Showing 84001 words to 87000 words out of 95354 words

Chapter 29 - BUGUN ZUCIYA Hausa Novels Complete by Fadila Lamido.txt

29 Oct 2025

493

Lallai idan mutum ya rasa me masa fada ya shiga uku, tabbas Jamal bashi da makusa yana yin abubuwan shi kamar daddyn sa"

Duk cikin zuciyar shi yake wannan tunani tare da daukan alwashi insha Allahu zaiyi aure ko bana soyayya ba, dan yaga ya mallaki yara ya basu tarbiya ba irin wacce aka bashiba"

Kallon daddy yayi yace daddy dan Allah kabar fadan nan, ni tun tuni na hakura da asma'u nacireta azuciyata, ba tun yauba, daddy ya zan yi na aure asma'u, bayan d'an uwana na auren ta, daddy kayi kuskuren cewa Jamal yabar min mata, wlh na barta har abada, dan Allah abani no Jamal nakirashi ya dawo gida, zama awani waje be dace dasuba"

Kowa afalon kuka yake yi ba mazan ba ba matan ba"

Daddy ne ya share hawaye sannan yace......

Ai be tafi da waya ba, dan dana kira naji karanta adaki"

Shiru deeni yayi zuwa can yace........ .


Daddy ina son nayi aure, nabaka zabi ka zabar min mata ko ya take indai ka amince da tarbiyan ta, inaso na haifi yara na musu tar biya ba irin wacce akamin ba






Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[24/01, 11:04 a.m.] β€ͺ+234 906 689 6652‬: πŸ’—πŸ’πŸ’πŸ’—
​*BUGUN ZUCIYA*​
( ​Heartbeat​)

πŸ’“πŸ’πŸ’—
πŸ’—

πŸ’“πŸ’πŸ’—
​By​
πŸ’—
​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🀝*




1⃣0⃣2⃣






Jamal bana wasa dakai, karkace zakayi jayaya dani, kuma wannan mgnr bana son wani yajita tsakanina ne ni dakai"

Daddy dan Allah ka jayen wannan mgnr, wlh daddy bazan iyaba, bazan iya rabuwa da Husna ba, daddy idan nabarta zan shiga wani hali"

Jamal koma waning hali zaka shiga baxai kai wadda shamsu yake ciki ayanzun ba, bana son nakarajin komai daga gare ka, takarda na nema kuma ita nake son kabani"

Kara dukar dakai Jamal yayi, sun dauki lokaci ahaka sannan daddy yace......


Jamal wlh zan bata maka ranka"

Cikin zuciyar shi yace.....


Raina ya dade da bacci daddy"

Cigaba daddy yayi da cewa, zakai abin da nagaya maka ko kuwa?

Murya kasa kasa yace daddy kayi hakuriπŸ™πŸ»

Wlh Jamal zan iya tsine maka"

Kallon daddy yayi da sauri sannan ya maida kanshi kasa yace......

A'a daddy kar kamin haka, dole ce tasa na maka musu daddy ba'a son raina bane, daddy idan na saketa rayuwata zata zama cikin hadari, dan gaskiya inasonta sosai babu rabuwa atsari na, kuma itama tana sona"


Cikin daure fuska daddy yace bantabaye ka wannan ba, kaida shamsu nasan kuna da babbanci kai mutum ne me tawakali da kaddara mekyau ko mara kyau, shamsu bayi dashi, ba'a daura shi akan wannan tarbiyan ba, banaso ya mutu, inaso yayi rayuwa kamar kowa"

Kunya ce ta fita a idon Jamal kwata kwata, tsintan kanshi yayi yana fadin daddy wannan ba kaddarata bace, bazan iya kashe kaina na raya wani ba, Allah ne ya bani Husna, batare da naje neman aurenta ba, duk da cewa na dade ina sonta bantaba nunawa kowaba har usman, kuma ni na sani deeni bawani sonta yake ba, wlh nafishi sonta, yana ikirarin yana sonta ne saboda besan menene so ba"

Itama kanta taso deeni ne cikin yarinta alokacin da batasan me take ba, na tabbata ayanzun Husna bazata so deeni ba"

Daddy idan kace lallai saina saketa bakamin adalci ba, Allah ne ya bani ita batare da yayi shawara da kowa ba, haka kuma Allah ne ya kaddara asma'u ba matar sa bace, dame bazai yi hakuri da hukuncin Allah ba, lallai ne abin da yake so saiya samu?, daddy karku shiga hurumin daba nakuba, deeni ba mutuwa zaiyi ba, darasi ne Allah yake nuna mishi, daddy idan ma muwa zaiyi sakin husnan dakace nayi zai kara mai kwanaki ne? Dan Allah daddy munar Allah yayi hukuncin shi, munemin zabin alheri agurin shi kawai"
Jikin daddy sanyi yayi sosai, shiru yayi na dan wani lokaci zuwa can ya sake cewa.....

Jamal nasani duk abin da ka fada haka ne, shiyasa ako ina nake alfahari dakai, amman kayi yadda nace d'in"

Wani irin yar fa hannun Jamal yayi, sannan ya rungumi hannuwan shi akirji"

Ganin haka daddy yace nakara ma lokaci nanda zuwa gobe ka yanke shawaran, zakamin biyayya ko kuma bijirewa umarni na"

Juyawa daddy yayi da sauri yabar dakin"

Yana fita momy ta fito daga dakin ta bayan daddy tabi da harara sannan taja tsaki ta nufi dakin Jamal"

Tana tura kofar ta hango fuskan Jamal hawaye shabe shabe"

Yana ganinta ya fara sharewa tare da boye idon shi"

Kusa dashi ta zauna sannan ta dago kanshi tace......

Jamal karka tada hankalin ka, bare har ka biyewa zancen mahaifin ka, idan har ka saketa bazan taba yafe maka ba, karka manta, nima ina da hakki akan ka"

Cikin rawar murya yace toh momy ni yanzun yaya zanyi?

Ka dage mishi akan kana son matar ka, ni bantajin inda akayi haka ba, alhaji yana da wani irin son 'yan uwan shi, wadda ya wuce misali"

Jamal be sake cewa komai ba, idonshi ya dauke daga gurin momy ya juyar dashi can gefe, cikin tsananin damuwa"

Momy kokarin kwantar mai da hankali take, amman ta kula hankalinta baya gurin ta, yayi nisa cikin tunani"

Mikewa tayi tai waje tare da fadin Allah ya kyauta"

Jamal naganin fitan ta ya kira wayar ma'u, yauma kashe take kamar kullum, tsaki yaja gashi bashi da no mama"

Wata zuciyar ce tace, ka kira usman, wannan tunani yasashi ya kira layin usman

Zuwa can aka daga usman ne yace gauro ya gari?

Cikin rashin kwarin jiki Jamal yace babban yaya ka huce kenan?

Dariya usman yayi tare da fadin aini daman ba zafi nayi ba"

Kayi fushi mana tinda ka tafi babu sallama, ya gida ya iyali?

Lfy lau suke, karkace min asma'u bata gaya maka fa'iza ta haihu ba"

Yake Jamal yayi kamar yana gaban usman yace da gaske?, me muka samu?

Nana Firdausi, usman ya fada cike da murna"

Allah ubangiji ya albarkanceta acikin addinin musulinci, kace inanan nasake baki nayi 'ya ban sani ba"

Dariya usman yayi tare da fadin wlh jiya da dare ta sauka, na dauka Asma'u zata gayama ne"

Karka karamin haka, ko Husna zata fadamin yana da kyau kaima naji daga gareka, amman bakomai tunda Husna taganta kamar nine"

Hmmm wlh Jamal kana min rashin kunya fah, ya jikinka najika wani iri ne"


Eh wlh bana jin dadi ne, dan hadani da husna mana"


Tsaki usman yaja sannan yace batanan gidan kuma basu dade da tafiya ba ita da mama"

Shiru Jamal yayi zuwacan yace toh sai an jima"


Kashe wayar yayi tare da binta da kallo, lallai yanason suyi waya da husna ayau, dan haka ya yanke shawaran kiran daddy"

Bayan sun gaisa da abba yamai barka samun karuwar da akayi"

Dariya abba yayi tare da fadin toh ai Jamal ku za'aiwa barka, kunji kunya tika tika daku sai yanxun kuka aje daya, daker"

Guntuwar dariya Jamal yayi tare da shafu keyarshi kamar yana gaban abba, acikin zuciyar shi fadi yake abba me kakeci nabaka na zuba"

Jim, sukayi zuwa can Jamal yace.........

Amm abba nakira wayan ta ne akashe, ban saniba ko wayar ta samu matsala ne"

Wai asma'u ?

Eh Jamal ya fada ahankali"

Toh, toh, ina zuwa"

Kashe wayar yaji anyi zuwa can yaji wayar na kara"

No Abba yagani, jikin shi har rawa yakeyi wajen daukan wayan"

Muryan ma'u yaji cikin murna da dauki tana rangada sallama"


Tsintan kanshi yayi da lumshe ido sannan ya amsa mata tare da fadin Husna shine kika yadda kika tafi ko sallama babu ko?

Toh ai momy ce tace haka"

Hmmm Husna toh ya kwana 2?

Lfy lau, ya jiki?

Yayi sauki Husna, yasu mama?


Suna lfy"

Yayi kyau"

Cikin siririyar murya asma'u tace....

Yaya Jamal albishirin ka"

Goro ya fada cike da zumudi dan tunda yake da ma'u bata taba sakar mai jiki kamar yauba"

Yar dariya tayi sannan tace.....

Fari ko jah?

Dariricewa yayi domin bazai ce ga takameme abin da ake cewa ba, tsintan kanshi yayi yana cewa jah"

Kukan shagwaba tasa kamar tana gaban shi, tare da fadin fari fa zakace"

OK toh ya isa kisan ban iya irin wad'an nan abubuwan ba, inajiki toh nace fari"

Cikin murna tace....

Na samu d'iya anty fa'iza ta haihu jiya da dare"

Yi yayi kamar be sani ba, ya lankwasa murya yace......

Dan Allah?

Wlh, yaya bakaga yariyar ba, kamarmu daya"

Har cikin jinin jikin shi yake jin muryanta dan haka ya kara kashe murya yace....

Da gaske?

Hmmm kai dai sai ganta da idon ka, wlh har giran mu iri daya ne"

Zanso inganta kuwa, kishafa min kanta, kice wani babanta na mata barka da zuwa"

Shiru sukayi nadan wani lokaci, zuwa can Jamal yace.....

Husna kina inane yanzun ?

Ina dakina"

Ke dawa?

Ni daya"

OK akwai mgnr da zan gaya miki, akwai wata babban matsala da ta tunkaro mu, daddy ya gindaya min umarni, wadda bazan iya biba, kinsan menene?

Girgiza kai tayi tare da fadin a'a

Ahankali ya fara warware mata abin da ke faruwa"

Kafin ya gama hawaye ya gama wanke mata fuska, cikin kukan tace........

Yaya Jamal nagaji fah, wlh nagaji tunanina bazai iya dauka ba, waini sai yaushe zanji dad'i inama na mutu tun ina kar.......


Wani tsawa Jamal ya buga mata wadda yasata yin shiru batare da ta shirya ba"

Kina hauka ne? Karna sakejin kin fadin irin wannan mgnr, duk inda kika samu kanki ki godewa Allah

Kuka take ahankali"

Shima hawaye ya share tare da ajiyan zuciya yace.....

Husna dan Allah karki yadda arabamu, deeni ba sonki yake ba, sha'awarki kawai yake yi, natabajin shi yana miki karyan banza da wofi, har yana kiran Ki da Furan sa, idan natuna inajin takaici, agidan ubanwa kika zama furan sa? Darajan Ki ta wuce ta fura, babu abinda da za'a kwatantaki dashi, yaudaran ki yaki yake, kuma ni tundaga ranan natsani fura
ko ganinta bana so yi"

Kosawa tayi yabar mgnr, dan tasan yana iya birkice mata, yanzu nan, dan haka tace....

Yaya Jamal kabar wannan mgnr"

Dif, yayi xuwa can yace.....

Husna daddy ya bani daganan zuwa gobe, nakawo mishi sakin ki, dan haka adaren nan zabar garin bazan dawoba sai daddy ya janye kudurin shi akaina, zabar wayata agida dan kada anemeni ke kuma Ki ringa barin wayarki akunne dan zan nemeki, idan na isa inda zan tsaya, sannan aurena nakan ki karki yadda da sako arubuce, ban rubutaba, kuma bazan rubuta ba"

Ban aiko kowa ba, kuma bazan aiko ba, karki yadda da kowa, idan bani kika gani idona da nakiba"

Kuka ta fasa, cikin kukan tace......

Yaya Jamal karka tafi ka barni dan Allah"

Husna nima ba'a son raina zantafi ba"

Cikin matsanan cin kuka tace toh ka tafi dani wlh zan bika.....








Heart beat
*Mmn Yazeed*​
[24/01, 11:04 a.m.] β€ͺ+234 906 689 6652‬: πŸ’—πŸ’πŸ’πŸ’—
​*BUGUN ZUCIYA*​
( ​Heartbeat​)

πŸ’“πŸ’πŸ’—
πŸ’—

πŸ’“πŸ’πŸ’—
​By​
πŸ’—
​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🀝*
​




*Masoya BUGUN ZUCIYA kuyi hakuri plsπŸ™πŸ»πŸ™ˆ abubuwa ne sukamin yawa, naso yau nabaku mamaki amman nakasa, gobe insha Allahu page 2 ko 3 zan turo, nagama typing editing ne ya rage, wadan da sukamin mgn ban amsa ba kuyi hakuri plsπŸ™πŸ» sakon ne yamin yawa*




1⃣0⃣3⃣





Indan katafi ka barni zan shiga wani hali bansan inda Zanyi ba"

Husna kiyi hakuri, nima bansan inda zani ba, kinga bekamata na dauki da karamin ciki inkaiki inda xaki wahala ba"

Cikin kuka tace nidai wlh xan bika, duk Inda ka zauna nima zan iya zama, wlh yaya karka tafi ka barni"

OK toh shikenan daina kuka, maza Ki share hawayen ki kuma ki saki ranki"

Make kafada tayi kamar tana gaban Sa, sannan tace a'a saika min alkawarin bazaka gudu ka barni ba"

Namiki husna, ki shirya yau dinnan inanan tafe, amman karki gayawa kowa"

Dahaka sukayi sallama, jikin ma'u sanyi ya kara haka ta takure guri daya taita kuka"

Jamal ko yana gama waya da ma'u ya tashi ya dingisa, mahimman abubuwan shi ya hada guri daya sannan ya sauya kaya"

Awaya ya kira drive bayan ya shigo yace ya dauki jakar yasa amota gashi nan zuwa"

Drive ya fita babu dadewa Jamal ya fito, babu kowa afalon dan haka har ya fita babu wadda ya ganshi"

Hanya suka dauka acikin su babu me cewa kala, yamma likis suka isa Kano"

Sauka Jamal yayi ya nufi cikin gidan cike da zumudin son ganin ma'u

Salama yayi abakin falon, daga ciki mama ta amsa"

Ma'u tunda taji muryan Jamal ta mike tare da ajiyan zuciya"

Cikin ladabi ya shiga falon yana dingisawa tare da sunkuyar da kanahi kasa"

Mama naganin Jamal tace ah'ah Jamal kai da kanka ka kwaso hanya kana fama da kafar ka"

Shafo keyarsa yayi tare da satan kallon ma'u yana murmushi"

Itako ma'u tsaye tai ta kasa cewa komai, kallon Jamal kawai take tare sonjinta jikin shi"

Bayan sun gaisa mama ta shiga kitchen sannan ta kira ma'u"

Bin bayanta yayi da kallo tare da hadiye miyau"

Zuwa can ta dawo dauke da kayan marmari ta aje gaban shi"

Tana kokarin ajewa ya rike hannunta tare da kokarin dagota"

Kan cinyar shi yaso zaunar da ita ta cije tare da fadin ciyon ka fah?

Gefe ya nuna mata tare da fadin daga nan zaki zauna"

Zama tayi sannan ya hada hancin shi da tana tare da fadin kince zaki bini ko?

Kai kawai ta daga almar eh"

Cikin sauri ya wawuro bakinta, nisa yayi sannan ya fara shafa jikinta"

Ummi ce ta sawo kai bakinta dauke da sallama, cikin sauri ta juya tun batakai ga karasawa ba"

Hakan yayi daidai lokacin da suke kokarin rabuwa da juna"

Ganin mama tajuya ya tabbatar musu ta gansu dan haka takaici yasa ma'u ta fara kuka"

Jamal ma kunya ta kamashi, amman fuskan sa na dauke da murmushi yake kallon ma'u, zuwa can yace......

Ke dai kuka be miki wuya, yanzun dan Allah meye abin kuka?

Cikin kukan tace mama fa ta ganmu"

Toh menene husna?, nifa mijin Ki ne bare kice za'amiki fada, dallah ni tashi ki dauko gyalen ki, sai kice ma mama zaki rakani naganu Firdausi"

Wlh yaya bazan iya ba, ni yanzun kunyan hada ido da mama zanji"

Mikewa jamal yayi tare da fadin toh shike nan, ni bari na wuce, dan bani da lokaci'

Rikeshi tayi da sauri, tare da fadin to yaya ai kai ya kamata ka gaya mata"

Shiru yayi yana kallon ta zuwa can yace....

Ok toh yanzun abin da za'yi, kije ki Debi kayan ki kadan kisa amota"

Yana tsaye harta dawo sannan ya matsa kofar mama yace.....


Mama zantafi"

Fuskarta dauki da fara'a tace yau yau din nan ai na dauka kwana zakayi"

Cikin jin kunya yace a'a yau zantafi nazo ganin Firdausi ne"

Murmushi kawai mama tayi dan haka jamal ya sake cewa......

Zamuje da Husna ne ta raka ne"

Adawo lfy Jamal kaida matar ka"

Dan sosa keya yayi sannan yajuya ya kalli ma'u yace dauko gyale"

Basu wani zauna agidan usman ba suka fito bayan Jamal ya gama tofawa yariyar addu'oi"

Tasha Jamal yasa drive yakai su sannan suka sauka tare da kayan su"

Gargadi yawa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login