Showing 72001 words to 75000 words out of 134057 words
Chapter 25 - FARRAH BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MY SHAKUR .txt
tai ihu tace “Ya Zayn kasakeni kaga za’azo aganmu” kallon fuskanta yayi ganin yanda take kallon kofan ajinsu dukta rude, tabe baki yayi yace “and so?” Dasauri takalleshi tai kini kini da fuska kaman zata fashe da kuka, gira daya yadaga mata yace “ba rashin kunya kikemin ba kin rainani” wani kalan hararanshi tayi da manyan idanunta kaman zatai ihu tace “to ka saukeni mutafi zan bika” girgiza mata kai yayi yace “wlh ahaka zan daukeki har waje” yana maganan yajuya hannunshi daya yasa ya sunkuci jakanta kan table ya rataya akafadanshi yacigaba da tafiya yace “yarinya kaman paper better be eating inba hakaba haka all your mate zasuyi girma su barki” turo baki tayi tace “baruwan ka dani, ka saukeni nayi tafiya da kafata nidai” batare daya kalleta ba yace “anki din” yafice da ita daga ajin, kokawa tashigayi dashi cikeda masifa kaman zatai hauka tace “Ya Zayn ka saukeni wai sai anganmu banson haka, nace kadaina tabani, ka saukeni” yana tafiya da ita effortlessly yace “idan kin isa ki sauke kanki kome zakiyi bazan saukeki ba dan I gave you the chance baki daukaba” ganin sun fara sauka daga stairs kuma tasan akwai student akasa yasa ahankali tace “Ya Zayn to kayakuri bazan kara maka gardama ba” tsayawa yayi chak kan stairs din yakalli fuskanta itama kallonshi take tai tsuri kaman bazata cijeka ba kasamata hannu abaki, ahankali yace “I thought ai barakice nayakuri ba stubborn girl kawai” dauke kai tayi dasauri dan batasan mesa ba idanunshi namata wani iri, ahankali yaduka yasauketa dirkowa tayi da sauri tajuya zata wuce yace “come back here waye dan aikin ki dazai daukan miki jakan ki” wani kalan bakin ciki ne yacikata ciki kaman tadakeshi takeji, juyowa tayi tajuyar da kanta gefe tareda mikamai hannu akumbure tace “bani jakana” binta yayi da kallo saikuma yadanyi murmushi yarasa maisa yanda take kumbure kumburen nan tana nuna tanajin haushin shi abin is so cute to him, kodan baitaba samin abokin fada arayuwanshi bane oho, ganin taki kallonshi ta juyarda fuskanta gefe tana wani mikamai hannu yabata jakanta yasa yace “nine kika tsana” bata ankaraba kawai yaduka yadauketa chak kaman yar yarinya ihu tahauyi tana shila kafa tace “Ya Zayn nika saukeni wlh ka saukeni kada kafita dani nagayamaka” murya chan kasa yace “better save your breath” kawai yafice da ita suka shigo school premises din ga students wasu na basket ball wasu na wasa, wasu na ciye ciye duk aka juyo ana kallonsu dawani kalan sauri tajuyar da fuskanta ta manna a kirjinshi tai lamo tana nishi ahankali kaman zata nutse akasa dan kunya gashi ya tsaya chak kaman soyake aganta aganeta intentionally yaki tafiya.
Security makarantan ne sukazo da sauri daya yace “sir what happen? Is she sick again” dan yagane Farrah, dan murmushi Zayn yayi yasaci kallon fuskanta data manna akirjinshi yace “lafiyanta ka……..” jin zai tona mata asiri yasa ahankali tafashe da kuka dasauri daga Zayn har security suka kalleta har lokacin fuskanta na manne akirjinshi, dasauri security yace “Ayyah sorry, Sir I think ku kaita asibiti abata proper check up dan exam suke” gyadamai kai Zayn yayi yawuce abinshi yana murmushi kukan makircin datayi nabashi dariya.
Fitowa sukayi yay wajen mota da ita, saida yabude kofan motan sanan yakalleta yace “sauka daga jikina drama queen kafin na jefar dake” dirkowa tayi daga jikin nashi da sauri tashiga motan tana turobaki, girgizakai kawai yayi yamaida mata kofan yarufe ganin taki rufe kofan yabude baya ya jefa jakanta sanan yadawo yashiga gaba ya zauna tareda kallon agogon Rolex din hannunshi dan tsaki yayi yace “you just waste my today gabaki daya, stupid girl” yajuya tareda hararanta, batare data kalleshi ba ta ballamai hararra tana magana ciki ciki tace “ni ba stupid girl bane kaine stupid boy” dasauri yace “what? Speak louder” juyamai kai tayi tana kallon hanya hakan yasa ya kunna motan yaja motan ahankali yana tafiya, bini bini yana tuki yana kallonta, baisan mesa ba but he’s just happy sosai.
Suna kaiwa gida kafinma yakarasa parking tabude kofa tafice tai side dinsu da sauri, saida yagama parking sanan yakashe motan yafito, jakanta ya kalla sanan yadaga kai yakalleta yanda take sauri zata side dinsu sanan yanuna kanshi da hannu yace “is that gurl turning me into her servant or what nita barma jakanta” ya jinjina kai abinma mamaki yake bashi, wucewa yayi yafara tafiya saikuma yay kwafa yadawo yabude bayan motan yasa hannu yadauki jakan yarataya akafadanshi sanan yamaida kofan yafara tafiya yataho zuwa side dinsu, ahankali yabude kofa da sallama abakinshi chan kasa, Dad da Mami ne zaune a falo Mami na gyaramai kumba duk suka dagokai suka kalleshi, daure fuska yayi tamau yace “Afternoon Paps & Mami” yajefa jakan kan kujera yajuya zai fita Mami tace “Zayn” ahankali yajuyo yana tsaye wajen kofan, ahankali Mami tace “have you had lunch” girgiza mata kai yayi yace “no Mami” murya chan kasa tace “zokaci kafin ka koma” gyadamata kai yayi yataho ciki satan kallonshi Dad yayi gani yayi yaron nashi ya rame ma sosai.
Zama yayi ahankali a dinning Mami tace “when was the last time kaci tuwon shinkafa”? Dan kallon fuskan Mami yayi yace “I can’t remember” zubamai Mami tayi da lafiyayen miyan busashen kubewa yaji kifi tasamai spoon dan tasan bazaici da hannu ba, sanan tawuce takoma wajen Dad tacigaba da yankemai kumban, saukowa Farrah tayi bayan ta chanza kayan makaranta tasa wani Riga da skirt na kanta black and white dasuka mata kyau ko dankwali bata daura ba ko kadan batasan Zayn na dinning ba falo ta sauko kaman zatai kuka tace “Mami yunwa” Mami dake yankema Dad kumba tace “jeki zuba yana dinning” juyawa tayi zatai dinning Zayn tagani zaune yana cin abinci, daure fuska tayi tawuce dinning din ko kallonshi batayiba shima haka ta dauki plate ta saka tuwo tazuba miya da namomi daban daban sanan ta zauna adayan side of the dinning tafara ci Zayn yadan saci kallonta namomin dayagani tazuba saida yasa yakusan tuntsirewa da dariya, ijiye spoon din yayi bayan yaci just little dan shi he’s not a of su tuwo sanan yamike yana rike da glass cup na juice kaman zai zaga ya ijiye wani abu yana zuwa ta bayan Farrah bata ankaraba kawai hannunshi tagani cikin plate na abincin ta ya kwashi namomi iya naman da hannunshi suka iya kwasa dabaisan guda nawa bane, zabura tayi ta mike tareda kwala kara, tace “Mami, Mami kinga Ya Zayn ya debe mini namomi na ko”? Dasauri Zayn yatura namomin abakinshi daidai Mami da Dad najuyowa suka kallosu wani kalan kwarewa Zayn yayi dayasa yafara tari ya watso namomin waje Farrah tahau dariya sosai, Dad yataho wajen harda gudu yakama Zayn din yana bubbugamai baya yace “sorry son, bani ruwa Farrah” ruwan ta tadauka tabama Dad, Dad yakarbi ruwan zaikai bakin Zayn dasauri Zayn yature ruwan yace “bazan sha ruwanta ba Dad” dariya sosai Farrah tayi harda tsalle tamai gwalo tace “eh nima banso kashamin ruwa kasha naka” tsayawa daga Mami har Dad sukayi suna kallonsu juice dinshi Zayn ya kwankwade tass sanan tarin ya tsaya, yakalli Dad yace “Dad kar akara bari tana kwasan nama haka, all she knows how to do is cin abinci babu abinda ta iya” murgudamai baki Farrah tayi yajuya yafice daga dakin fuuuu.
Dad yakalli Farrah dake tsaye har lokacin tana murmushi yace “cinye abincin to azo agyara wajen” gyadama Dad kai tayi dasauri tazauna tace “Dad ni zan gyara dazaran nagama ci, na iya ai ko Mami” Gyadamata kai Mami tayi, Dad yadawo ya zauna, mota Zayn yashiga yafice harzai wuce masallacin su nawaje sai kawai yatuna baiyi salla ba, dan yatsine fuska yayi zagin Farrah na fadomai arai takirashi stupid irresponsible boy&, zai nuna mata he’s responsible kuma yasan abinda yakeyi.
4️⃣5️⃣
Wuraren 10 aka budema Uncle gate yashigo gidan yana kallon ko’ina he can’t wait for lokacin da all this money will be his, saiya gina gidan dayafi wannan kyau yay alkawari, bari Yaya yayama zaman gidan da akasa yayi a asibiti yahuta yadawo office zaisa yakira lawyer shi, anyway mema yasa yacemai yazo da sassafen nan haka.
Wuraren 10 Uncle yashigo falon Mami, tana zaune ita kadai tana duba wani medical book hakanan ga farin glasses a idanunta, gaisawa sukai da Uncle dake sanye da manyan kaya yace “Mami ina Yaya”? Sama Mami ta nunamai tace “yana dakinshi asama” daidai lokacin Dad yahau saukowa daga stairs yaci manyan kaya farare yana kamshi, kallonshi Mami tayi tace “I thought you are still on bed rest ina kuma zaka”? Wani kalan murmushi yayi yazauna kusada ita yace “I will tell you about it idan nadawo yanzu baga Uncle din danki ba he will take care of me don’t worry” kallonshi Mami tayi kaman zatai magana saikuma tai shiru, tashi Dad yayi hakan yasa Uncle shima yatashi yadubi Mami yace “tom saimun dawo” “adawo lafiya” dukowa Dad yayi ya manna mata peck a goshi yace “smile for me Matata” dan murmushi tamai hakan yasa yace “tom natafi, idan Zayn yadawo daga wajen aiki kice nace kada yafita yajirani” gyadamaikai tayi tana kallonshi yafice daga dakin.
Saida suka shige jeep din Dad bodyguards suka rufo kofan sanan Uncle yadubi fuskan Dad yace “Yaya wai ina zaka ka kirani karfe biyun dare kaga yanda naji tsoro nazaci wani abu yama sameka ne, ance kadinga bacci maisawai baka iya bacci, me kake tunani haka”? Dan ijiyan zuciya yasauke ahankali yace “tunanin Zayn kehanani bacci” yadaga kanshi yana kallon bodyguards dinshi dake tuki ahankali yace “when we get on board we will talk about it” gyadamai kai Uncle yayi haka dukansu suka zauna sukai jugum har airport, wannan karan private jet suka shiga saida suka tashi sanan Uncle yakalli Dad dayay nisa atunani yace “Yaya wai ina zamune? Yaya tell me what is going on, wani abu yakuma faruwa ne ko Zayn yamaka wani abune Dan Zayn ne kadai kesa kashiga irin wannan damuwan aduniya” dan ijiyan zuciya Dad yasauke ahankali ya kalli Uncle yace “nayi magana da governor Adamawa yanzu haka motoci na jiranmu a airport dashi gwamnann inaso naje kauyen nan na nemama Zayn auren Farrah, inaso adaura Auren!” Wani kalan kallonshi Uncle yayi gabanshi na bugawa ahankali yace “did Zayn know about this?!” Girgixamai kai Dad yayi yace “hatta mahaifiyar shi batasani ba dan banson any abu dazai batamin hukuncin dana yanke bayan angama komi nakoma gida zan gayamusu” daga Uncle har Dad din shiru sukayi suna kallon juna, murya chan kasa Uncle yace “Yaya kasan aure baya gaban Zayn, banda haka ayanda Zayn yake tayaya zai iya rike Farrah amatsayin mata, bama wannan ba kanaganin Zayn zaiso Farrah she is just 18, Yaya anya wanan decision din naka is right kuwa?” Shiru Dad yayi kafin ya sauke ijiyan zuciya yakalli Uncle yace “bayan abinda yasameni dan zaman gidan nan danayi na hutu I was seriously praying har istikhara nayi kan Zayn bawai hakanan natashi zan hada aurensu ba naga abubuwa da dama na sign da alamomi da Allah ya nuna mini dayasa na natsu da hukuncin dana yanke kan shi da Farrah, da ko maganan kirki basayi but kwanakin nan suna magana suna wasa suna tsokanan juna and nasan is a sign Allah ke nunamin I know what I am doing” yay shiru, sanan ahankali yace “bayan abinda yafaru fushin da ni da mahaifiyarshi mukayi dashi yasa yadan natsu at least bai kara zuwa club ba, akwai mutane danasa ana binshi duk inda yashiga sabida yanzu dakanshi yake driving kar wani abu yakara samunshi yasa bai hiring security personnel sudinga binshi dan har yanzu ban manta cewa akwai people out there dasuke son hurting mini yaro ba, yabar zuwa club ko gidan banza, daga office sai school nasu Farrah kawai yake zuwa haka suka gayamin, yadan fara salla yanzu, yadawo da gemunshi baki, sanan tabama yarage sha sosai though yanasha bawai yadaina bane but yaragu, bansan ko nine ke suspecting nashi ba but I’ve seen him making advances on Farrah!” Yay dan shiru, ahankali Dad yace “da Zayn yama Farrah wani abu gwara na aurar mishi da ita, she’s very young tarayyansu I believe shine sanadin shiryuwanshi dan na nemi zabin Allah kafin nai abin nan, naki fadama Mami dan nasanta bazata taba yarda ba, I know my wife sosai, saisa kaga I am doing this all on my own, kaima I need you to support me” gyadamai kai Uncle yayi yace “to Yaya are you planning on suyi moving zuwa gidansu ko mene” girgizamai kai Dad yayi yace “for now suna gabanmu, we will be monitoring them, Zayn is still 26, inaso nagane menene so, inaso yay developing strong affection for Farrah, yarona baitaba soyayya ba, baitaba son wata ba tunda yake saisa nakeso yaso Farrah matuka ta yanda sonda yakemata zaisa ya chanza, Zayn is a good person idanmu iyayenshi bamu iya mun fito da that good side of him outside ba I believe Farrah can, just trust me” gyadamai kai Uncle yayi ahankali &yace “shikenan Yaya Allah yabada sa’a.
4️⃣6️⃣
12 suka sauka a airport din garin, wasu manyan government cars ne sukazo daukansu da governor Adamawa da kanshi yazo ya tarbi Dad duk gaisawa sukai sosai sanan aka shishiga mota aka kama hanyan akauyen su Farrah da already tuni security personnel sun cika kauyen dan yau sanadin Dad Gwamna zai taka kafanshi a wannan kauyen.
Kusan tafiyan 2hrs yakaisu har kauyen.
Mai gari dawasu manyan mutanen gari ne suka tarbesu sanan aka hadu aka wuce falon mai gari, duk aka zauna kafin kace me mutanen kauye sun taru agaban gidan mai gari ana yada cewa gwamna yazo, saida sukadan natsu sannan Dad yafadi wanda suke nema tukunna da sauri Mai gari ya aika aje akira Malam yazo fada yanzun nan kada yabata lokaci.
Malam na zaune kan tabarma yanacin dafadukan shinkafa da wake dan yanzu rayuwa tai kyau tun kudin da Alhaji yabashi yanzu agarin sune yangayu bayan gidan mai gari, dagashi sai Rakiya ne agidan Inna as usual tanachan gidan nai gari sallama dayaji anata bugawa a kofar gidansu yasa yahakura da abincin yamike yana zura silipas yace “waye, ganinan zuwa” butanshi yadauka yakafa abaki yasha ruwan sanan ya ijiye yay zaure yabude kofa, ganin yaran mai gari Madibbo da babban aminin mai gari yasa yace “ah’ah Tanimu da Modibbo ne, Meya kawoku nan” Tanimu dake kallonshi yace “munyi manya manyan baki a rugar nan, mai gari na neman ka yanzun nan” dan zaro idanu Malam yayi yace “incedai Lafiya” dasauri sukace “lafiya lau muje ance kada mubata lokaci” gyara riganshi Malam yayi yace “to shikenan muje” yana biyedasu abaya har zuwa gidan maigari dayaga kusan duka mutanen karkaransu agaban gidan ga yan sanda nataresu kada su shiga, suna zuwa yaga anbarsu sun wuce faduwa gabanshi yayi yana tunanin mesukayi, suna shiga falon yaga Alhaji (Dad) da wanan kannin nashi (Uncle) dayama ganinsu yaganesu wani bakin yawu yahadiye yana addu’a Allah yasa badai sun gaji da Farrah sun dawomai da ita bane tunda tabar gidan nan gidan yanzu kaman anjanna more kudinsu suke sunaxin dadi hankalinsu kwance yana zaman lafiya da Inna abinshi idan sun dawomai da Farrah ai yashiga uku, waje yasamu ahankali yazauna duk jikinshi yau wani kalan sanyi yace “barkanku da war haka Alhaji dafatan kun iso lafiya, ince bawani abu Farrah tayi kuka dawo da ita ba”? Yay maganan yana karabin falon da kallo yana neman Farrah, murmushi kowa na falon yayi Maigari yace “ba abinda yakawosu ba kennan, abinda yakawosu yafi karfin wannan” wani kalan yankewa gaban malam yayi yafadi yakara kwalalo idanu yace “tooooh” gyaran murya Dad yayi yace “to Alhamdulillah da Allah yasadamu anan wajen gabaki daya” yadanyi shiru yanadan girgiza kai kafin anatse yadubi gwamna yace “gwamna wato kaga Allah yanada yanda yakeyin abubuwan shine sai yanzu nakara gasgata hakan rabo ne yakawo Zayn wanan gari” murmushi gwamna yayi yace “rabone kam yaron dako hanyan dazaibi yazo adamawa bai saniba balle kauyen kudiri” dan murmushi Dad yayi sanan yakalli Malam yace “Malam kasan nai adopting diyarka abisa ka’ida na shari’a dudda hakan bai dauke cewa amusulunce kaine mahaifinta mai asalin iko akanta ba tunda kaine yayan mahaifiyarta uwa daya uba daya saisa yau natako nazo garin nan domin ka” gyadamai kai Malam yayi yana kallonshi shi kawai kalman dayace yake bala’in tsoronji shine suce sun dawo da Farrah kokuma sun gaji da ita zasu maidota, Allah ka dawwamar da ita achan Malam yay addu’an azuciyanshi.
Anatse Dad yace “Malam namo nemawa yarona daka sani Zayn, wanda diyarka Farrah ta taimakamawa awanan gari, nazo nemama d’ana Auren yarka Farrah idan ka yarda” “waiiii!” Malam yafadi yana goge gumin dake ketomai yashiga murmushi yace “Alhamdulillah Alhamdulillah, yooo Alhaji idan ban baku Auren yarnan ba wayema zan bamawa” yasake washe baki yace “kuda kuka mata sutura sannan ni kawunta ma kukamin suruta ai nafadiwa mai gari shatara na arziki dakukamin dan haka Alhaji amatsayina na jinin Farrah, amatsayina na Kawu kuma Uba awajenta nabaku Farrah, ni so samune ma adaura Auren yanzu kubani sadakinta tunda ga mutane daman makil awaje ko mai gari” Malam yay maganan yana washe baki, mai gari ya gyadamusu kai yana murmushi yakalli Modibbo dake gefenshi yace “jekira Alaramma” dasauri Modibbo yatashi, Gwamna yabada ordwr anshigo da goro biscuit da alawa da abubuwa da yawa wanda yasa aka siyo aka loda a booth din mota tun da safe yau dama, nan aka shiga shigo da abubuwa Dad sai washe baki yake yakalli Uncle dake zaune dunkum kaman dusa yace “ciro wayanka kai video komi” gyadamai kai Uncle yayi yaciro wayanshi, Gwamna yace “abar mutane su shigo” kafin kacema fadan yacika makil wasu awaje wasu ta window, liman yatashi atake aka daura aure tsakanin ZAYN GANUWA && FARRAH MUHAMMAD akan sadaki miliyan goma!.
4️⃣7️⃣
Zaune yake a office din Dad yana sanye cikin wani black suit dayamai kyau bana wasaba idan kaganshi da farko baraka yarda Zayn bane dan he’s so concentrating, tunda Dad yabashi aikin nan sai yaune ranan dayasan yazauna ma aikin dan murmushi yayi yadago kanshi dan yagama cikin just how many minutes, hakanan kawai wani kalan faduwa gabanshi yayi dayasa ahankali yakai hannunshi kan kirjinshi yashafa daidai atishawa yazomai dan mikewa yayi tsaye yanabin duka