Showing 87001 words to 90000 words out of 95354 words

Chapter 30 - BUGUN ZUCIYA Hausa Novels Complete by Fadila Lamido.txt

29 Oct 2025

506

drive sosai cewa duk wadda ya taban baye shi yace kano ya kawo shi, daganan karya kara komai"

Saida drive ya wuce sannan suka hau motan sokwato"

Drop suka dauka dan haka karfe 10 da wasu mintoci suka shiga cikin garin sokwato, lokacin har Bacci ya kwashe ma'u tana manne ajikin Jamal"

Har suka isa kofar gidan da Jamal yama drive izinin shiga, ma'u bata tashi ba, kallonta Jamal yayi, bacci take kuma dagani tanajin dadin macci"

Kallonta yake vabu kyaukyautawa muryan drive yaje yace oga nagama sauke kayan"

Azabure jamal ya kalleshi sannan yace......

Toh kashi kuma madam tana bacci ni kuma inada matsalan kafa bazan iya daukanta ba"

Cikin sauri drive yace oga tashinta zakayi ai"

A'a bazan tasheta ba, hukuri zakayi har ta tashi ko wani abu ne saina kara maka, dan babu kyau mutum yana bacci atasheshi"

Shiru drive ban yayi acikin zuciyar yace......


Lallai wannan ba karamin so yakewa matar nan tashe ba, ni ina ruwana indai za'abani kudi, Allah yasa ma karka tashi sai gobe"


Jamal babu abinda yake banda kallon ma'u, tun da yake betaba tsayawa ya kallita hankalin shi kwance kamar yau ba"

Tayaya daddy zaice saina sakeki, bayan na farajin dadin aurena, tayaya hakan zai kasan ce, Addu'a yayi azuciyar shi Allah yasa abba ya fahimci gaskiya"

Ma'u ce ta bude idonta tare da fadin nifa nagaji har yanzun bamu kawo ba"

Munkawo husna cewa nayi bazan tasheki ba sai kin gama baccin"

Wani irin kallo tamai tare da mamakin jamal, kwallah taji ya cika mata ido, Ashe Jamal zaisota haka?, lallai ta yadda kiyayya na komawa soyya"

Waigawa tayi ta kalli gidan tare da zare ido, barikine irin na sojuji, ko ina sojujin ne ke zurga zurga, suna fitowa daga cikin motar wani ya taho ya sarawa Jamal sannan ya mika masa key"

Ma'u na manne jikin shi ya bude kofar suka shiga"

Falo ne madaidaici me dauke da daki daya tak da bayi aciki, daga can gefe kuma akwai madaidaicin kitchen"

Bayan ya zaunar da ma'u yace ina zuwa bari nayi sallah ke kuma kibari ki huta"

Kallon shi kawai tayi yana fitowa toilet din ta shege, dan haka tare suka yi sallah"

Bayan sun idar yace bari naje na samo mana abinci"

Be dadeba ya dawo bayan sunci sunsha, ma'u ta fara hamma "

Kallonta Jamal yayi tare da fadin tashi kije Ki kwanta"

Hawa gadon tayi sannan ta kalli shi yana zaune akasa ya mike kafafuwan shi tace......

Yaya gidan nan fah ya mana kadan, yazun kai a inazaka kwanta?

Ban gane a ina zan kwanta ba?

Jan bargo tayi ta rufe idobta sannan tace naga gado daya ne, kai kuma mace bata hawa gadon ka"

Take sanda ya fada mgr ya dawo mai, dan haka yayi dariya sannan yace.....

Ke bakya mantuwa ne?

Bata sake cewa kalla ba ta rufe idotan tai shiru"

Tanajin shi ya mike ya sauya kaya, sannan yahau gadon tare da yaye bargon ya shiga, zuwa can ya mika hannun sa ya rungumota jikin shi"

*Abuja*



Bayan tafiyan jamal, zuwan momy dakin uku bata ganshi ba, lekawa waje tayi nanna megadin yake shaida mata Jamal ya fita tare da drive"

Momy bata tsorata ba, saida taga drive ya dawo babu Jamal"

Tambayan shi tayi ina jamal, kamar yadda Jamal ya fada mai haka ya fada"

Acikin zuciyarta tace wai meyasa Jamal bejin mgn, wannan kafar tashi so yake ta rube, idan ba hakaba me zai kaishi kano"

Da daddare daddy suka dawo tare da deeni da alhaji bashir harda ummi"

Rike daddy yake da deeni yana mai sannu"

Bayan sun zauna momy ta kawo musu abinci"

Daker deeni yaci kadan kallon shi momy tayi taga ya rame"

Shima daddy kallon Sa yayi sannan ya mike cikin sauri ya nufi dakin da Jamal yake"

Alhaji Momy ta kirashi, sannan tace......

Jamal baya nan"

Bayanan?, ina yaje?

Kwashe yadda sukayi da drive tayi ta gayamai"

Shiru daddy yayi na wani lokaci, sannan yace"

Ni Jamal zai watsawa kasa a ido?, shi kenan nasan abin da yake nufi, wayar sa ya dauka ya kira abba"

Bayan sungaisa yace Jamal yazo"

Daga can Abba yace........

Eh haka na samu lbr ance yazo amman ni bangansa ba"

Asma'u fah ?, tananan agida, koya dauketa ne?

Eh mamanta tace sun fita tare, kasan yaran zamani, ita maman tasu dai yace mata gidan usman zasu"

Wani zancen daddy ya dauko sannan sukayi sallama"

Koda ya kashe Wayar alhaji bashir ya kallah cikin tsananin bacin rai yace......

Wlh zan nunawa Jamal nina haifeshi be isa yaja dani ba"

Meyayi ne haka da zafi?, cewar alhaji bashir"

Umarni nabashi shine bazaibiba, yaje ya dauki asma'u ya tafi da ita"

Cikin rashin fahimta alhaji bashir yace.....

Ban game umarni ba?, kuma inda yake kwance beda lfy kamata yayi atausaya masa"

Cikin ido daddy ya kalli alhaji bashir sannan yace.....

Yanzun kaman Jamal bazaiji tausayin d'an uwansa ba, ni dashi nagaya mai halin da shamsu yake ciki, yau zan gaya muku abin da nake ganin shamsu be gaya mukuba, Asma'u yariyar da deeni ke tsananin so itace asma'u matar da Jamal ke aure"

Alhaji bashir da ummi mikewa sukayi ummi harda gutun hawayenta"

Daddy yaci gaba da cewa ganin inda shamsu ke tsananin sonta yasa nace ma Jamal ya saketa bayan ta haihu shamsu ya aura, bantaba ba Jamal Umar yaki biba sai akan mace?

Komawa alhaji bashir yayi ya zauna sannan yace sai kamai uzuri, kaida kanka ka fada wannan ne na farko, kuma aikai ka nemi yama tawaye, tayaya mutum na zaune lfy da matarsa acemai ya saka wani ya aura"

Shiko deeni wani irin kallo yakewa daddy mekama dana Allah ya kiyaye"

Fada daddy yaita yi tare da yin fushi me tsanani da Jamal"

Itama momy hankalinta tashi yayi, ina Jamal zaikai ma'u tana cikin yanayi irin na laulayi, shikuma yana faman dingisa kafa, yaya za'ayi wannan zaman gashi ta kula jamal yacika fitana, baya duba yanayin jikin shi"

Kuka take sosai deeni na kallonta juyawa yayi ya kalli daddy yaga shi sai fada yake, har zuciyan shi so yake d'an shi yasaki mata shi ya aura"

Tunawa yayi da lokacin da alhaji vashir yace idan ansami mutumin daya aura asma'u zai kashe konawa ne dan ya saketa"

Wannan nanufin baba bashir besan kowaba sai ni kenan, daman haka sukemin tun ina Karami abin da nake so shi suke min"

Sun kuyar dakai yayi sannan yace....

Toh shi daddy be kyaunar jamal ne? Nasha jin daddy nawa Jamal fada kota waya ne, niko basu min fada har gara ummi takanyi wani lokaci"

Ahankali deeni yaketa babbacewa tsakanin shi da jamal akwai babbaci, dakanshi ya hango ashe ma idan ka samu wadda zai tsaya ya maka fada kai dan gata ne"

Lallai idan mutum ya rasa me masa fada ya shiga uku, tabbas Jamal bashi da makusa yana yin abubuwan shi kamar daddyn sa"

Duk cikin zuciyar shi yake wannan tunani tare da daukan alwashi insha Allahu zaiyi aure ko bana soyayya ba, dan yaga ya mallaki yara ya basu tarbiya ba irin wacce aka bashiba"

Kallon daddy yayi yace daddy dan Allah kabar fadan nan, ni tun tuni na hakura da asma'u nacireta azuciyata, ba tun yauba, daddy ya zan yi na aure asma'u, bayan d'an uwana na auren ta, daddy kayi kuskuren cewa Jamal yabar min mata, wlh na barta har abada, dan Allah abani no Jamal nakirashi ya dawo gida, zama awani waje be dace dasuba"

Kowa afalon kuka yake yi ba mazan ba ba matan ba"

Daddy ne ya share hawaye sannan yace......

Ai be tafi da waya ba, dan dana kira naji karanta adaki"

Shiru deeni yayi zuwa can yace........ .


Daddy ina son nayi aure, nabaka zabi ka zabar min mata ko ya take indai ka amince da tarbiyan ta, inaso na haifi yara na musu tar biya ba irin wacce akamin ba






Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[24/01, 11:04 a.m.] β€ͺ+234 906 689 6652‬: πŸ’—πŸ’πŸ’πŸ’—
​*BUGUN ZUCIYA*​
( ​Heartbeat​)

πŸ’“πŸ’πŸ’—
πŸ’—

πŸ’“πŸ’πŸ’—
​By​
πŸ’—
​​*Fadeela Lamido*




*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🀝*
​


*Sadaukarwa ga duk me karata BUGUN ZUCIYA, nagode da irin soyayyar da kuka nuna min tare da wannan lbr BUGUN HEAT, Allah yabar kyaunaπŸ’‹*



*Sakon gaisuwa da fatan alheri ga marubutan mu, wad'an da suka karamin karfin guiwa wajen rubuta wannan lbr, bani da bakin mgn, hakika kun nunamin kyauna, sai dai nace Allah yabar xumunciπŸ™πŸ»*



1⃣0⃣5⃣





βœ‹πŸ»βœ‹πŸ»βœπŸ» Karfe 3:15pm suka shiga gidan momy murna momy take sosai tana rike da hannun ma'u tare da tsareta da ido, nandan lbrin dawowan su ya zaga ko ina, tsilum saika Nafisa aguje ta shigo da cikinta daya fara tasowa manne ajikinta"

Jikin ma'u taso fadawa, momy ta tareta tare da fadin nafisa lfyr ki lau kuwa? Kewai bakijin nauyin jikin ki ?

Komawa tayi kusa da ma'u ta xauna, sannan ta shiga gaida Jamal wani irin amsawa ya mata batare daya kalleta ba,

'Daga ma'u nafisa tayi sannan ta suka nufi daki, kallon nafisa ma'u take tana mamaki wai yanzun cikin deeni ne jikin nafisa?, Ikon Allah kenan"

Hira suka barke dashi daga falo su momy sunajin dariyar su"

Sai dare deeni yazo daukan nafisa be shigo ba, waya ya mata tafito sutafi sannan tace yana gaida momy"

Daddare momy so tayi ma'u ta kwana gurinta amman taga Jamal sai zarya yake yafita yadawo dan haka tace tashi su tafi"

Dukda kwaciya kawai zasuyi tare yafison haka akan ace sunyi nesa da juna,

Washegari da safe sukaje gaida daddy abinda ya bawa Jamal mamaki daddy be nunafushi ba, sosai farin ciki ya bayyana afuskar shi, koda zasu tashi yaga ma'u na kici kicin tashi, cikin fada daddy yace haba Jamal taimaka mata mana, kunya ce ta kamashi daker ya iya mika hannu ya dagata Albarka daddy yaita samusu tare da addu'ar Allah ya sauketa lfy"

Adaren ranan ciwon nakuda ya tayarwa ma'u tunda momy taga inda take cije baki ta kira jamal, daki ta shiga ta dauko kayan haihuwa tace asibiti zamu"

Karfe 10:39pm ma'u ta haifo zarkada zarkadan 'ya'yanta guda biyu dukkan su maza ne masu kama da Jamal"

Bakaramin maki Jamal yayi ba, tunda suke zuwa asbiti babu wadda yataba cewa yan biyune acikin husnan shi"

Momy ko farin ciki ya hata mgn, adaren suka dawo gida domin ma'u lafiya lau take"

Tun asuba momy ta fara gayawa yan uwa da abokan arziki dan haka tunda safe gidan ya fara cika da baki"

Nafisa ma murna ba'a magana tare da deeni sukazo fuskanshi dauke da murmushi nafisace ta kwaso yaran ta mika mishi kallon yaran yayi gwanin ban sha'awa nan danan idonshi yacika da kwallah yasa hannu ya share tare da fadin nafisa yaran nan sun bani sha'wa inason yara sosai sunbatan yaran yayi tare da fadin Allah yayi muku albarka ya karawa mahaifiyar ku lafy shekara me zuwa ta sake haifo mana kalan ku, yakuma bawa mahaifin ku abinda zai ciyar daku"

Amsawa nafisa tayi da ameen, sannan tace ka manta addu'a daya da bakiyi ba"

Dagowa yayi
ya kalleta, idontshi da ragowan hawaye ga kuma murmushi akan bakin shi yace....

Wacce kenan?

Cikin murmushi tace......

Bakace muma Allah ya bamu irinsu ba"

Murmushi yayi tare da cewa a'a nafisa muruke me albarka kawai, ko mace kona miji ke duk abinda Allah yabani zan karba nayi godiya lokuta da dama abinda mukeso ba alheri bane agare mu"

Dahaka ya mikawa nafisa yaran sanan yace ta gaida asma'u"

Aranan momyn usman ta iso tare da dada"

Tunkafin ta shiga gidan take fadin you alkawari ya cika gani agidan takwara"

Koda suka shiga dakin ma'u daure fuska tayi, tare da kyauda kai, itama dada daure fuska tayi tare da fadin nima ba gurinki nazo ba"

Aranar da daddare hajiya asabe tazo ganin jarirai, farin ciki sosai ta nuna"

Acikin zuciyan Momy tace inma bakin ciki kike ke kika sani, ni baki gabana mantawa ma nake inada kishiya idan yana gidan ki gani nake kamar tafiya yayi"

Awaya deeni ya kira Jamal yamai barka, ana gobe suna ya dauki nafisa suka shiga kasuwa kayan yara yaita kwasa kala kala tare da kayan wasa kai harda keke komai iri daya ne kuma bibbiyu, mota sukaita lodawa, Wata sarka nafisa tagani tace ka saiwa asma'u"

Wani kallo ya watsamata tare da fadin awani dalilin zan saimata ?, kinason mijinta yakaini kutu ko?

Turo baki tayi sannan tace wato ka maida yaya mafadaci ko?

A'a nafisa aiko nine sai inda karfina ya kare"

Washegari akwai suna, anci ansha jama'a ba masaka tsinke da sunan su aka barsu *Hassan da Hussain* aciki waddan da sukazo suna harda zainab kawar ma'u"

Lokacin da yan waliman Jamal suka cika gidan da hayani ma'u ta jawo zainab bakin window da hannu ta mata nuni da deeni"

Tabassa deeni yayi kyau babu wadda zaice yayi rin
rayuwar da yayi abaya, Saika ma zaci yafi su Jamal roko da addini domin su dikine na zamani sanye ajikin su, yayin da deeni yake cikin jallabiya fara karrr hannun sa rike da carbi, gefenshi Faisal ne zaune"

Washegshegari duk yan suna suka watse, sai dada kadai ta rage"

Kulum abba ke kiran dada awaya tare da tambayan jikokin shi, wata rana abba ya kira dada suna cikin mgn ma'u ta kwace wayar tasa akunne tare da fadin abba kulum ni baka tambayata"

Dariya yayi sannan yace......
Asma'u ai muna waya da mijin Ki, nasan lfy lau kike, ya mutanen gidan naku?

Lfy lau"

Toh madallah, Allah ya miki albarka, yadda kika min biyya kema Allah yaba ki masu miki, akullum ina miki addu,a zama lfy tare kwanciyar hankali"

Ameen abba, idon ma'u cika yayi da kwallah, sallama sukayi da abba, hawaye kawai ma'u taji suna Zubo mata daman haka iyaye sukeji idan dan su yai masu biyyaya, lallai naso nayi kuskuren nabi son zuciyata, kome nayiwa iyya na bazan biyasu ba, addu'a ta shiga ma iyayenta Allah ya saka musu da alheri"


Haka dada taciga da kula da yaran ma'u Hassan da Hussain har sukayi arba'in aranan Jamal yakaisu Kano, bayan sati 2 ya koma ya dauko su"

Bayan wata 5

Nafisa ta haifi katon danta, murna gurin deeni ba'a mgn, ya dade rungume da yaron, yana kwalla tare da tufa mishi addu'oi"

Ma'u ma bakinta ya kasa rufuwa, shiryawa sukayi ita da momy zasu tafi, momy na rike da hassan, hussaini a hannun ma'u har sun fito harabar gidan, motan Jamal ya shigo"

Tunkafin ya fito ya daure fuska"

Ma'u ko fara'a take tare da zumudin fadamai nafisa ta haihu"

Cikin basarwa yace naji ai, ina zaki?

Sanyi jikin ma'u yayi, tare da rasa abincewa"

Momy ce ta kalleshi tace.....

Zamuje gano jariri ne"


Da sauri yace amman bada Husna ba"

Daure fuska Momy tayi tare da fadin da Husna kuwa, Jamal wai me kake nufi ne?, kiri kiri ka hana Asma'u zuwa gidan Nafisa, bata taba zuwaba, watanta 6 da haihuwa amman ka hanasu suyi zumunci, wanne irin bakin kishine wannan?

Shiru Jamal yayi tare dasa idon shi akasa"

Cigaba momy tayi da cewa toh abin ya fara damun nafisa, dan harta fara korafi akai, abinda kake nufi baxai yuwuba gara ka canza tunani, jayawa tayi ta kalli asma'u tace wace mutafi"


Acike suka samu falon, ummi na zaune rungume da d'an deeni ahannunta, bayan gaishe gaishe ma'u ta amsa yaron, dakin nafisa ta nufa, tana kokarin shiga dakin sukai karo da deeni yana fitowa"

Cikin sauri ya matsa gefe tare da fadin Ya subuhananlah"

Dago ido ma'u tayi ta kalkeshi, shima idosa nakanta"

Tafiya ta fara tare da gaidashi bayan ya amsa tamai barka sannan ta shiga dakin jikinta asanyaye"

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login