Showing 48001 words to 51000 words out of 95354 words
Chapter 17 - BUGUN ZUCIYA Hausa Novels Complete by Fadila Lamido.txt
haka Momy ni inason nai aure yanzun"
Wani kallo Momy tamai mekama da harara sannan tace"
Amman dai Jamal wautanka yawa gareta, inna fahimceka kana nufin bazaka iya rayuwan Aure da Asma'u ba"
Shiru yayi bece komai ba, dan haka Momy ta sake cewa toh shikenan Jamal tunda bazaka iya zama da itaba ai saika sallameta, dan za man beda amfani"
Shiru yayi zuwa can ya daga jajayen idon shi yace"
Momy nifa cewa nayi zan kara aure bawai wani abuba"
Eh ainaji zaka iyayin aurenka ammafa idan ka sallameta, dan baza,a tauyewa yariya rayuwa ba"
Mikewa yayi fuuuu ya fice"
Binshi da kallo Momy tayi afili tace wawa kawai, yana girma yana cin kasa"
*****
Allah sarki deeni bawan Allah,
Deeni ne zaune atsakar gida, ya rame yayi duhu, gefen shi ummi ce kwance kan tabarma, tun daga ranan dauren auren ma'u bata sake samun lfy ba, deeni ko baya iya tabuka mata komai, shima kaman mara lfy yake domin yau sati kenan, beji muryan ma'u ba"
Zaune kawai yake hawaye na zobo mai, hannu yake sawa yana sharewa, jifi jifi yanawa ummi kallon tsana"
Suna haka suka farajin haushin duna, cikin sauri deeni yayi waje"
Caka ya samu tsaye akofar gida, cikin fada yace"
Caka me yasa zaka kawo min shi, ayanzun bani da bukatan duna, katafi dashi bana son ganin kowa, idona asma'u kawai yake son gani, caka bani da kowa, kuma bani da gata, duk abin da ya sameni laifin ummi ne, itace tajamin narasa asma'u, inaji ajikina indan bansamu asma'u ba zuciyata zata Buga, wlh ina masifar son asma'u, hannun caka ya kama ya daura akan kirjishi tare da fadin taba kaji inda zuciyata take yi inaji kaman numfashina zai dauke"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[24/01, 11:04 a.m.] βͺ+234 906 689 6652β¬: ππππ
β*BUGUN ZUCIYA*β
( βHeartbeatβ)
πππ
π
πππ
βByβ
π
ββ*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATIONπ€*
β
*Slm inaba masoya BUGUN ZUCIYA hakuri sakamakon jina shiru kwana 2 da kuka yi, haka ya faru sakamakon wani uzuri nawa, ifatan zaku fahimce ni, kumin uzuri, insha Allahu zan dinga yi, ko babu yawa, wadanda sukamin mgn prvt sukaji shiru suyi hakuri plsππ» sakon yamin yawa sosai, masu son group ma suyi hakuri plsππ» insha Allahu page nagaba zan bada no dazuyi mgn asaka Ku*
5β£7β£to5β£9β£
Haka deeni yaita sambatu, batare daya san me yake cewa ba"
Sosai caka ya tausayawa deeni, bayan ta fiyan caka deeni ya shige gida, samun ummi yayi tanata nunfarfashi, kallonta yayi, kamar bazaije ba, sai kuma ya fara takawa harya je gabanta saida ya share hawayen fuskan sa sannan yace"
Ummi jikin ne?
Hannu ta fara miko mishi dan haka ya tsuna agabata tare da mika mata hannun shi"
Rike hannun tayi da kyau, hawaye na zuba a idonta cikin murya irinta wadda take jin jiki tace"
Auta dan Allah kayi hakuri naga har yanzun fushi kake dani, inacikin wani hali auta, zuciya namin kuna ina takaicin rayuwata, har inajin inama ba,a halittoni ba, duk bawani abu bane ya jawo min illah bin zuciya, gashi yanzun nazo ina dana sani, babu wadda yafi bani mamaki irin baban ka, tunda yasa kafa yabar gari har yau ban sakijin duriyar saba, juyawa tayi ta kalli deeni dayai kasake yana yana sauraronta tace auta kana jina?
Kai ya gyada mata sannan ya kauda kansa gefe"
Ummi taci gaba da cewa, auta babban burina ayanzun shine inga mahaifin ka, inason inganshi kafin ta Allah ta kasance akai na" banason na mutu nabarka babu dangin uwa babu na uba, auta nasan cewa ka girma amman nasan baka iya zama da mutane ba, sai yanzun nake wani tunani, auta da ace kai natsatsene ko na mutu nabarka makota zasu taimake ka, kuma zasu tausaya maka"
Hawaye deeni ya share sannan ya Kali ummi, tausayinta yaji ya kamashi, hawaye ya fara share mata yana fadin bayanzun zaki mutuba ummi, kuma kicire tunanin wannan tsohon a zuciyan ki, ni banason ganin shi natsane shi, kuma duk ranan dana ganshi idona dana shi, wlh wlh na rantse da sarkin dake busan numfashi sai yayi daya sanin kawoni duniya, bana sonshi sam, kuma duk randa na ganshi idona dashi saina mai SAKK"
Girgixamai kai ummi take ahankali take cewa karkayi haka auta"
Cikin sauri ya mike tsaye haba ummi ina tsananin son asma'u Amman gashi tana neman tseremin yau kusan sati 2 kenan banji muryanta ba, ummi inason asma'u kuma inason na aureta, dan haka nifah saina aureta, kuma wlh idan jamal ya kuskura ya tabamin kayana sai na masa CAN CANTA
Hmmm auta taya zaka aureta bayan tana gidan wani, zansu ka cireta azuciyar ka, ka daina kiran matar wani da kayan ka, dan musamu mu fuskanci gaba"
A,a ummi saina aureta, daga baya ma fuskanci gaban"
Toh auta karinka hadawa da insha Allahu, kuma kayi addu'a Allah ya baiyana Mahaifin ka"
Girgiza kai yayi tare da mikewa tsaye, kallon ummi ya sakeyi sannan ya kada kai yayi waje"
****
Shiko Jamal bayan yabar part din momy bangaren su ya koma, afalo ya zauna sannan yasa hannun shi duk 2 ya dafe kai, zuwa can ya cire hannun nashi sannan ya daura tagumi, neman hanyan dazai bi yake, dan gaskiya ayanzun yana bukatar mace akusa dashi, amman fa yana son wadda zai aura ta kasan ce ta girme shi, ko kuma suzo sa annan juna, daker ya iya tashi ya shirya cikin kakin Sa ya fice"
Momy ko batasan da shigowan ma'u sai kusan 12 na rana"
Dakin nafisa ta shi tana fadin nafisa zoki kiramin asma'u"
Turusss tayi ganin asma'u kwance ta kifa kanta akan gado"
A,a ke kuma yaushe kika shigo?
Nafisa ce tace momy ai tunda asuba, yaya Jamal ya rakota, kuma tun lokacin take kuka"
Tahowa Momy tayi tare da fadin kukan lfy, zama tayi abakin gadon sannan ta daga hannu ta jawota tare da halan wani abu Jamal din ya miki?
Shiru batace komai ba, dan haka Momy ta sake cewa asma'u waini me kika daukeni?, nace miki idan kina da matsala ki dinga samu na kina gayamin, ko menene kiji ko"
Murya kasa kasa tace momy inaso nakoma gida bazan iya za agarin nan b....
Sabo da me? Cewar momy tana tsare ma'u da ido"
Tsoro nakeji momy bazan iya zama abangaren yaya ba akwai aljanu aciki"
Aljanu? Inji Jamal din ne ya fada miki?
A,a momy jiya ne na kwanta bacci ban daura dan kwali ba amman dana tashi sai naga andaura min dan kwali"
Murmushi momy tayi kadan sannan ta kauda kanta gefe tare da fadin to banda abin ki, Asma,u ai bake kadai bace adaki, yanzun haka Jamal ne"
Jin ta kawai tayi tace bashi bane momy, shi ai baya ma shigowa dakina"
Shiru momy tayi zuwa can ta waiga ta kalli nafisa sannan tace"
Nafisa kira min umma me lalle"
Mikewa nafisa tayi ta zura hijjabi sannan ta kama hanya"
Cikin kan kanin lokaci nafisa ta dawo da me lalle"
Bayan sun gaisa Momy ta nuna ma'u tace kitso zaki mata da lalle"
Cikin kankanin lokaci ma'u ta fito ras, yamma likiss jamal ya dawo lokacin ma'u na zaune afalon Momy"
Sallama yayi sannan ya nemi guri ya zauna"
Idon shine ya sauka akan lallen hannun ma'u, ya ilahi ya fada azuciyan shi, cikaba yayi da cewa tunda nake ban taba ganin irin wannan lalle ba, gani yayi fuskan ma'u ta kara wani irin kyau, dan haka ya sakankance yana kallonta"
Zuwa can yaga tana kokarin dago kai cikin sauri ya maida kanshi kasa tare da saka hannu aljihu ya Ciro wayar shi"
Daga ta yayi ya kare fuskan shi, zuwa can yaga bazai iya hakuri ba, kautar da wayar yayi daidai lokacin da ma'u ta dago idonta dan haka cikin sauri ya maida wayar"
Camera ya shiga yayi saitin ma'u sosai, ya kura mata ido, har ya shagala da kallonta"
Gyara zaman shiyayi, harda kishin gid'a, yana kara mata kallo babu wadda ya lura dashi"
Momy kallon Jamal take ajikin zuciyanta tace wannan kwai miskilin jaraba, wato ko kallota bama bazaiyi ba, harda wani tare fuska da waya"
momy harara kawai take jefawa Jamal, dan babu namijin da zai kalli ma'u beso ya kara kallonta ba sai Jamal"
Shiko Jamal tuni kwakwalwar shi ta nitsa cikin kogin tunani, kallon ma'u yake yayin tunanin shi ke kimanta masa wani sura tata"
Be Ankara ba yaga ma'u ta mike tana kokarin barin wajen"
Aranshi yaji beji dadin tashinta ba dan haka yaja tsaki ya sauke wayan"
Wani haushi ne ya sake kama ummi wato, saida yaga asma,u ta tashi sannan ya aje wayan, itace beson ya kallah kenan"
Ummi ce ta juya tace Jamal ka tashi ka tafi part din ku, ga asma'u can ta wuce, kuma dan Allah karkai nisa da ita, dan naga tana da tsoro"
Mikewa kawai yayi, saida ya fara tafiya sannan yace saida safe"
Allah ya tashemu lfy momy ta fada, cikin sauri ya nufi part din dan ya kosa Yasa ma'u a idon Sa"
Adakinta ya sameta sai dube2 take, abakin gadonta ya zauna sannan ya bita da ido"
Daker ya iya furta me kike nema ne?
Kuka ta fara matsuwa tare da fadin jakatace bangani ba"
Jaka ? Kuma ? Menene ajikin jakar"
Rasa abincewa tayj dan haka taca kayan kwalliya ne aciki"
OK indai kayan kwalliya ne karki damu zan saya miki
Ko inda yake bata kalla ba, taci gaba da neme2 ta, shima bekara bin ta kanta ba, waya ya sake cirowa ya kare fuskan shi, hotuna ya fara daukan ta, duk inda tabi saitin ta yake bi"
Lokaci lokaci ma,u na waigowa ta kalle shi acin ranta take cewa shi kuma wannan me yakeyi anan bayan ba shigowa yake ba"
Gajiya tayi dan haka ta koma gefe ta zauna, ko banza sarkan deeni tana debe mata kewa, idan ta kalli sarkan har kanshin deeni takeji, hawaye taji yana zubo mata, tasa hannunta ta share, sannan ta fara neman hanyar da Jamal zai bata aron wayar shi"
Kara karfin kukanta tayi, ahankali ya juyo ya kalleta, kewai baki gajiya da kuka ne?, kulum kuka, kullum kuka, yanzun kukan kayan kwalliyan kike?
Dago kanta tayi ahankali ta kalleshi, cikin sanyin murya tace inaso ne, nayi waya da mutanen gidan mu"
Murmushi yayi kadan, sannan ya dannan wayar ya mika mata"
Gani tayi har ya danna kira, Abba ta gani akan wayar cikinta ne ya duri ruwa domin ita deeni taso kira"
Muryan Abba ce ta katse mata tunani, cikin karsashin shi yake cewa, Jamal ya Kuke, yagida"
Rasa abin cewa tayi, zuwa can Abba ya sake cewa Jamal kanajina kuwa?
Cikin kuka tace Abba bashi bane ni ce"
Jim abba yayi zuwa can yace"
Yaya aka yi?, shiru yaji dan haka yacigaba ta cewa"
Kinanan da halin naki ko kuma ya dan lafa?, ki kula kisan abin kike idan kinason kiga fara'a ta kaman da, to kiyiwa mijinki biyayya, ki kwantar da hankalin ki kikautawa mijin ki, kinji ko?
Hankali tace toh abba"
Sosai abba yaji dadin inda ta amsa, dan haka ya mikawa mama wayar"
Itama nasiha ta mata sosai, sannan sukayi sallama"
Jamal ta juya ta kallah zuciyanta cike da haushin shi, tabas Jamal be da makusa, ya hadu sosai, kuma ya iya daukan wanka, sabanin deeni da kullum yana nan dai cikin kananun riguna kusan kullum jikin shi abude yake, dan wandonan shi da wuya su wuce guiwa"
Tunawa tayi da yadda batan Jamal take sheki luf luf, sannan ta hango ta deeni data baci da sara kaca kaca"
Juyawa ta sakeyi ta kalli Jamal, sannan ta kyauda idonta gefe, acikinranta tace ni babu ruwana da wai kyan ka, duk da haka nidai deeni nake so"
****
Tundaga ranan haka Jamal yake lalacewa wajen kallon lallen ,ma,u ko gaban Momy da daddy ko haka zaiyi saitin da wayar shi,
Har aka kwashe tsayon sati 2 zuwa wannan lokacin lallain ma'u ya fita dan haka ya farajin babu dadi, besan yana son lalle ba sai wannan lokaci"
Ranan da ta cika sati uku momy ta sake kiran me lallai, Momy cewa tayi wannan karon kiyi mata na gargajiya"
Juyawa Momy tayi ta nufi dakinta, afili take fadin nikam narasa gane kan Jamal, wannan wacce rayuwa ce?, nidai nasan babu namijin da zai kalli ma'u yace beso, amman al'amarin Jamal ya fara bata tsoro, ko kallo ma'u bata isheba"
Jamal be kula ma'u tayi lallai ba sai washegari nan ya lalace gurin kallo har ya makara fita gurin aiki"
Koda yajema haka yake lalacewa gurin kallon hotonan ma'u
Har lallen ma'u ya fita Jamal be nuna yana so ba ko sha awan shi ba, dan haka momy bata sake kiran me lallai ba, aramta ta fara tunani kila ba lafiyaye bani, ganin tun tasowan shi bashi da budurwa, duk da cewa yan mata da yawa suna cewa suna sanshi amman saiya ce wai sun rainashi ne"
Tunanin hajiya asabe ne ya fado mata, kodai tayiwa Jamal wani abu ne dan ta cerai mai sha'war mace, dan ta kula kiyayyan da hjy asabe take nunawa Jamal tayi yawa"
*****
Ran da lallen ma'u yayi sati 1 da fita Jamal ya gaji da jiran ganin sabon lalli, dan haka daya shirya tafiya ya fito afalo ya samu ma'u"
Bayan ta gaidashi yasa hannun a aljihu yaciro, dubo 20 yaje agefen ta, tare da fadin gashinan kiyi lalle da kitso"
Dasauri ma'u ta kalleshi sannan tace, aini daman momy ce take cewa ayimin, bani nake zuwa ba"
Shiru yayi zuwa can yace toh Ki rike kudin saikije kicewa momy kinason amiki lalle"
Turo baki tayi kamar me shirin kuka tace nifah daman bason nake ba, dan dai momy ce kawai nake tsayawa"
Wani haushi ne ya kamashi cikin fada yace"
OK rashin kunya zakimin kenan ?
Ganin ta sunkuyar da kanta kasa yasa ya fice, yana kada kai"
Bayan kwana biyo yaga bazai iya hakuri ba, dan idan yana kallon lalle wani irin nishadi yakeji part din Momy ya nufa yana sanye da jallabiya"
Momy da daddy ya samu afalon nafisa na kwance jikin momy,"
Bayan ya gaida su ya kalli nafisa yace"
Ke bannan?
Mikewa tayi ta fice"
Motse ya fara da bakin shi, ya rasa ta ina, zai fara zancen yana son husna tayi lalle, ai wani ma sai yace sonta nake"
Wata zuciyar ce tace, to meye dan motum yace yana son kawar sa tai lalle"
Daddy ne yace jamal kaman bakin ka da mgn"
A'a daddy ba komai"
Shiru sukayi zuwa can Jamal ya mike ya nufi fita har yakai tsakiyan falon ya tsaya, tare da Fadin momy ina son na ganki.....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[24/01, 11:04 a.m.] βͺ+234 906 689 6652β¬: ππππ
β*BUGUN ZUCIYA*β
( βHeartbeatβ)
πππ
π
πππ
βByβ
π
ββ*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATIONπ€*
β
6β£0β£to6β£3β£
π€³π»π€³π»π€³π» Yana gama fadin haka ya shige dakin momy"
Mikewa tayi tabi bayan sa, yayin da daddy ya bisu da kallo"
Bayan momy ta zauna ta kalli Jamal tace ina jika yaya aka yi?
Dariricewa yayi yarasa mema zan ce, zuwa can ya dan sosa keya sannan yace"
Yariyar can ne naga kafarta kaman na maza, ko dan irin kunshin nan babu"
Cikin mamaki Momy tace wacce yariya kenan?
Husna, ya fada atakai ce"
Hmmm Jamal Kenan, ka manta kanwar ka ce?
Dukar dakai yayi kasa sannan yace ban manta ba momy, ai bawani abu bane dan nace kanwata tayi kunshi ko?
Murmushi Momy tayi sannan tace"
Eh bawani abu bane, amman ina baka shawara tun wuri ka sauke girman kan nan naka, ka daina yaudaran kan ka"
Kanshi akasa yace momy ban gane yaudaran kaina ba?
Tsaki Momy taja tare da mikewa tsaye tana fadi, ni wlh bana son munafunci mutun naso yana kaiwa kasowa"
Har momy