Showing 21001 words to 24000 words out of 134057 words

Chapter 8 - FARRAH BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MY SHAKUR .txt

24 Jan 2025

7510

heck are you guys? What do you want from me? Where am I? Kunsan ni waye”? Har mutumin zaiyi magana wanda ke waya yace “give me chair Lamido” dasauri dayan yajuya yana saramai yace “to Oga” sanan yadauko kujeran karba yayi ya ijiye daidai gaban Zayn yay wani irin zama agaban Zayn yana kallonshi kaman yanda Zayn ke kallonshi da jajayen idanunshi, cikin dakewa yace “kaine Ogan su”? Gyadamai kai Ogan yayi, cikin fushi Zayn yace “then who the f*ck are you”? Fas! Wani mummunan mari yama Zayn da saida Zayn yay ihu. “Shit!” Yakai hannunshi yana shafa wajen tunda aka haifeshi ba’a taba marinshi ba sai yau, cikin wani irin zuciya still yana shafa kuncin nashi da kullallen hannuwanshi yace “how dare you slap? I will make you pay for this, sainasa arayuwan nan baraka karajin kwadayin Marin wani ba” HAHAHA! Ogan yay dariya kaman wani Boss yana kallon Zayn din sanan yakalli yaran nashi yamike tsaye yace “kumai ladabi bakin nan nashi ya mutu kafin nazo nai magana dashi” sanan yawuce chan yana ciro wayanshi yana dialing number dan cigaba da wayanshi.




Wani irin faduwa gaban Zayn yake ganin gardawan maza su uku sunyo kanshi yanaso yatashi yagudu amman babu dama, duwaiwai yashiga ja yana komawa baya suna binshi yace “don’t touch me, don’t f**king touch me, I am telling y……” bai karasa maganan ba daya daga cikinsu yamai kafa abaki sai jini kafin ya ankara saukan dukan maza kawai yakeji ta ko’ina babu ko digon tausayi sumai ta kafa sumai da hannu, tun yana iya ihu har bakinshi yau liss ya mutu yana kwance awajen kaman wanda yamutu bakinshi ya kumbura sosai yana fitarda jini hakama fuskanshi duk ya kumbura sabida da kafansu dake Dante da jungle booth sukamai duka.


“Oga angama” Lamido yafadi suna komawa baya, Oga ya katse wayan dayake yi sanan yataho ahankali yazauna akan kujeran yana kallon Zayn din dake kwance akasa yace “Lamido adagomin shi ya zauna” dasauri sukai kanshi dagashi sukai suka zaunar dashi saida yay kara sabida azaba sanan suka koma bayan Oga suka tsaya.
Kallon fuskan Zayn din Ogan yayi yace “welldone boys” sanan yakalli Zayn yace “you look Cute Dadys boy” HAHAHA yakara dariya sanan yace “dagamu sai kai adajin nan babu mai kwatan ka, kariga kabaro Abuja kabaro yankin garinku ma kwata kwata inda zan fada maka inda kake dasaikasha mamaki so kada ma kayi tunanin zaka kubuta daga hannunmu” yay dan shiru sanan yace “mutane uku suka bamu Wanan kwangilan na kidnapping naka, biyu daga cikinsu naso mu halakaka har lahira kamutu kawai babu labarinka, mutum daya kuma nasonka da ranka amman sai an gama karbe komi na mahaifinka sanan za’a maidaka, so the whole case akanka is interesting, kidnapping aikina ne tun inada saurayi amman bantaba kamo babban nama iri ka ba, kasan irin kudin dana samu nakuma ke samu akanka kuwa? Yanzu muka fara wasan” Hahaha yasake dariya sanan ahankali yace “kubashi abinci” hanyar jakansu Lamido yayi sanan yadauko wani bushashen buredi na irin na naira hamsin da pure water guda daya yataho gaban Zayn sanan ya Yar akasa kaman yabama kare, ture abincin Zayn yayi azuciye yace “I am not eating” dariya dukansu sukahau yi harda tafi, tsinkewa zuciyanshi yayi da kyar ya iya bude baki yace “konawa mutanen dasuka saku ku kamoni zasu baku zan baku x10 inhar kun sakeni” duk kallonshi suka tsaya yi kaman wayanda suka gamsu da maganan shi sanan sukahau dariya, kafin Ogan yace “ku karyamin hannunshi daya” wani kalan zaro idanu Zayn yayi tsabagen shock yama kasa magana, ganin sun taho kanshi gadan gadan yasa yafara ihu. “Somebody help me, help me, mutanen nan sun saceni, mutanen nan sun saceni” hannunshi suka fuzga suka warware kullin sanan suka kama left hand din Zayn yanajin yana gani wanda ke kama da doki ya ballamai hannu bass tsabagen azaba sumewa ma yayi, Ogan yace “finally gwara yayi bacci yadameni”.
Wanan kenan……








Tana zaune acikin dakin nan nata ita kadai dayake da duhu ko fitila babu tana zaune ta idar da sallan isha’i taji muryan Rakiya ta kwalamata kira cikeda bala’i. “Farrah” tashi tsaye tayi da sauri jikinta harya fara rawa hannunta dasauri takai ta taba goran pepper spray da Shafa tamata dake makale gefen zaninta tana numfashi da sauri da sauri. “Wai bakiji ina kiranki ba Shegiya Yar Jaka nazo dakin nan naki na tumakai kashekine kawai bazan yiba” Rakiya tafadi ranta abace, ahankali tasa hannu tabude kofan taramo tafito daidai lokacin itama Inna dake sallan isha’i lokacin da Rakiya tashigo gidan tafito tana kwace hijabin tana daurawa kan igiyan tsakar gidan tace “meya faru Rakiya”? Cikin fushi Rakiya takalli Farrah daya fito tana rabewa abango daga nesa dasu, Rakiya tace “yau kin hadu da Modibbo kobaki hadu dashi ba”? Da bala’in sauri Farrah ta girgiza mata kai tana hadawa da yatsu alamun a’a basu haduba, cikin fushi Rakiya tadubi Inna tace “Inna kinga dai yarinyar nan da Baba yasaka mana agida bata gabana bana shiga harkanta, wlh Inna takiyayan mini Moddibo na, ko ganinshi tayi tama chanza hanya dan banso ko hanya yahadasu, Inna yau ina kawomiki karanta na karshe wlh wlh na rantse da zatin Allah ko magana aka kara zuwa akacemin anga ta tsaya tanayi dashi koko kima hada hanya dashi komenama yarinyan nan ita taja, komenamata ita taja, Modibbo nawa ne nikadai ne matarshi a kap karkaran nan, idan kunne yaji……” Inna tace “gangan jiki ya tsira” Rakiya tajuya tawuce dakinsu itakuma Inna takalli Farrah da kanta ke kasa tanaji kaman ta kasheta tace “in ciyar dake sanan in ciyar da Baffan ki da kudina sanan kice zaki kwacema y’ata Modibbo Farrah wlh wlh zan iya halakaki har lahira ki kiyayeni” tana maganan tajuya fuuuu tai ciki ganin Malam yaleko daga dakin ahankali itakuma tajuya takoma dakinta tasamu gefe daya ta kwanta sai bacci Allah yasota takoshi.


Da asuban fari ta bude ido tana fitowa ta zaga bayangida sanan tadauro alwala, tadawo dakin ita harta saba rayuwa acikin duhu salla tayi na asuba sanan tazauna tana addu’a, mahaifiyarta kafin tarasu takoya musu karatu sosai dan haka ta iya ta iya salla daidai gwargwado sanan bata wasa da addu’a.
Gari nafara haske tafito ita kadai da sanyin safiyan nan nan tadauki tsintsiya ta share gidan tass, sanan tai wanke wanke, saida tagama sanan tabama tumakan gidansu da shanaye abinci daidai lokacin Inna tafito daga daki fitowa tayi daga wajen tumakan ta tsugunna har katsa alamun gaisuwa ko amsata Inna batayiba tawuce bandaki itakuma tadauki tulu dan fita debo ruwa rafi tanada kuzari da zafin nama nan da nan tashiga cike ko’ina, tana cikin tafiya zata koma rafin zuwan karshe kenan zatayi ko’ina yacika agaban rafin taga Modibbo tsaye rikeda wani paranti mai kyau da buredi kekai da kofi babba dayacika da shayi sai cinyan kaza agefe soyayye dakuma soyayyan kwai, kallo daya tamai tawani irin juya, dasauri yabiyota yace “Farrah Farrah tsaya” tana shirin kwasa dagudu yasha gabanta yana kallonta yana murmushi yabi kayan jikinta da kallo sunyi daka daka dan tabe baki yayi yakalli fuskanta dahar wani sheki yake dudda ko wanka ma batayi ba ga uban gashi a goshinta da giranta baki sudik har wani kyalli suke yace “bakiji ina kiranki bane zaki gudu, Kari nakawo miki nasan ba’a baki abinci awanan gidan bani tulun nan kigani” yakai hannunshi zai sauke tulun daga kanta dasauri takoma baya tace “iiiiii” cikin yanayi na kurmanci alamun yabar shi, jiyayi ranshi yabaci daurewa yayi yamika mata tray din yace “to gashi kici” dauke kai tayi takalli gefe dasauri dan bamataso taga abincin ranta yabiya, sosai yaji ranshi yabaci cikin fushi yace “wlh idan baki amsaba zansa akulleki amiki bulala dariya wawiya kawai sabida kinga ina sonk……” “Farrah” wani irin bari jikinta yayi jin muryan Rakiya daga ita har shi Modibbo juyawa sukayi suka kalli Rakiya, kana ganinta zakaga tsantsan bacin rai da kishi a idanunta dan takai minti daya tsaye a wurin amman ta daure dasauri takaraso wajen Farrah tai baya dasauri danta dauka dukanta zatayi Rakiya tasa hannu ta amshi tray dake hannun Modibbo tace “Allah sarki Hamma haka kake sona kabama Farrah takawomin gida, gidan su Atine fa zani nace bari nabiyo tanan, nagode Hamma Modibbo” tai maganan tana amsa tana juyawa dantama Farrah mugun kallo amman harta bace daga gudun, juyawa Modibbo yayi fuuu yawuce batare dayace ma Rakiya uppan ba, saida yabace mata sanan tai kwafa tawuce gida.




Awani irin zuciye Rakiya tashiga gidansu tana ihu. “Farrah, Farrah” Inna datagani na rege shinkafa atsakar gida tace “Inna ina Farrah”? Baki Inna ta tabe tace “kinfasan tunda tagama gyara gida ta debo ruwa sai kwasan awakai da shanaye ta wuce daji kiwo ko Rakiya baki sani bane? Me Wanan ahannunki” ko kallon Inna batayiba tajuya tawuce tashige dakinsu.








💫 FARRAH 💫




✍🏻M SHAKUR






Littafin nan is 500 pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank Saiki turomin evidence of payment ta WhatsApp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting.






EPISODE 9️⃣
Tunda aka haifeshi yataso yafara wayau baitaba shiga wani yanayi na azaba dazaisa harya furta sunan mahaifinshi ba sai yau, yanada gatan dakome yakeso basaiya fadi ba za’amai, kafin yay tari anmai providing, baitaba shiga wani yanayi dazai kira mahaifinshi ba dan mahaifinshi has always being there for him kafinma ya nemeshi, yau shine dayaji azaban karya kashin hannu da idanunkashi biyu kuma yana cikin hayyacinshi bawai anmai anesthesia bane kowani abu ba baisan lokacin da bakinshi yafurta. “Paaa….paaa!” Da bala’in karfi hawaye na tsantsan azaba na zubomai, dariya gardawan sukahau yi babu ko alamun imani a tattare dasu sukace “sannu yaron Papa, ko Papaya kakira yau ba Papa ba bazaijika ba” sukai maganan suna haska fuskanshi da tocula dan duhu yasomayi amman tuni yasume sai hawaye dasuke kan fuskanshi nan fresh ganin haka yasa suka koma wajen Boss dinsu dake waya, juyowa yayi ya katse wayan dayake Lamido yace “Oga wai yaya ake ciki ne”? Dan ajiyan zuciya yasauke yace “sunce nabasu awa ashirin da hudu, yisu yisu su ukun sun kasa tantance abinda sukeso na akashe yaron ne koko abarshi da ranshi ne, kuma uban yaron da shine kadai zai iya bada order kudi idan muka kira ya gigice yana asibiti anyi kidnapping rayuwarshi wanan katon banzan dakuke gani, nidai nabasu 24hrs din, inhar basuyi making decision ba suka bani order kiran uban yaron ba dan Billyan dari nakeso yabamu toni kashe yaron zanyi asalin aikina najirana chan, bazan wuce gobe agarin nan ba saina kammala aikin nan, kuma bayan na kashe shi ko sunaso ko basaso saisun biyani kudin aikina da resources dina da akai amfani dashi inba hakaba suma sun sanni shi kidnapper baida amana dan tonamusu asiri zanyi ku yageta kawai” Lamido yace “bakada case Oga kome kace ayi hakan zamuyi bamaja dakai” yay maganan da muryan nan nashi irin na yan wiwi dinnan, murmushi Ogan yayi yanajin dadin aikin Lamido, dan sosa kai dayaga Lamido nayi yasa yace “ya akayi dawata maganan ne” dan yake Lamidon yayi yace “ahhh Oga dama nazo nadan zaga dajin nanne naga kaman akwai rugan fulani kusa sonake naje nasamo mana taba sanan idan akwai bani (yammata) nadan girgije nasa chaji kagane ai Oga eh yane” dariya Ogan yayi yana zare safan fuskanshi yace “dakai da Lamba kuje, Sagir yazauna gadin wanchan yaron kada kubata lokaci” angama Oga yay maganan yana cire tashi safar fuskan shima Lamba da Sagir duk suka cire sanan suka wuce shikuma Sagir yatafi gadin Zayn dake baccin wahala anan kasa kan ciyaye.




Wuraren 6 nasafiya wani kalan sanyi dakuma zugi na innanaha da hannunshi keyi yafarkan dashi daga wahalallen baccin dayakeyi bude idanunshi tass yayi yanabin dajin dasuke da kallo gasu Lamido duk suna kwance akan bargon dasuka shimfida akasa suna shakan bacci abinsu shikuma kwance a kan ciyayi, wani kalan fuzar da iska yayi abakinshi yana kokarin yunkurawa yatashi zaune amman yakasa sabida hannunshi dayake akarye kaman ya kurma ihu yakeji hannun ya kumbura, ahankali yabi buredi da pure water da aka bashi jiya daya zubar yakeyi akasa da kallo, yunwa yakeji bana wasa ba rabonshi da abinci tun na safen jiya da Mami tabashi baida wani cin abinci dama sabida su taba da sauransun dayake sha suna cikamai ciki amman inhar bai shaba sanan baici abinci ba yunwan dayake zuwa yaji yana zama extreme, dudda kalan yunwan dayakeji baikai kalan kishin ruwan dayakeji ba, lips dinshi sun bushe, bakinshi ya kape sabida tsan tsan kishi dayakeji ga azaban ciwo, tunda yake shi baima taba ganin pure water ba sai jiyan dasuka bashi, ganin abin yayi kaman fitsari amman yanda yakejin kishin nan yanzu he’s willing yasha maybe yamasha zaiji sassauci a zugin da hannunshi kemai, yunkurawa yayi da hannunshi dakeda lafiya amman ina abin yagagara sabida hannun a daure suke tare koyaya yay motsi damai lafiyan saiyaji amara lafiyan, wani kalan kara na azaba yasaki yahakura da tashin yana kallon sama yana tunani cikin tsananin tsoro da azaba da fargaba dakomi ma yace “am I going to die”? Yay maganan ahankali muryanshi a tsinke shi baitaba sanin akwai kalan wahala da azaba haka aduniyan nan ba saiyau, hawaye ne suka zubo daga gefen idanunshi na tsananin wahala ahankali yace “Dad, Mami I am scared” yay dan shiru sanan kaman karamin yaro yace “I am afraid of this place, I am afraid of this people, Papaaa” har cikin ranshi yakejin tsoron komi na wurin, shi baitaba fada ba, he just lived a wired life, baidama friends at all, rayuwanshi kawai yayi shaye shaye, yaci abinda yakeso, yasha abinda yakeso and have sex, ko matayen dayake sex dasu bawai yana magana dasu bane no, kawai yayi abinda yakeso yabasu kudi su wuce, ko kina sonshi kin sama kanki wahala ne dan baimasan yaya ake soyayya ba, baisan anything kan life ba, his entire life revolve around, shaye shaye, cin mata, kallon ball, ga zuwa club, babu any aboki namiji ko Aboki ya mace in his life, he is Zayn, and he is alone kaman yanda Baban shi ya haifeshi alone haka ma life bashing yake alone. Baisan inane wajen nan ba, baitaba zuwa wani gari a Nigeria ba banda Abuja wanda nan iyayenshi suke sai lagos, lagos ma airport kadai baitaba fita daga airport ba, baisan inane nan ba, baisan wani daji ne nan ba, baisan tayaya aka kawoshi nan ba, tayaya su Papa zasu rescuing nashi, ahankali yace “am I gonna die today”? Yakara tambayan sararin samaniya dayake kallo wanda rana ke shirin fitowa, hawaye ne suka zubomai ahankali cikin wata kalan raunanniyan murya irin muryan wanda yay loosing hope completely dinan yay giving up yace “Ya Allah save me please” (niko M shakur nace yau kasan da Allah Zayn).
Tafiyan abu dayaji akan hannunshi yasa dasauri yajanye idanunshi daga sararin samaniya yakalli hannu, wani bakin babban gizogizo yagani irin na dajin nan wani kalan zabura yayi yatashi yakwala ihu. “Ahhhhhhhhhh Spider, Spiderrrrrrrrrrr somebody help meeee” yanda yake ihu with all his power saika tausayamai kaman zai zare, farkawa kidnappers din sukayi jin kalan ihun da Zayn keyi duk atsorace suka zazzauna, ganin yanda yake ihu yana juye juye yakasa kabar da gizogizon shima gizogizon ya rude dan ihun Zayn ya rudashi yana neman hanyan guduwa, wani kalan tsaki Oga yaja. “Mtssswwwww what kind of a spoilt boy is this” sanan yakalli Lamido yace “please tashi kaciremai abinchan daga jiki koyabar kunnuwanmu suhuta dan dodon kunnena na gab da mutuwa” azuciye Lamido yatashi zuciyarshi tai bakin kirin sabida yanda Zayn yatadasu daga bacci yana zuwa gabanshi hannu daya yasa yacire gizo gizo yaa jefar sanan akufule ya dumama Zayn wani annamimin naushi akan idonshi yace “dan shegiyan yaro kawai malalaci gizogizo yakema ihu haka saikace mace” tashi Oga yayi dasauri ganin nushin dayama idanun Zayn dayasa Zayn yakife fuskanshi kan kafafunshi dasauri yace “haba Lamido kakosan iyayen yaron nan zasu tambayi proof of life zaka tsiyayemai idanune” cikin fushi Lamido yajuyo yadawo Ya kwanta yace “shiyaja ai uban wayace yatadamu kashe shi girgizon zaiyi, saisa na tsani yaran masu kudin nan wlh, bana ragamusu idan mukai kidnapping nasu, Allah ya soshi namiji ne da wlh ya cinyemai gutsu” kallon Lamidon yayi dahar yamaida idanunshi Ya Lumshe sanan yakalli Zayn da fuskanshi ke kife kan kafafunshi yay shiru kaman anyi ruwan sama an dauke sanan yakoma shima ya kwanta ranshi abace da abinda Lamidon yayi.
Zayn ji yayi idanunshi na dama da Lamido ya nusa yama daina aiki, jiyayi kaman irin an fasa kwai abu kawai tsiyayowa yake daga cikin idanun hakan yasa yay shiru yama kasa kuka yakasa ihu yakasa komai sai dan karen azaban dayakeji gashi bazai iyakai hannunshi yataba idanunba saisa kawai yadaura fuskanshi akan kafafunshi yay shiru yariga ya sadakar mutuwa zaiyi.
****








Saida ta chanza kaya agurguje kafin ta kwaso tumakon su fito tana addu’a Allah yasa kada Rakiya ta rutsata agidan, kayan fulanin ta tasaka dan rigan fulanin da suka koma kaman brown tsabagen sakawa koda yaushe yay mata chachas ajiki sai zanin dabai gama kaimata har kasa ba ta daurashi tsaf sai fararen kafafun dake sanye da silipas dinta da duk yagama sudewa shima Shafa tabata, kanta ta daureshi tsaf da adiko (dan kwali) na wani kodaddiyar atampa, goshinta sanye da wani oldi (sarka) ja na beads dayan fulani kesawa a goshi, kunnenta na sanye da dankunni na beads suma ja, sanan tadaura babban hulan hat 👒 na zuwa kiwo dinan akanta tadaure igiyan a gemunta sabida rana, hannunta rikeda sandar kiwo, tai wani irin bala’in kyau dudda babu wani something meaningful kokuma mai kyau ajikinta amman ka kalleta baraka iya cire idanunka akanta ba saika gama karemata kallo tsaf sabida she looks simply beautiful abinda yake karasa Modibbo ke bala’in sonta kenan.




Ahankali take tafiya sabida yunwan datakeji tun safe ko ruwa ba’a bata tasha ba, amman bata wani damuba dan yawanci dama idan tafita kiwo saitayi nisada karkaran su zata tsaya ta tatsi nonon shanu tasha abinta tai nak sanan tasakesu tashige cikin wani kogo Awani dutse daya zaman mata kaman gidanta tai bacci ta abinta.




Sosai tai nisa dan sunbar karkaransu gabaki dayama suna dajin Allah awakan sai cin ganyayyaki suke suna jin dadinsu,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login