Showing 111001 words to 114000 words out of 134057 words

Chapter 38 - FARRAH BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MY SHAKUR .txt

24 Jan 2025

7522

Hajiya adaure for attempt murder na dana dakuma kidnapping but yanzu data fadi har dan uwana I cannot do anything” yasakeyin shiru sannan yakalli Zayn yace “kawomin journal dina da pen” tashi Zayn yayi yay sama agaban bene yaga Farrah tsaye idanunta sunyi ja, Shafa ma haka” wucesu yayi zuwa dakin Dad yadauko journal yadawo kasa yabama Dad atake yarubutama kowaccen su saki bibbiyu daman duk yataba musu saki daddaya sabida Zayn yanzu yabasu biyun daya rage, sannan yay waya yasa aturomai manya manyan trailer da ma’aikata yanason duka kayayyakinsu afitarmai dasu daga gida harta plate na Dakinsu baiso abari sannan ya ijiye wayan ahankali yasake sauke ijiyan zuciya yakalli Mami yace “zaki iya rike Layla tunda batada iyaye”? Shiru Mami tayi batace komiba hakan yasa da sauri Layla tahade hannayen ta biyu tana kallon Zayn da Dad tace “Dad the greatest gift dazaka bani aduniyan nan shine Auren danka, Dad inason Zayn kaman zuciyata zata buga, wlh idan ban auri Zayn ba zan iya mutuwa, dan Allah Dad kurufamin asiri” ta wutsiyar idanu Zayn yakalli Farrah dake tsaye sama gaban bene tana kallon Layla idanunta sunyi jaa gawani kalan wutan kishi daya hango cikinsu dan murmushi yayi azuciyanshi, baki Dad yabude zaiyi magana Zayn yace “I will marry you Layla!” wani mugun bugawa gaban Farrah yayi saida tai wani baya zata fadi da bala’in sauri Shafa ta tareta, Zayn yakalli daga Dad har Mami dake kallonshi baki sake yace “Dad arrange the marriage inaso muyi aure nan da 7days” ganin yanda Dad da Mami ke kallonshi baki sake yace “chill after all she just saved yaronku from those evil people she betray her Mommy for me kodan hakan ta canchanci na aureta dan haka I will marry her” yatashi daga kan kujeran zuwa inda Layla take zaune akasa ahankali yadaura both hands nashi kan kafadarta yadagota tamike tsaye yace “daga yanzu you will be staying here har zuwa rannan aurenmu akaiki gidana okay” wani kalan gyadamai kai Layla tayi tana kuka sosai hannunshi yadaura kan lips nashi yace “shiiiiiii” dawani kalan rinanun idanu Farrah takalleshi daga sama tana tuna yanda yake cemata shiiiii harma yadaura hannunshi akan lips nata, ahankali yace “let’s go lemme take u to your room” ahankali yana rikeda kafadarta yay stairs da ita suna hawa ahankali suna sama, ko kallon inda Farrah take baiyiba yawuce da ita dakin dayake gaban na Farrah wanda daga dakin Farrah sai dakin yabude ahankali yashiga da ita har zuwa gaban gado, dan kallon kofan yayi hakanan yanaji ajikinshi Farrah zatazo inhar tazo tanason shi inhar batazo ba dagaske bata sonshi.






Wani kalan fizge kanta Farrah tayi daga hannun Shafa idanunta har duhu duhu sukemata kaman bata cikin hayyacinta tashiga tafiya tana tangal tangal Shafa na kallonta batare data bitaba, gaban dakin da Zayn yashiga da Layla ta tsaya tana kallon dakin ita kadai tasan metakeji azuciyanta bazama ta iya misaltawa ba jitake kaman ta mutu, ahankali tadaura hannunta kan handle na kofan, ji ajikinshi Zayn yayi Farrah na gaban dakin hakan yasa yakalli Layla dake kuka sosai har lokacin dan takasa yarda Zayn yace zai aureta yakai hannunshi kan fuskanta yace “stop crying is okay I am your now” wani kalan fadawa tayi jikinshi ta kankameshi sosai daidai Farrah nabude kofan, ganin Layla jikin Zayn ta kankameshi gam tana kuka yana shafa bayanta yasa taji wani jiri zai kwasheta da sauri tadafa bango tana wani kalan nishi tanaji kaman an dauramata block akan zuciya.






VIPs so for the first time I will use opinion naku.
Listen VIPs normally few pages yarage nagama book dinnan, but yanzu should I take another turn in this book kunaso???


Bantaba book na kishiya ba nabari Zayn yama Farrah kishiya????


Ko kawai I should just end my book???


Say your mind❤️




7️⃣4️⃣










Dago kanshi Zayn yayi yazubamata wasu mugayen idanu babu alamun wasa akan idanunshi kaman bai santa ba yace “lafiya what are you looking for here?” Dasauri Layla dataji Zayn yay magana tajuyo da kanta tana jikinshi still takalli kofa ganin Farrah tsaye tana kallonsu ta dafa bango idanunta sunyi jajir yasa tai wani kalan murmushi takara kankame Zayn tana sauke ijiyan zuciya tana kallon Farrah dake kallonsu, da yatsa Zayn yanuna mata kofa yace “get out and shut the door” tsabagen abinda takeji tama kasa motsi da kafa jin ankama hannunta yasa tajuyo da rinanun idanunta Shafa ce, ahankali takamata tareda janta batare datai magana ba suka wuce dakinsu ta shiga da ita kaman jira Farrah take tawani duke awajen tareda fashewa da kuka, maida kofan ahankali Shafa tayi tarufe sanan tajuyo ta kalleta tace “yanzu kukan menene kikeyi Kurma? I thought kince baki sonshi guduwa ma zakiyi to maisa yanzu dan yace zai auri Layla kike kuka haka”? Dago jajayen idanunta Farrah tayi zatai magana kawai ta tashi tafada kan gado takasa daina kuka, Shafa shiru tayi dan tasan kozata lallasheta bazata lallasun mata ba koba komi yanzu tagane ai tanason mijinta maganinta ai, dudda itama bawai so take Zayn ya auri Laylan ba but idan hakan zaisa Farrah tagane tana mutuwan sonshi so be it.






Kafin kaceme gidansu ya kachame da ma’aikata abinki da masu kudi ana kwashw komi nasu hajiya ana zubawa a trailer hatta spoon nasu Dad bai bari anbar kai agida ba before 7na yamma an gama kwashw komi tas tas trailerr kowanne yatafi gidan iyayenta da kaya, misalin 8 Hajiya Fatima tafara karasowa gaban babban gate na asalin anguwan nasu aka tsayarda ita inspector yakaraso gaban motan nata tareda knocking hakan yasa ta saukar da glass na motan tana mamakin yanda sojoji da yan sanda suka cike anguwan, takardan sakin da Dad yarubuta mata yace “Hajiya my name is Inspector Sani incharge na this case, wannan shine takardan ki daga wajen Alhaji, sannan dagayau bakudawata alaka da gidan nan, u are expected to stay 1000feet away from this estate koyaya kikazo kusadashi we have the right to arrest u” duk maganan nan yanayi ne tana kokarin bude takardan ganin saki 2 daman chan yataba mata daya yasa tabuga wani ihu tace “what is this saki biyu Meya faru? Menama Alhaji dazai sakeni har saki biyu” kai tsaye Inspector yace “you can call him and ask sannan you have 2min to leave this gate ko muyi arresting naki, kayanki kap antafi dasu gidan iyayenki” daidai lokacin motan Hajiya Mariya shima ta iso gaban gate din karasawa yayi itama yabata nata yafadi mata exact abinda yafadi ma Hajiya Fateema wani kalan bari jikin Hajiya Fatima yafara the only thing she could think of is Layla taje ta tonamata asiri, Innalillahi wa innailaihi raji’un tashiga fadi gabanta nafaduwa dasauri tace “Inspector diyata fa? Ta acikin gidan”? Wani mugun kallo yamata yace “Alhaji yariketa kibar gate din nan cikin 2min ko muyi arresting naki” Innalillahi itane Layla zata yaudara tama butulci bayan duka abubuwan datamata aduniya eh, lallai dan adam butulu. “Madam you have less than a minute kibar wajen nan” maganan da police yamata yadawo da ita hayyacinta dasauri taja motarta Hajiya Fatima ma tabita abaya chan gidan dasuke dashi na meeting sukayi suna parking suka shishiga gidan Hajiya Mariya na kiran Uncle ringing daya yadauka kafinma yay magana tace “kasamemu agidan meeting Layla ta tona mana asiri duka Alhaji yasakemu yakiraka”? Uncle dabai gane kan zancenba yace “slow down Mekike cewane I don’t understand you” cikeda ihu Hajiya Mariya tace “nace Layla tafadama yayanka komi ta tona mana asiri Alhaji bai kiraka ba” Uncle da gabanshi yashiga faduwa sosai yace “w…..what!” Katse wayan yayi dasauri yama rasa mezaiyi da sauri yafito yashiga motanshi yaja motan sai zuwa gidan Yayanshi daga gate shima aka tsareshi Inspector yace “har kawayenka sun sanarda kai komi kenan wannan dahar kazo”? Wani kalan kunya Uncle yaji ya lullubeshi inspector is just like a family friend yanzu to them, ganin yakasa magana sai gumi dayakeyi yasa ya girgizakai yace “katafi all I know is Alhaji bai Riga ya yanke any hukunci akanka ba amman dai he’s not ready to see you today” bakin Uncle har rawa yake yace “please kabarni na shiga nai magana da Yaya” girgizamai kai yayi yace “ba hurumina bane wannan ba kawuce katafi” Uncle yakai kusan 2min awajen kafin ahankali yaja motanshi baisan mesaba yadade yana kwadayin kudi da mallakan dukiyoyin Yayanshi but yau da Yayanshi yasan komi jiyayi ya tsani kanshi for the first time, ringing da wayanshi yashigayi yasa yakai wayan kunnenshi da sauri yace “in your life kada kima kara mafarkin ku kirani, dukku kuka zigani ina zaman zamana nai betraying dan uwana dayamin komi na duniya” dasauri Hajiya Mariya tace “Uncle muzaka juyama baya da abu ya baci” akufule tace “last warning” ya katse wayan tareda jefa wayan kan kujera yana goge hawayen daya zubomai da sauri.




7️⃣5️⃣




Saida yaji shigansu daki tareda maida kofan dasukayi suka rufe sannan yasaki Layla dasauri yana mikewa tsaye batare dayama kara kallonta ba yawuce yafita daga dakin tabishi da kallo, dakin Farrah yabida kallo sannan yawuce yasauka kasa, Mami yagani tareda Dad da jikinshi yay sanyi karasawa gabanshi Zayn yayi yadagashi yace “cheer up Papa I don’t want you so dull you know, just forget everything haka rayuwa yayi, kowa tries to take advantage na mutum no matter how good you are to them, saisa kaga rana daya Allah yanuna maka gaskiya, idan kai calming down talk to Uncle” dasauri Dad yakalli Zayn, gyadamai kai Zayn yayi sanan yakalli Mami yace “right Mami”? Gyadamai kai Mami itama tayi tace “yes” ahankali Zayn yace “besides nasan su Matanka ne sukai brainwashing Uncle they’re so evil Dad, so cheer up let’s just move on Dad okay” gyadamai kai Dad yayi yajashi suka fice Zayn nata kanshi da hira shifa Dad idan yaronshi is okay to shima he’s okay.
Sai gab da magrib Farrah tafarka daga baccin daya kwasheta takalli Shafa dake kan dadduma ahankali tasauka kasa kusada Shafa murya chan kasa tace “Shafa” ahankali Shafa dake kallonta tace “naam Farrah” murya chan kasa tace “dagaske Ya Zayn aure zai kara”? Gyadamata kai Shafa tayi tace “to kin kishi sai dukanshi kike kaman wata uwarshi, kwata kwata Farrah yanzu bakida kunya kindawo fitsararriya wanda ni ba ahaka nasanki da ba, kindawo diya mara kawaici da danne Zuciyanta kidubi tsabaragen idon katon namiji ki waskamai mari har kina fasamai kai, ai wlh Allah kara gwara ya auri wacce take sonshi tazo tana kuka wiwi ataimaka a auramata shi kinga ko babu komi ita zata darajja abinta tunda tanaso kekuma bakiso” wani kaya Farrah taji ya tsayamata awuya wasu new hawaye ne suka zubomata dasauri ta mike tawuce bayi tana goge fuskan nata to kodai sonshi take yanzu? Inba hakaba maisa harwani zazzabi zazzabi taji yana neman kamata sabida zai auri Layla what’s happening to her? Alwala tayo tafito tahau kan dadduma tai salla shigowa Shafa tayi tace “Mami tace ki sauko ayi dinner” ahankali ta tashi tabiyo bayan Shafa suka sauko tun kafin takarasa saukowa dagakan stairs taga Zayn zaune a dinning din kusada Layla yana zubamata abinci a plate, Zayn dako kanshi baya zubama abinci yau shine yake zubama Layla abinci, wani abune ya tokaremata wuya hakan yasa ta turje ta tsaya daidai Mami tafito daga kitchen din rikeda flask kallo daya tama Farrah dake kallon Zayn da Layla suna ma juna murmushi sannan ta sauke ijiyan zuciya takai kulan ta ijiye batare daya kalleta ba tace “zokici abinci daughter na” dasauri ta share fuskanta jin Mami takirata takarasa dinning din tazauna ahankali kusada Mami tana kallon Zayn dakaman baimasam akwai wata halitta maisuna Farrah zaune a falonba.




Mami data lura Zayn da Layla kawai yake kallo saisa tabata tausayi wato Zayn ko saida yakoyama Farrah sonshi cikin dan kankanin lokaci shine kuma yanzu wai Layla zai aura sabida kawai akwai dan tension agidan yaune saisa batai magana ba but wlh Zayn bai isa ya wulakanta Farrah agaban idanubta haka ba yay kadan. Plate na abincinta ta turamata agaba tace “eat” Gyadamata kai tayi ahankali sannan tafaraci ko kadan takasa cin abincin ma sai wasadashi datakeyi, wani kalan murmushi Zayn da Layla sukayi atare kome yagayamata oho duk Farrah na kallonsu takasa daina kallonsu barinma Zayn bata taba kwadayin Zayn yakalleta koda sau daya bane sai yau amman ko kallon inda take baiyiba daga Mami har Shafa bakaramin tausayi Farrah tabasu ba tama kasacin abincinta at all tashi tayi Mami tace “ina zaki” ahankali bakinta narawa sosai tace “fi……sari” Gyadamata kai Mami tayi tace “wuce kije” takalli Shafa hakan yasa ta kwashi abincinsu tai sama dashi Zayn yakalli Layla yace “go and get some rest” gyadamai kai tayi babu musu tawuce sama zai tashi Mami tace “Zayn” dasauri yakalleta hakan yasa yasa tace “what do you mean by zaka auri Layla”? Dan yatsine fuska yayi yace “Mami badagake har Yar taki daman bakuson Auren ba, I want to marry wacce kesona hartana kuka for me” wani kalan kallon mamaki Mami kemai kafin anatse tace “kai gani kake harkayi hankalin rike mata biyu? Zayn dududu nawa kake” ahankali yace “I am 26 Mami” cikeda fushi Mami tace “Zayn you must be very stupid for even thinking cewa zakama Farrah that small girl kishiya, poor thing has been suffering tun dazu just look tama kasacin abinci, I don’t even know why you always find your way around women” wani makirin Iskancin murmushi Zayn yayi yace “your son is a pro Mami” baki Mami tasaki bude ganin rashin kunya mikewa tayi zata kaimai duka yatashi da sauri yay waje yana murmushi Mami tanuna kanta tace “ni Zayn kecema he’s a pro” kwafa tayi tace “zan nunamaka ni uwarka I be pro max zanga awani gida zaka kara aure” tai maganan duk ranta abace.


Wasa wasa yau ranan Saturday wanda yaune ranan biki, an gyara gidan anyi kwalliya da flowers, Farrah bata iyacin komi ta rame tai zuru zuru banda maganin da mai maganinta ke bata dasu farfesu babu wani abu datake iyaci, Shafa ta lallasheta harta gaji itama dataga maganan Auren da gaske Zayn yakeyi dan sai shirye shirye ake tadamu itama Mami tadamu gashi dan Iskanci Zayn yama daina zuwa side din nata sabida kada tamai magana.


Wuraren 12 ta tashi zaune dagakan gadon idanunta sun kumbura sunyi luhu luhu, Shafa ta kalla dake kusada ita ahankali tace “karfe nawa Shafa” “shabiyu na rana, 1 za’a daura Auren Ya Zayn da Layla” mikewa Farrah tayi tsaye tasaka slippers dasauri Shafa tace “ina zaki”? Batare data amsa Shafa ba tabude kofa tafita Shafa tabiyota da sauri anan falon sama sukaga anama Layla makeup ko kallonta Farrah batayiba ta sauka kasa Shafa tabita da sauri daidai zata fice daga falon takama hannunta tace “ina zaki Farrah”? Chak Farrah ta tsaya tana rike kukan datakeji kafin ta fizge hannunta tace “wajen mijina zani” sannan tafice tai side din Ya Zayn Shafa ta tsaya tana kallonta bude kofan flat na Ya Zayn tayi kai tsaye ta shige.






7️⃣6️⃣






Wani kalan lumshe idanu tayi data shiga falon bata taba sanin tai kewanshi sosai ba saida taji yanda kamshin turarenshi ya lullube falon, she really miss his scent, falon tabi da kallo babu kowa ciki hakan yasa tai stairs tafara hawa gabanta nafaduwa dan she don’t even know mezata gayamai, batasan mezatacemai ba all she knows is idan yakara mata kishiya she can die dan ko yanzu hakan nan she’s semi dead, wani kalan ciwo heart dinta kemata, karasawa sama tayi tana kallon kofar bedroom nashi data gani adan bude kadan karasawa gaban dakin tayi takai hannunta ahankali ta tura kofan daidai Zayn nafitowa daga closet nashi yaci wata arniyan Shadda fara fat gizna data dauki aiki sai kyalli take yana kokarin saka agogon Rolex a hannunshi, ko kadan bai lurada Farrah ba sai ita data tsaya tana kallonshi idanunta sun cikada hawaye taf yawani kalan kara mata kyau bakinshi harwani kyalli yake lips dinshi sunyi so pink Kaman yashafa musu wani abu, shigowa dakin tayi jikinta har rawa yake she don’t even know what to say babban rigan dake kan gadonshi ta kalla datasan shi zai daura akan jumper jikinshi yafita hannu takai ahankali tadauki rigan taboye abayanta tana kallonshi yanda yajuya mata baya yana kokarin saka agogon batare daya juyoba yakawo hannunshi tabaya sai dauki babban rigan jin wayan yasa yajuyo ahankali ido da ido sukayi da Farrah dake sanye dawani dogon Riga na material ja daya mata wani kalan kyau takara haske takara kyau saidai tarame sosai baisan cewa he missed her this much ba sai yanzu daya daura idanunshi akanta, daurewa yayi yahadiye koma meyakeji yakalli kwayan idanunta dahar kyalli suke sabida yanda suka cikada hawaye sannan yakalli hannayenta data rike babban riganshi dashi taboye abaya tana kallonshi kaman yaune rana na farko daya fara ganinshi.






Hannu yamikamata babu alamun wasa yace “bani babban rigana I am almost late for daurin aure na, give it to me” makemai kafada tayi daidai hawayen na zubowa da kyar bakinta ya iya budewa cikin sheshekan kuka tace “bazan bakaba” wani kalan mugun kallo yamata yace “Farrah you realize I am getting married today to wacce ke sona right” wani abu taji yazo mata wuya runtse idanubta tayi sannan tabude su ahankali takalleshi tace “ai……..ai…..ni….nima ina so…….son…..ka!” Wow Zayn yafadi aranshi he can’t believe abinda kunnuwanshi suka jimishi yau, zai iya rantsewa cewa he’s the happiest man alive today yau amman no baiso taga farin cikinshi ko kadan, cikin fushi yatako zuwa gabanta yace “Madam stop wasting my time kinsan yanzun nan za’a daura aurena da Layla awaje kinzo kina fadamin something that I know is not true, Farrah dana sani bazata tabaso Zayn dan iska ba, nai bin mata da sauran su, Farrah dana sani tafi karfin Zayn, tafi karfin hada jini dashi tafi karfin hada zuri’a dashi, Farrah dana sani only has hate towards Zayn not love, so please save all this thrash as you can see I am super happy and in a very bright mood today I am getting married to wacce ke sona and she’s ready to do anything for Zayn’s happiness, I don’t have room for negativity please get out” yay maganan yanakai hannunshi yana fizge babban riganshi tabayanta ya warware rigan tareda sakawa yana murmushi sannan tazura takalmi tareda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login