta zauna ta bude sabon kuka, hankalin ummi kara tashi yayi, rufe abincin tayi sannan tace ki daina kuka Asma'u bakiga inda fuskan ki ta kunbure ba, mutaru miyi hakuri inada tabbacin auta na zai dawo gida domin nasan shiba rago bane, wannan tashin hakalin da kika ganni ci narashin tabbacin inda yake ne da rashin sanin halin dayake ciki amman da yardan Allah auta zai dawo"
Dahaka ummi ta samu ta shawo kan ma'u, ta wuce makaranta"
Da daddare Asma'u na kwance afalo tana cigaba da tunanin deeni badan tana tunanin kar asirinta ya tonu ba data ansa no Jamal agun yaya usman ta bashi hakuri ya sakar mata deeni"
Tana cikin wannan tunanin taji sallaman yaya usman rufe ido tayi kaman me bacci, Allah2 take ya wuce amman saitaji ya zauna akujeran dake kallon nata"
Zuwacan mama ta fito tana fadin ka iso?
Eh naje gidan momy yanzun tacemin kina nema"
Zama tayi sannan tace eh Daman Asma'u ce gatanan narasa gane mata, kwashe duk yadda akayi tayi ta gaya masa"
Sannan ta nuna masa yadda tayiwa wayar da Jamal ya kawo mata"
Cike da baccin rai yace mama bawani abinda yake damunta banda iskanci da sangarta, bataga ba,a dukanta ba kuma ai ba wuce dukan tayi ba, dan ubanta Jamal din sa'anta ne
Usman na tsaka da fada Abba ya shigo, daga mama har usman sannu suke mai" amman abban yaki amsawa fadin yake ina Asma'u
Toh fah mama ta fada azuciyarta domin indai taji alhaji ya kira ma'u da sunan ta toh akwai mgn"
Itako ma,u tanaji Abba ya kira sunanta ta bude ido tare da sakkowa akan kujeran azuciyarta tace shikenan dada ta fadawa abba"
Kusa da ita abba ya zauna sannan ya rike hannunta guda daya"
Jikinta gaba daya rawa yakeyi"
Abba ko ido ya kureta dashi zuwa can yace, yau naje gidan malam idris na tuntubeshi game dake, ya nunamin komai lfy kuma kina karatu sosai yadda ya kamata, amman abinda ya bani mama cewa da yayi wai baki zuwa makaranta akan lokaci, bayan nikuma nasan kina fita gida da wuri"
Shiru Abba yayi yana jiran yaji me zata ce"
Jita shiru yasa yace badake nake mgn ba"
Kanta akasa tace Abba wlh ni babu inda nake zuwa"
Amman kinsan malam idris bazaimin karya ba ko?
Nasani abba, amman ni daga nafita wlh tallahi banazuwa ko ina sai makaranta, sai dai idan kafin naje lokaci yake kure ....
Cikin ido abba ya kalleta sannan yace bari rantsuwa, ai bacewa nayi ki rantse ba, bakomai daga yau drive zai dinga kaiki makaranta, idan lokacin tashi yayi zai dawa ya daukeki, haka yayi ko ?
Daga kai tayi badan ranta yaso ba"
Juyawa abba yayi ya kalli usman sannan yace kaikuma me kazoyi da daddaren nan ?
Cikin natsuwa ya fara fada mishi komai kamar yadda mama tafada mai, sannan ya kara da cewa abba ya kamata adauki mataki akanta be kamata azuba mata ido tanayin abinda taga dama ba"
Shiru falon yayi zuwa can abba ya nisa sannan yace...
Ke !! Asma'u wani abu na damun ki ne?
Cikin sauri ta girgiza kai tare da fadin a'a"
Akwai wani abunda kikeson ne ko kike son a saya miki ?
Nan ma a,a ta sake cewa"
Shiru abba yayi sannan yace....
Ninasan abinda ke damun ki, Aure ne baki so, kuma bazai yiyoba, tun ranan dana miki mgnr aure kika fara koke2 ita kuma dada ta biye miki har tana taya Ki, bazan kara kaiki gidan ba bare ki kara sata kuka"
Juyawa yayi ya kalli mama sannan yace wlh tun ranan danakaita gidan, dada na nan babu lfy, yanzun jiya nakaita asibiti sunce jininta ya fara hawa"
Juyawa yayi ya kara kallon asma,u sannan yace ki shirya gobe zakiyi bako, ni ba nufina namiki auren dule ba, a'a zaizo ne ya ganki, kema ki ganshi, idan kun daidaita shikenan, idan kuma baku daidaita ba zan sake turo wani, bana bukatar kice wai saikinsa halinshi, duk wandan
kikaga na turo miki na yadda da inganshi tare da mutuncin iyayen sa, dan haka kwana 2 kawai na baku, ganin inda tayi shiru yasa abba fadin kinajina ko ?
Kai kawai ta iya dagawa sannan tasa hannunta ta share hawaye"
Tattaunawa suka fara tsakanin mama da abba tare da yaya usman, haka ne yabata daman tashi tabar musu falon"
****
Washegari ma'u ta tashi da matsanan cin ciwon kai, saka makon rashin baccin da batasamu, taso taki zuwa mkrnt amman kuma tanason taga halin da ummi take ciki, dan haka ta mike tahau shiri"
Drive ne ya kaita har bakin mkrntr sannan ya juya, dan kaka bata samu daman zuwa gidan su deeni ba saida aka tashi break"
Xama sukayi jugum ita da ummi kamar masu zaman makoki"
Bayan antashi makaranta abba da kanshi yazo ya dauketa"
Koda ta shiga gida a kitchen ta samu mama tanata soye2 sai alokacin ta tona da bakon da abba yace zaizo"
Yatsuna baki tayi sannan ta juya ta shige daki, wanka tayi tai sallah sannan ta tsaya tai addu'a sosai Allah ya kubutar da deeni daga hannun Jamal"
Tana zaune kan sallayan mama tashigo tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"
Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
Mama dan Allah kice bacci nake, nifa bansan mezance mai ba"
Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"
Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"
Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"
Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"
Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"
Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"
Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"
Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"
Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"
Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...
Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"
Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?
Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"
Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar, kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"
Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"
Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"
Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"
Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"
Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin nashi"
Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"
Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"
Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?
Kanta akasa tace eh"
Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
To me kika ce ? Ya miki ?
Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....
Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda