Showing 9001 words to 12000 words out of 134057 words

Chapter 4 - FARRAH BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MY SHAKUR .txt

24 Jan 2025

7509

the limit dazata dauki iskancin Zayn, budemai kofa Alhaji yayi zai fita cikin kakkausan murya Ummi tace “Zayn!” Chak ya tsaya batare daya juyoba, cikeda fada Alhaji yakalleta yace “wai mekuma baraki barmin yaro yahuta ba”? Cikeda bacin rai Ummi tace “Alhaji enough please! Ba gata kake ma yaron nan ba wlh, iyayenshi ne nan zaune sun taso tundaga various bangare nasu sunzo nan dan sugaida Zayn wanda bahaka yakamata ba ai shine dansu shiya kamata yaje one after the other ya gaidasu iyayenshi ne, yanzu kuma sunzo sun gama jiranshi yace yagaji bacci yakeji su dawo anjima sabida zamanshi suke wani irin rashin da’a da tarbi……” Kul! Alhaji yafadi cikeda bacin rai yana nuna Ummi da yatsa yace “kada kisake ki kira yaro na mara tarbiya kafin kija bakinki yabishi, idan bakison yaron nan ne kigayamin zan daukomai the best Nany in this entire world dazata dinga kulamin dashi, inda ma na iya girki kin zaci zan bari d’ana yadingacin abincin wasu ne konaki ma? Jarabanki, masifanki, korafinki da damuwanki yasa Zayn bayason zaman gidan nan bayason dawowa Nigeria sabida kin tasashi agaba yi wanan bar wanan haba, kinsan irin wahalan danasha kafin nasamu ya yarda yadawo Nigeria, kinsan awa nawa yayi cikin jirgi yanzun nan yadawo yaci abinci yagaji yanajin bacci nace sudawo anjima su gaidashi barasu dawo bane! Akwai wanda ya isa yajadani cikinku ne, dukanku nan zaman mahaifinshi kuke, nace anjima adawo agaida Zayn akwai wanda ya isa yajadahakan ne!” Yabuga uban ihu dasauri Hajiya Hadiza tamike tana yake cikin makirci tace “Ahhh abu yay zafi Alhaji kamata hakuri, babu wanda ya isa yaja dakai, zaman ka mukeyi wlh! kasan Shafa’atu har yanzu yarinya ce, wani zubin gidan dakataso ma yana affecting mutum, kaga muda muka taso gidan masu shi munsan yanda akeji da yara, yaran mu sune number one kome sukeso yazauna, yan gidan talakawa dama haka suke sai hakuri, basusan menene ririta danda suka haifaba saidai su wulakanta shi, bama su iya son yaransu ba sabida basu taso cikin gata ba, Zayn yaje yay bacci abinshi anjima ma dawo, Zayn Son sorry kaji anata bata maka rai daga zuwanka, uwarka sai ahankali, Alhaji ayakuri dan Allah” yanda Alhaji yaji dadin magananta ko baisan lokacin daya tura hannunshi a aljihunshi yaciro key wata Babban jeep nashi that worth 70M yajefa mata yace “nabaki motata Hadiza” wani irin ihu tayi tazube akasa shikuma Alhaji yakama hannun Zayn dayadan saci kallon Ummi datai jugum azaune tana kallonshi suka wuce suka fita zuwa bangaren shi.










Tashi Hajiya Fatima tayi cikeda bakinciki da kishin Hajiya Hadiza tafice fuuu daga dakin, sanan itakuma Hajiya Maryam ta tashi tana dan kakalo murmushi tace “akashe lpy Hajiya Hadiza” sanan takalli Ummi tace “sai anjima Hajiya” Gyadamata kai kawai Ummi tayi takasa magana, saida tagama dariyanta Tsaf sanan tamike tsaye takalli Ummi daga sama har kasa tace “ohh’uhh ni wlh har tausayi kike bani dan banga banbancinki da mu dabamu haihunma Alhaji ba, da wanan haihuwa ai gwara bakayiba, yaro bayajin maganan ki baki isa dashi ba, baki isa ki tofa wani zance kanshi ba ubanshi ya hayayyako miki kina bani tausayi Ummi” tawani kwashe da dariya tana juya key motan hannunta tace “jibi kyautan motan dana samu Allahu Akbar” takara kecewa da dariya sanan takalleta tace “dan da ake mana gadara dashi ana daddaga mana kafada kalleshi, da inhaifi d’a dai irin danki Ummi gwara na mutu bantaba haihuwa ba, wai inata cewa danki, dan mijinki” tasake kecewa da dariya sanan tawuce tafita daga dakin tai waje Ummi jitayi hawaye sun saukomata daga idanu sharrrrr dasauri tasa hannu ta share, duk gidan nan kap itace tafito daga gidan talakawa, bayan tagama secondary school taci scholarship da Alhaji ke bayarwa every year taje takaranci medicine gynecology, ranan da tai graduating a ranan ne tafara ganin Alhaji sabida angayaceshi yazo yaga graduation na yaran dayabama scholarship kuma a ranan yaga Ummi yaji yanaso itace matarshi tabiyu, Hadiza ce babba sai ita sai Fatima sai Maryam ta karshe




💫 FARRAH💫






✍🏻M Shakur






4️⃣
Tadade zaune awajen sanan ta mike tsaye ahankali sama tawuce tana nunama yan aikin dinning alamun su gyara wajen tabude wani daki da cikinshi zaka dauka kana wata duniyan ne ta shiga ciki ta maida kofan tarufe, wayan ta dake kan gado ta dauka ahankali sanan ta zauna taciro number datai saving da Mama tai dialing ringing daya aka dauka daga ta dayan bangaren zaka iyajin murya wacce ta kwan biyu aduniya kaman muryan tsohuwa tace “Jikana ya iso Ummi?” Gyadakai tayi sanan ahankali tace “eh Mama, Zayn ya iso” muryanta kadai Mama taji tasan akwai wani abu dake damunta, cikeda kulawa dakuma damuwa tace “ke likita menene, meya faru”? Dan jim tayi sanan ahankali tace “Mama Allah yasani ina iyakan bakin kokarina wurin bama Zayn tarbiya amman Mama idan kinga Zayn ko saikin firgice, rashin jinshi dakika sani da bakomi bane yanzu ne yake asalin rashin ji, Mama Zayn yadada baci sama da da, Alhaji bayaganin hakan, soyayyan dayakema yaron ya makantar dashi, Mama kinsan ko yanzu kafin yadawo dinan Uncle yatura da bodyguards rututu akaje aka taho dashi da karfi da yaji shi kanshi mahaifin nashi fushi yake dashi, Mama Zayn baya kallon uban kowa da daraja ko mahimmaci hatta ni, Mama Zayn sai wulakanci da rashin da’a da………” “Ummi” Mama takirata cikeda natsuwa hakan yasa ta yanke magananta tace “Na’am Mama” ahankali Mama tace “Ummi nasha gayamiki yaro ba wani abu bane dazaki shiga shago kibada kalan design din dakikeso daza’a keramiki yazo miki ayanda kikeso ba, Yara sai wanda Allah yaga daman baka zai baka, iyawanshi ne, ni nan sama da kowa nasan yanda kike iyakan bakin kokarinki kan Zayn tun yana yaro nasani Ummi, dan haka abu daya zuwa biyu zan fada miki, yanzu dai inaso karki kara zubarmada Zayn hawaye, dan hawayenki zai iya binshi uwa ba abun wasa bane” gyadama Mama kai tayi ahankali Mama tace “ki dage da yima Zayn addu’a karki sake ki gaji, ki tabbatar sallolin dakikeyi na farilla sau biyar arana cikin kowacce saikinma Zayn addu’a, sai shawara ta biyu wanda manya kadai zasu iya baki shawaran nan, Ummi” ahankali tace “Na’am Mama” anatse Mama tace “ki kyautata ma wasu yaran, duk inda zakiga wani yaro dakeda bukatan wani abu na taimako koma wani iri ne inhar kinada shi to ki kyautata musu, sanan kimusu addu’a, duk addu’an dakikama wasu yaran malaiku zasuma naki, dan haka ki rike wanan sirrin da kyau ki kyautatama wasu yaran kisakasu farin ciki Allah zai iya amfani da wanan ya shiryan miki da naki dan kinjini ko” ahankali tace “eh” Mama tace “Allah yamiki Albarka, Allah yacigaba da daukakaki yasamiki albarka a aikin ki, Allah ya shiryarmiki da danki yamai albarka, bari na shiga gidan Safiya ta haihu zanma jariri wanka” murmushi tayi tace “Mama kedai da yima jarirai wanka baki gajiya, to Allah raya” Ameen Mama ta amsa sanan ta katse wayan, ahankali ta ijiye wayan kan gado tana sauke ijiyan zuciya jitayi duk wani nauyi da bakincikin datakeji azuciyanta yabace wato uwa daban ce, ita har mantawa ma take tayi girma wlh. Shiru takarayi tunanin Zayn nakara lullube fuskanta batasan mesa ba Alhaji gani yake ta tsani Zayn tana takuramai bata sonshi zata iya rantsewa da ace za’a tsaga zuciyanta a tsaga na Alhaji za’agani cewa son datakema Zayn yafi na Alhaji sau dubu, Zayn shine farin cikin rayuwanta, shine kadai abinda takedashi aduniya dazata kalla taji dadi, she loves her son a whole lot kawai bazata iya kyale kuskuren shi bane, huhhhh! Ajiyan zuciya ta sauke ahankali sanan tamike ta shiga bayi dan dauro alwala.








Saida Alhaji ya tabbatar bacci yay awon gaba dashi sanan yazare hannayenshi daga cikin gashin kanshi dan sosamai kai yakeyi saisa yayi bacci, tun yana yaro yakeson ana sosamai kai tareda dan massage nan da nan zakaga yay bacci, kwalin taba yaga ya leko daga aljihun riganshi, ahankali Alhaji yasa hannu yadauki kwalin yana karantawa sanan gentle yabude kwalin, karan tabane aciki guda 6 da lighter mai kyau, wani irin ijiyan zuciya Alhaji yasauke ahankali sanan yace “why Son?” Har cikin ranshi baiso Zayn yafara shan taba ba amman kuma bazai iya hanashi ba shifa komenene inhar zaisa Zayn farin ciki zai iyamai, kawai maidamai kwalin yayi a aljihu yace “dasauki taba kakesha ba giya ba ko wiwi, shima kuma taban nan gaba zaka daina duk kuruciyane ke damunka” sanan yatashi ahankali yay folding hannunshi akirji yana kallonshi kaman zai hadiyeshi, aduniyan nan kap baida abinda yakeso kaman yaron nan, shi kanshi baisan iya adadin son dayakemai ba, baiso daidai da sauro yacije shi balle kuma uwa uba mutum yabatama dan shi rai ai sai inda karfinshi yakare kodako mahaifiyar shi ce, indai kanaso kaci riba dashi kasamu kome kakeso daga wajenshi to kabiyo ta hannun Zayn, takalmin kafanshi yabi da kallo hakan yasa yazo bakin royal bed din ya ciremai takalmin yana kallon yatsun kafanshi komi na Zayn irin nashi ne wato da Allah yatashi mai kyautan Zayn yamai kyautan ne nagata dan yaro yabashi da komi sak nashi ya dauko jibidai farin fatan mahaifiyarshi mamarshi kaman baturiya dan Fulani ce ita amman bai dauko haskenta ba bakin fatar Babban shi ya dauko sak babu wani banbanci, murmushi Alhaji yakara yi sanan yaja bargo ya rufamai kafin yakara dukowa yatofamai addu’a sanan yabude wani sliding glass door yafito daga bedroom din, wasu bodyguards guda 4 ne gaban bedroom din ganinshi duk suka zube alamun gaisuwa, bama takansu yabiba yace “Zayn is asleep, dazaran yatashi akwai almond milk dinshi da honey nahadamai a glass cup kusada shi kubashi yasha sanan kumai setting ruwan wanka yayi daganan saiku barshi” dasauri sukace “yes sir” sanan yawuce yafita.






Wuraren 6 na yamma yatashi, shifa yanada son bacci, kuma yawanci yana baccin ne sabida baya na dare, dare yana club, bin dakin dayake yayi da kallo hakan yasa yaja dan gajeren tsaki tunawa dayayi yana Nigeria he’s not just happy, ahankali yatashi zaune yana bin dakin da kallo, ganin milk nashi akan side drawer yasan aikin Baban shine yasa ahankali yamika hannu yadauka yakai baki yanasha ahankali harsaida ya shanye sanan yatashi tsaye da kyar yana kara yatsine fuska wani haushi na kamashi ya danna wani botur a bango” da gudu all the bodyguards suka shigo dakin, tsaki yayi awulakance yace “I need just one person out!” Yay maganan kaman yanama kashi magana, duk wucewa sukayi suka fita daya ya tsaya wanda yake babban su, akufule Zayn yace “bakasan abinda yakamata kayi ba” wucewa dasauri yayi yashiga bayin ganin yariga ya shanye madaran, hadamai bubble bath yayi da ruwa mai dumi sosai sanan yafito, wani mugun kallo yakaramai yace “get out” wucewa yayi yafita shikuma yashiga cire kayanshi ahankali anan kasan dakin yabarsu yawuce yashiga bayin, idan kaga bayin zaka iya ranstewa ba bayi bane dan harda wani durmemen tv ne aciki, ga flowers ta ko’ina, shiga ruwan yayi yayi resting head nashi sanan yadauki remote ya chanza tashi zuwa na kwallo kafin ya ijiye remote din yanadan yatsine fuska wankan ma bashi wahala yake kaman amai, danna wani botur yayi dasauri bodyguard din yazo gaban bayin dan baima rufe kofa ba yace “yes Sir” “my cigarettes in my cloth” yay maganan agajiye kaman baiso yayi, kayan daya cire bodyguard din yashiga duddubawa ganin kwalin taba da lighter aciki yasa yashigo bayin yakawomai hannu yasa ya karba sanan yawuce yatafi, kunna tabar yayi yakai bakinshi ya zuko, wani kalan dadi yaji yadan lumshe idanu sanan ya fuzar da hayakin yana tunani saida yasha kusan kara 5 abayin sanan yay wankan da kyar yay wankan tsarki yafito yana daure dawani tsinannen towel dan karami a waist ya zauna kan kujera dake dakin yakara danna botur din dake wajen wani bodyguard ya shigo kafinma agayamai yasan mezaiyi bayi ya shiga ya wanko hannayenshi tass sanan yaje closet nashi yadauko wasu lafiyayyun cream kaman na mata yazo yana shafamai ko ajikinshi danna wayama yake saida aka gama sanan yafitomai da kayan dazai saka kallon kayan yayi native ne hakan yasa yace “get me english wears, i wants shorts, sneakers, neck chair, a t-shirts with my perfumes” komawa closet din yayi wani Kenzo belted straight short dark blue yadaukomai da dolce gabana white logo print t-shirt, sai Rick owens clip fastening neck chain silver, sai wani Bell & Ross 40MM diamond writs watch dawani Nike Air Force high top sneakers, saikuma wani farin singlet na CK da boxer ma na CK, da all turarukan shi yakawo mai, ganin kayan sunmai yasa da yatsa yamai alamun ya ijiye ya fice, ajiyewa yayi yawuce yafita shikuma yatashi ya shirya cikin kayan dasuka amsheshi sosai kaganshi kokai waye saika kara juyowa ka kalleshi sabida kalan kyan dayayi kana ganinshi kaga rich Bobo, wayanshi yadauka a hannu da kwalin tabanshi sanan yafito daga bedroom din saiga Baban shi dan tsayawa yayi ganinshi hakan yasa Alhaji yakaraso dasauri cikin falon yana kallonshi yace “wanan kyau haka da Son dina yayi sai ina”? Hannu yamikamai ahankali yace “car keys Papa” dan kallonshi Alhaji yayi sanan cikeda lallashi yace “Zayn nadauka yau hutawa zakayi ina kuma zaka daga zuwanka” hade fuska yayi yace “ka dawo dani against my will are you trying to ground me ne kuma yanzu” dasauri Alhaji yace “no no nooo, Zayn kasan duk inda zaka anan Nigeria u cannot go alone, nasan bazakaso hakan ba amman kayakuri nan ba Indiana bane please my Son, kaji yaron Albarka, nasan nama laifi but banace maka sorry ba” Alhaji yakara matsowa kusadashi sanan yadaura hannunshi yakama kafadarshi anatse yace “your Dad have so many enemies Zayn, inada yan adawa dani kaina bansan iya yawansu ba, kuma wanan da next meeting namu da board na directors dudda ban fadama kowaba but I am planning to announce you as the new CMD, inaso nabarmaka komi nawa nahuta na tsufa Zayn baka gani ba, so please Zayn dina you should be careful, ko’ina zaka go with bodyguards naka, go with them do that for your Papa please my son” yanda yaga Baban shi na lallabashi tunda ya iso garin nan yasa yaji yadan bashi tausayi, shi bawai ta CMD shi ko menene yakeba all he wants is kawai yafita yaji dadi, murmushi ya kakalo sanan ya gyadama Alhaji kai ahankali alamun ya yarda dasauri Alhaji yace “ka yarda bodyguards sudinga binka”? In a very very lazy voice yace “yes Paapa” wani irin dadi Alhaji yaji yaciro key mota daga aljihun shi yarike a hannu sanan yace muje waje kaga motan ka, waje sukayi bodyguards su hudun na binsu abaya wajen wata wild car Alhaji ya taaya sabuwa fil ko bare ledan kujerun ba’ayiba sanan yabama babban bodyguard din key motan yace “drive safe, kubiyu zaku dinga binshi” sanan yakalli Zayn din yace “ankira magrib muyi salla kafin kafita ko”yatsine fuska yayi ahankali yace “zanyi ahanya Papa” “tom adawo lpy, ku kulan mini da d’ana” atare sukace “yes sir” sanan daya yabudema Zayn din bayan mota, ahankali yatako yashiga bayan ya zauna sanan yamaida kofan yarufe yakoma gama ya zauna bodyguard dake tukin yaja motan Alhaji na daga musu hannu suka fice.




Wani kalan ijiyan zuciya Zayn yasaki murya chan kasa yace “I hate this house” murya chan kasa yace “take me to Area 3 Old lady’s house”…..








*****
Har sukakai kofar gidansu Shafa bata cemata komiba kan dakalin dake kofar gidan Shafa ta zauna tace “jeki juye ruwan kifito” ciki tawuce taje tajuye ruwan tafito rike da empty tulun tana kokarin daurawa aka Shafa tamike tasa hannu ta fizge tulun cikin fushi tai gaba tace “bazaki kara komawa rafin nan ba muje gidan mu nabaki ruwan mu kikai” tai gaba dasauri Farrah ke binta har zuwa gidan su babu kowa agidan ko’ina tsaf tsaf saida sukaje gaban babban randansu sanan Shafa ta sauke tulun tashiga deban ruwa tana zubawa aciki gabanta Farrah taje ahankali tamika mata biscuit din alamun ta amsa wani kalan mugun kallo Shafa ta mata saikuma cikeda masifa ta yarda kofin datake deban ruwa dashi ta kalli Farrah tace “waike maisa wawiyace ke kurma eh? Kinfiso ayita cin zalunki aduniyan nan? Maisa bazaki tsayawa kanki ba sabida kinga bakida kowa bakida gata ke barakima kanki gata ba iyye? Ni wlh abin namin ciwo idan ana cin zalinki abin namin ciwo” kawai Shafa tadaura hannuwanta biyu akan fuskanta sabida kukan dataji yazo mata dasauri bataso taga ana zaluntar Kurman nan har cikin zuciyanta takejin abin, wani irin sanyi jikin Farrah yayi ganin Shafa na kuka bata taba ganin Shafa na kuka ba sai yau yarda biscuit din tayi akasa sanan ahankali takai hannunta tacire hannun Shafa dake kan idanunta tasaukar da su kasa hawaye na fitowa daga idanunta kaman yanda Shafa itama hawaye ke zubowa daga idanunta dawani irin sauri ta rungume Shafa tana kuka sosai, sunkai kusan minti biyu dukansu suna kuka da kyar Shafa ta hadiye nata takai hannunta tashare fuskanta sanan tadago Farrah daga jikinta tana kallon yanda take kuka tace “dalla to ai nadena kukan kema kidaina” girgiza mata kai Farrah tayi tana kuka, ahankali Shafa takai hannunta tagoge mata fuska tace “karki damu watarana sai labari kinji, Allah shine masanin gobe Kurma ke marainiya ce bakida uwa bakida uba kokuma ince babu wanda yasan ubanki, duk wanda yaci zalin maraya zaiga sakayya kiyakuri kinji amman kuma daga yanzu zaki dinga tsayawa kanki kinajina” dasauri Kurman ta Gyadamata kai, hannunta Shafa takama taja zuwa dakinsu madubi tadauko suka fito waje sanan ta kama hannun Kurman tasamata madubin aciki tace “kalli kanki kurma, tunda nake akauyen nan bantaba ganin yarinya mai kyau kyakkywa datafi kowa gashi ba dudda muna karkaran fulani kowa nada gashi amman kinfi kowa tashi irin ki ba, kalli yanda suka zamar da ke, kalli jikinki” Shafa taja wuyan riganta ta bude shoulder nata duk tabon duka, tace “ke mace ce kinga Inna tana cemin baikamata diya mace nada tabo ajikinta ba sabida zatai aure, miji bayason tabo ajikin matarshi, su Rakiya da Mamanta na neman lalataki, su wulakantaki sabida sunga bakida kowa amman basusan kinada Allah ba sanan kinada ni, karki kara yarda wani yadakeki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login