Showing 27001 words to 30000 words out of 134057 words

Chapter 10 - FARRAH BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MY SHAKUR .txt

24 Jan 2025

7512

tasaki tunda tai wayau yaune rana na farko data taba haduwa da namiji matsoraci, ko Baffa dayake nan siriri baikai Inna kiba ba baida tsoro, rashin mutuncin yake surfafama Inna dudda idanma duka ne zata iya zauneshi ma amman baya tsoron ta balle uban kowa, su Moddibo dabama sukai wannan girma ba suma basuda tsoro amman jibi wanan katon yanda jikinshi ke rawa, tabe baki tayi tadauke kai batare data cire hannunshi daga kan hannunta ba ta jingina da bangon ramin hankalinta kwance ta lumshe idanu dan wani kalan baccin gajiya takeji ko minti uku batayi ba bacci yay awon gaba da ita azaunen, minsharin dayaji taja yasa dasauri yajuyo da kanshi ya kalleta bacci take azaune bayanta jingine da bango tadan dukar da kanta hakan yasa bama ya iya ganin fuskanta sai saman hulanta, mamaki ne ya kasheshi how can she sleep comfortably acikin rami akan wanan dattin? Yana nan inda yake yanajin duka neme nemen shi dasukeyi aka wani kalan tsuge da ruwan sama dayasa yaji sun kwasa dagudu, kalan azababben kishin dayakeji yasa yabude bakinshi ahankali yanajin wani iri but ji yake idan baisha ruwan nan ba zai iya mutuwa, ruwan dake tsiyaya daga ganyayyakin nashiga bakinshi yana hadiya ahaka, saukan ruwan dataji kan fuskanta yasa tabude idanunta ahankali kafin taja hulanta baya tadago kanta ta kalleshi ruwa na fesowa a fuskanta shima kallonta yake, saikuma chan yamaida bakinshi yarufe ganin kaman yanda takeshan ruwan yake kallo, dan yunkurowa kadan tayi taja reshen gefe ta lelleka ganin basanan yasa ta matsar dashi gefe tafito sanan ta tsugunna gaban ramin tamikamai hannu ahankali yakalli hannun nata sanan gently yasaka mata nashi aciki yafito ahankali da taimakonta, mangwaron su ta katse daga jikin reshen sanan tamikamai guda daya kallon mangon yayi sanan yakalli reshen da bolan da aka rufe dasu yanajin amai na zuwan mai tuna ruwan dayasha amman aman yaki zuwa sanan ya girgiza mata kai, maida mangwaron tayi tarike tafara shan nata dan rawa yafara na sanyi dan ruwa ake mai karfin gaske ita ko ajikinta, tafiya tafara da sauri shima yabita yana tafiya da sauri har zuwa gaban dutsenta hawa sukayi sanan suka shiga kogon, waje tanunamai hakan yasa ya zauna akasan ahankali fita gaban kogon tayi sai yanzun nema gabanta yafadi duka tumakan su Shanu daya kawai tagani awajen yana yawo, wani irin kalan mugun faduwa gabanta keyi, dawowa ciki tayi ta zauna sanan ta kalleshi kaman yanda yake kallonta batace mai komi ba.




Ahankali yana kallonta yace “do you have phone please”? Kallonshi ta tsaya tanayi kuri hakan yasa gently yace “kinada waya”? Girgizamai kai tayi alamun batada shi, shiru yadanyi saikuma yasake dago kai yakalleta still tana kallonshi murya chan kasa yace “wani gari ne nan?” Da demonstration tagayamai ganin yanda ya tsaya kuri yana kallonta bai gane abinda take cewa ba yasa tamai alamun tana zuwa tamike tsaye tafice daga kogon bayan riganta yabi da kallo duk jini yabata dutsen da aka buga mata, sauka tayi daga kan kujeran ta kwasa da gudun bala’in sa’i karkaransu ana ruwan nan, direct gidan su Shafa tayi tana shiga taga Shafa ita kadai a kitchen tana soya manja zatai girki, ganinta yasa Shafa tasaki baki tace “yanzu da girmanki kika shiga ruwa kika jike haka Kurma?” Karasawa gaban Shafan tayi tasa hannu ta dagata daga kan kujera sanan tafara gayamata komi a kurmance Shafa nabin labarin tundaga farko har zuwa yanzu, saida tagama tass sanan Shafa ta zaga ta bayanta riganta ta daga ganin taji ciwo sosai yasa tace “waike Farrah maisa bakijin…..” Farrah bata bari takarasa magana ba ta girgiza mata kai sanan tamata alamu itadai tabata wayan, jim Shafa tayi tana kallonta tanason Farrah sama da tunanin Farrah but bataso Farrah taje tasa kanta a matsala, wucewa tayi ta shiga dakin Baban su, wata tsohuwar waya taciro wayan ma akashe tabama Farrah karba Farrah tayi tana murmushi sanan takama hannun Shafa suka fice daga gidan, suna fita ta tuna yanda yakeji tadawo cikin gidan dasauri dakin shafa tashiga ta dauki bargon Shafa dake kan gadon tafito Shafa tabita da kallo sanan tai shiru, gudu sukahauyi nan da nan sukakai wajen, shiga ciki sukayi yana zaune inda Farrah ta barshi sanyin gaske yakeji ya kankame jikinshi warware bargon Farrah tayi ta lullubamai ya sauri yarike bargon sanan tamikamai wayan da Shafa tabashi karba yayi dasauri yana kallon wayan yana dannawa ganin akashe, kugu Shafa tarike tace “kaga Farrah Kurma ce, kuma marainiya ce batada Baba batada Mama, yarinyar nan dakake gani batada gata akauyen nan wahala take, Allah ne kadai gatanta koma wa zaka kira ka kira sabida kafita daga hannunta banson kasamin kawa a matsala” tunda take maganan yake kallonta harta gama, kallon Farrah yayi da itama kallonshi take yanzu daman kurmace, juyowa yayi yakalli Shafa ahankali yace “inane nan?” “Kauyen kudiri” tafadi kai tsaye, murya chan kasa yace “awani gari”? Ahankali tace “garin adamawa” kunna wayan yayi cikin ikon Allah ta kunnu saura one bar, ga service ma kara daya itama rawa take, number Papa yasaka yay dialing yaji ana you have one minute remaining shima ana maganan tana breaking wayan yafara ringing dauka akayi yaji muryan Mami hakan yasa dasauri yace “Mami” muryanta na breaking sosai tace “Hello, Hello” dasauri shima yace “Mami, Mami, is Zayn” duk tsayawa kallonshi suke yanda yake maganan yana fama da wayan yakaita baki yakaita kunne, Shafa tace “ka karamata volume haka Baba keyi idan kawu yakirashi daga binni” da sauri yasa a speaker shima da kyar yagane sabida bai iya amfani da wayan ba “Zayn is that you, muryanka nakej………”. Muryan Mami shi yafito ras awayan daidai wayan ya katse kati yakare, gyadama wayan kai yayi ahankali saiga hawaye sharrrrr yazubo daga idanunshi, ware idanu daga Shafa har Farrah sukayi suna kallonshi, dama kattan maza na kuka, ringing wayan yashigayi hakan yasa dasauri yadauka yasa a speaker wanan karan murya Baban shi yaji kaman ma kuka Alhaji yake dan baya iya magana da kyau yace “Zayn dina kana ina are you okay”? Girgiza kai yayi kaman yana gabansu cikin tsantsan shagwaba yace “I am so scared Papa, please come and get me, I am scared” cikin wani kalan lallashi da so naban mamaki Alhaji yace “stop crying where are you tell me zanzo na daukeka” ahankali yace “kauyen kuduri adamawa state” “adamawa state Innalillahi we are coming with choppers gamunan, kafin nakaraso I am calling the governor na Adamawa stay with this phone okay, wherever you are they’re going to provide you with security, I am coming for you Zayn dina, your father is coming okay” gydamai kai yayi ahankali wani kalan zazzabi na rufeshi jin muryan iyayen shi, suka katse wayan hannunshi yasa akan fuskanshi ya share fuskan nashi tass, sanan ahankali yadago kanshi yakallesu hawaye yagani sun taru a idanun Farrah sosai tana kallonshi, hannunta Shafa takama tace “wuce mutafi tunda za’azo daukanshi wayan idan zai tafi ya ijiye mana anan zamuzo gobe mu dauka” dan kallonshi Farrah tayi kaman yanda shima yake kallonta kafin ahankali tafara tafiya tanabin Shafa dake janta suka fice daga kogon.
This is not a free book chat me up directly by clicking on this link;


wa.me/+2347012181461




💫 FARRAH💫








✍🏻M SHAKUR


Imagine yourself kina kwance a comfort na bed dinki kina duba pictures and videos na hadaddun atampopi kina gamawa kawai ki zaba, place an order, make payment akawo miki har gida batare dakin fita kinje kasuwa ba.




Imagine yourself in the middle of stress da kata kata na biki but you don’t have to worry akan atampopin anko dan akwai wacce zata miki supplying nasu har gida?


Imagine yourself kina tunanin that perfect and best gift dazaki bama kawarki be it birthday gift, wedding gift, suna gift or just casual gift, and M Shakur told you Atampa ne!


Just picture it lokacin da za’a kawo miki atampan acikin wata lafiyayyen fine jaka za’a saka miki atampan akawo miki ba abakin Leda ba kaman yanda aka sabayi a kasuwa?? Sweet right?
What if M Shakur tagaya muku yau all imaginations, dreams dinan naku can become through by introducing ATAMPA REALM to you guys💃
ATAMPA REALM is an online store dake saida atampopi variety of them, daki bari, masu kyau, masu ado, wayanda ake yayi, akan kudi kuma kalilan don’t you want that??
Atampa Realm are life savers, biki, akwati, birthdays or anything they come through and represent!! Ina gayamuku atampopin su makes statement🌹


All you have to do is give them a call 📞 +2348097573597


Ga wayanda basason kira you can chat them up a WhatsApp by clicking on this link:;
wa.me/+2348097573597




You can also follow them on Instagram by clicking on this link;
https://www.instagram.com/p/CiQcu1loZ7c/?igshid=YmMyMTA2M2Y=




You can join their WhatsApp group by clicking on this link;
https://chat.whatsapp.com/CUmRWXy4evqLtOoYp3XmNt












EPISODE 1️⃣2️⃣
Saida suka fita ta tsaya chak hakan yasa Shafa dasuke tafiyan tare tajuya takalleta, cikin fushi tanuna mata kogon tace “wai kinsan shi daga wani waje ne Farrah? Shi namiji ne Farrah ba kamar Yar uwanki datake mace ba, zai iya kare kanshi idan zasumai wani abu, banda ma haka ba yanzun nan agaban mu yay waya za’azo a daukeshi ba eh”? cikin kurmanci Farrah tanuna mata to su tsaya afara zuwa daukanshi kafin sutafi, zuciyanta yaki bata sutafi su barshi tausayinshi takeji sosai, sosai ran Shafa yabaci shiru tadanyi tanabin wajen da kallo sanan takalli Farrah tace “kinsan iya yawan abubuwan dakika fito dasu kiwo? Jibi chan saniya dayace kadai anan, Farrah so kike kisa kanki a matsala ko, meya kamata kiyi yanzu inace ba tumakan nan yakamata kije ki nemo ki tattarosu ki kada gida ba, kinsan wayanan dabbobin sune tattalin arzikin Inna na duniya da lahira ko, wlh ko kasheki tayi wanan karan bazan damu ba babu abinda yashafeni, karma kizo wajena kina kuka ni kinga tafiyata” tawuce zata tafi kaman ance Farrah takalli gabas su Oga ne dukansu hudun suka bullo dawani kalan bala’in sauri tasa hannunta ta fizgo hannun Shafa bama tajira mezata ceba tajata suka shiga kogon jikinta na tsuma, itama Shafan faduwa gabanta yahauyi sosai dan lokacin da Farrah ta fizgota ta hango mazan da bindigogi a hannunsu, kallonsu Zayn yayi ganin yanda suka shigo da gudu suna shaking hakan yasa yadafa bango da kyar ya mike tsaye ya kalli Farrah itama kallonshi tayi sanan ta gyadamai kai alamun eh sune, cikeda bala’in tsoro Shafa tace “sune Farrah?” Gyadamata kai Farrah tayi hakan yasa Shafa tace “kozo muyi sauri mu fice mu gudu karkaran mu muboye achan ni wlh banso na mutu yau” tai maganan tana hanyar kofa tafice dasaurin ta kallon Zayn Farrah tayi sanan tamai alamun yazo sutafi ahankali yabiyota abaya, ganin sun fito yasa su Oga suka hau gudu suma gudu sukahau yi Shafa agaba Farrah abayanta, Zayn abayan Farrah suna saukowa dagakan dutsen da gudun su, harbi sukahau yi amman cikin ikon Allah ko dayansu bai sama ba har suka karasa saukowa, ganin Zayn baya iya gudu sabida hannunshi yasa dasauri Farrah takama hannunshi ahankali ya kalleta daura hannun tayi a shoulder ta sanan tafara gudu shima Zayn na gudu Shafa na gabansu tana famfala gudu, su Oga na binsu abaya sun kusan cimmusu, juyawa Farrah tayi ta kalli bayanta, ganin Oga na saita bindiga saitin Zayn dake wani kalan haki yana gudu yasa dawani kalan sauri tasaki hannun Zayn tawani irin hankadeshi yafadi ta tare bullet din sai gefen kirjinta wani irin kara tayi ! bullet na nan ne kaman garwashi dake tattare dawuka mai kaifi, the pain is so sharp da saikaji kaman kabar duniya chak Shafa ta tsaya jin ihun Farrah daidai Farrah tawani irin faduwa akasa jini nawani kalan bulbulowa ta inda aka harbetan, juyowa Shafa tayi ganin Farrah azube akasa yasa tawani kalan Kurma ihu. “Kurmaaaaaaaa!” Sanan tawani taho kanta dagudu ta tsugunna shima Zayn dake kasa tashi yayi da sauri yana kallon Farrah da bala’in mamaki na she just saved him yama kasa tabuka komi sai rawan da hannunshi keyi kawai, murmushi Oga yayi yana tahowa cikin tafiya na kasaita yace “perfect haka ake harbi nakoya muku saiti nakoya muku amman abanza yau kun wasting bullets abanza a hofi” wani kalan rudewa Shafa tayi yanda taga jini na bulbulowa Farrah na tari yasa tasa hannu ta dumbuzo kasa ta maka akan ramin bullet din tana kuka takalli su Oga tace “Allah saiya kashe ku kuma azzalum……” bata karashe maganan ba sabida wasu kalan jiniyan motocin yan sanda dasukaji na tashi ata ko’ina sanan ga mutanen gari sun fara bullowa sabida karan harbin dasuka dingayi dazu ko’ina ya amsa, gakuma karan helicopters kusan uku dayasa su Oga suka kalkalli sama jikinsu nawani irin rawa, cikin ihu ganin mutane yasa Shafa tace “ku kamasu su yan sanda sukazo kamawa masu kidmashin ne” mazan gari suka yunkuro hakan yasa suka kwasa da gudu daidai lokacin motocin yan sanda na shigowa dajin, dan sunada device dake tracking bullet kaman magnet ne zai kaika wajen da akwai bullet, ga jirage nayawo asama, wani kalan ajiyan zuciya yasauke yana kallon yanda Shafa ke jijjiga Farrah dake tari har lokacin idanunta sunyi jajir suna fitarda hawaye, wasu manyan sojoji suka taho da microphone suna kiran sunan Zayn. “Zayn Ganuwa are you here”? Shiru Zayn yayi dan at this point iyayenshi kawai zai gani ya mike tsaye, helicopter su yasauka daga nesa sosai a filin, Mami dakuma Baban shi yaga sun sauko daga ciki, da Uncle, dawasu manyan Doctors ganin su yasa yamike tsaye ahankali yafara tafiya.






Daga nesa Alhaji yace “Innalillahi Zayn dina ne haka, Zayn” wani kalan fadawa jikinshi Zayn yayi ya kankameshi sai kuka ahankali, tsayawa Mami tayi a gefe tasa bakin gyalenta tana share hawaye ganin yaronta is fine, da kyar Alhaji yasakeshi sanan yay cupping fuskanshi yace “kowaye yamaka Wanan abun I will not rest sai justice yay taking place” gyadama Baban shi kai yayi sanan yasaki Dad yajuyo yakalli Mamin shi budemai hannu tayi hakan yasa yarungumeta ahankali ita tama kasa magana jin jikinshi zafi yasa tadagoshi kafinma tai magana Alhaji yakamashi yakalli Drs din yace “mu tafi sai su dubaka a jirgi” shida Baban shi suka wuce Doctors din suka bisu abaya, ajiyan zuciya Mami ta sauke sanan ahankali tadaga kafanta zata wuce kaman ance ta kalli wajensu Shafa dake jijjiga Farrah da idanunta ke kullewa idanunta suka sauka kan wasu yara biyu da dukansu ke sanye da kayan fulani daya na kwance akasa ga jini duk yabata riganta daya na rikeda ita tana kuka sosai dawani irin sauri Mami tace “Alhaji!” Tsayawa Dad yayi sanan yajuyo dasauri Mami tai wajensu Farrah ta tsugunna kansu takai yatsunta biyu ta taba gefen wuyan Farrah sanan tace “we have a gun short injury, bring first aid kit for me” Mami tai maganan cikin sauri tana ihu sanan takalli Shafa dake kuka sosai tace “kanwarki ce Ya akayi aka harbeta”? cikin kuka sosai Shafa tace “garin taimakon danku ne!” Chak Mami ta tsayar da abinda takeyi takalli Shafan, Gyadamata kai tayi cikin kuka sosai tace “tafito kiwo taga……..” nan takorama Mami labarin tassss wani iri jikin Mami yayi daidai one of the Doctors yakawo first aid kid, Ahankali tadago kanta takalli Zayn dake kallonsu yana tsaye tareda Baban shi sanan tasa hannu ta karbi first aid kit din tabude tawanke kasan da Shafa tazuba awajen tamata allura daidai Malam dashima yaji labari abinda ke faruwa awajen garinsu yataho wajen ganin Farrah ga likitoci akanta yasa da sauri yataho wajen yace “Maiya sami Farrah Shafa’atu”? Daidai lokacin Mami tagama abinda take tadago takalleshi sanan tamike tsaye ahankali tace “kaine mahaifinta Malam”? Girgizama Mami kai Malam yayi ganin babban mace yace “a’a diyar kanwata ce, marainiya ce babu uwa babu uba saini kadai” wani abu Mami taji ya tsayamata arai, anatse tace “an harbe diyarka garin kokarinta na taimakon d’ana, inaso idan ka yarda mu tafi da ita asibiti dole amata aiki acire bullet din, zaka iya biyomu idan yaso idan taji sauki sai adawo daku” kallonta Malam yayi sanan yabi yan sanda da sojoji da jiragen dake yawo asama, da wanda yake akasa, da yaron dayaga an lullube da bargo nai kyau yana tsaye kusada mahaifinshi dasuke kama wanda kana gani kasan shine yan kidmashin din suka kama daga ganinsu kaga yan birni masu kudi, ba yan yankan kai bane tunda ga yan sanda, lokacin yin kudinshi yayi yasan idan aka gama aikin zaa dawo dasu dole abasu kudi dayawa hakan yasa yace “to muje” wani gado aka kawo aka dauketa akai jirgin da ita suka shiga Mami na kusada ita tana monitoring heartbeat nata shikuma Zayn na zaune kusada Baban shi yay lakur ajikinshi sauran Drs na dubashi, shikuma Malam na zaune kusada yan sanda ya kankame jikinshi yanaji kaman Zai shide jinshi asama, tass Dr yaduba hannun Zayn sanan yakalli Alhaji yace “waya maka daurin hannun nan koma waye really saved his life daurin yayi kyau sama da wanda mu zama mumai a asibiti, idanunshi ne kawai needs work” ahankali Alhaji yace “waya maka daurin hannun?” Farrah yanuna murmushi Alhaji yayi yace “I will makesure I reward her awesomely for helping my son, for giving her life for you, me kakeso abata” murya chan kasa yace “anything” wani mugun kallo Mami tamai ita kanta tarasa gane kan wani kalan yaro ta haifa yanzu inda bataga Yarinyar nan ba da haka Zayn zai barta tamutu yarinyar data taimakeshi ta karbi bullet that was meant for him, ace Zayn yakasa fadi an harbeta adubata shi takanshi yakEe, ajiyan zuciya tayi ta zubama fuskan Farrah idanu.




💫 FARRAH 💫




✍🏻M SHAKUR




EPISODE 1️⃣3️⃣
Direct wani babban asibitin da Mami ke aiki suka wuce dasukakai Abuja, jikin manya manyan likitoci har rawa yake aka wuce wani observation room da Zayn, dakin daza’ayi mai general check up kafin eye Doctors suganshi, Mami kuma scrubbing in tayi dan itace in charge surgeon ma Farrah she just feel this is the least she can do for the small brave girl after saving her son’s life, shikuma Alhaji zama yayi acikin wani executive lounge da only VVIP guest dinsu ake bamawa, Malam dai yadawo dan kallo yana tareda su amman bai zauna akan kujeran da Alhaji da Uncle ke kai ba dan sunmai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login