Showing 90001 words to 93000 words out of 103785 words
ba ta ba? Mu'azzamu kada ka bari mu haɗu domin haɗuwarmu ba za ta yi mana kyau ni da kai ba." Daga haka ya katse wayar ya bar shi sagale da ita a kunne kafin shima ya sauke yana faɗin"Ikon Allah!
Ajiyar zuciya ya sauke kawai ya Cigaba da cin abincinsa Hibba ba ta yi mgana ba tana fama da Junoir ne ma a lokacin to ita ai ba ta isa ba wannan faɗan tsakanin Yaya da ƙaninsane, sai dai in bai yi masa wani abun da ya baɓa masa rai ba haka zai kirashi ya yi mishi faɗa ko Inna da Baba albarka.
Har mamakin masifar Yaya Mansoor take yi, shi abu kaɗan a wajensa na faɗa ne. Tana ta nazarin mijin nata ya na cin abinci yana mirmishi shi kaɗai, cikin mirmishin itama Ta ce.
"Me ya faru ne.? Na ga kana ta mirmishi kai kaɗai"
Kai ya kaɗa kafin ya ce"Ina son yayana, na tabbata duk duniya ba wanda zai kai sa kaunata wani abu na tuna kawai da ya sa naji zuciyata ta yi sanyi. Fata na nima wata rana na saka shi farinciki kamar yadda yake sakani." Ba ta matsa sai ta ji me ya tuna ba ta amsa da Amin Amin, sai da ya gama cin abincin sa sannan ya kira Inna bayan ta ɗauka sun gaisa ya faɗa mata yadda suka yi da yayan na shi cikin yar dariya Inna Meri ta ce"Kyale shi ɗan inna faɗan da ba zai iya yi min ba ne ya sauke maka, rabu da shi kada ya saurara ma kansa ya je bakar zuciyarsa ta hana shi zama lafiya da kowa."
Sun ji ma suna ta mgana da Inna, tana bashi labarin yadda Hajiya ta yi ta murna da ganinta amman ba ta faɗa masa mganar Mimin da Hajiya ta yi mata ba, amman ta faɗa masa Hajiya ta ba ta labarin Major ya so ya zo ya nemi gafaran Baban Inna kan lamarin da ya faru a baya sai dai Allah bai yi ba lokaci ya ƙare. Mu'azzam ya ce"Mu ai ba mu da matsala Inna, tuni mun yafe abunda ya faru matsalan daga Yaya Mansoor ne shi fa kamar ba ya iya yafiya ga wanda ya ɓata masa Inna."
Inna Meri tace"Allah shi ya ye masa wannan cutar, domin cuta ne ta bala'i da ya kamata a nema masa tsari wajen Ubangiji."
Mu'azzam sai da ya yi dariya jin abunda Inna ta ce itama sai ta biye mishi suna dariya ƙarshenta dai kafin su yi sallama sai da ya ba ma Hibba wayar suka gaisa da Inna Meri ta na tambayan Megidan ta Hibba ta ce ga shi a jikinta ya yi barci sannan suka yi ma juna sallama.
Yaya Amina washegari da ta zo gidan ta ji abin da ya faru ta yi ta dariyan Bintu da ta gudu cikin dariyan ta ce"Bintu ga tsoro ga ban tsoro."
Inna Meri ta ce"Ina za ta tsaya jiya nan ya warwareta, ɗan inna dai aka kira jiya aka yi ma borin." Walida ta ce"Inna ke ma fa jiya kin yi ma Yayanmu tsawa."
Inna Meri ta ce"Da ban yi mishi haka ba, da ba zai bar mganar ba, ni kaɗai nasan fitinar za ta faru ƙarkashin wannan maganar."
Yaya Amina ta ce"Gaskiya tunda shi dai ba zai gane abunda aka yi ba, Allah Sarki ashe ba ta manta damu ba."
Walida tace"Wlh ta ce duk a gaishe ku."
Yaya Amina ta ce"Mu na amsawa da Inna ta min mgana ai da tare za mu je."
Walida na riƙe dariyanta ta ce"To yanzu ma ba ta ɓaci ba, in za ki je ne ai gidan ba ɓoyayye ba ne."
Ita Kuma Yaya Amina sai ta ce sai dai in Walida za ta raka ta ita kuma ta ce ba da ita ba ya zo Baban Inna ya ji labari ya yi biji biji da ita. Inna na gefe ta na yi musu dariya kafin ta ce"Sai dai ya yi muku amman ni ai na kuna ba na tashin ƙauri ba yadda za'a yi dani sai hakuri."
Yaya Amina ta ce"Inna ke sha kumdun ne, ni kuwa sai ki sa ya kulla dani mu na yar mutumci da ɗan ƙanina,Halima har mamaki take yi in taga muna hira na kan ce ma ta tun tuni daman tamu ta zo ɗaya da Baban Inna" knna Meri na sakacen hakorinta ta ce"Ke ku rabani da halin Baban Inna, zuciyarsa har wani zaɓan wanda za ta yi mu'amala take yi, Allah dai ya ye mishi wannan cutar." Walida na kwasan dariya ta ce "Inna ba shi da lafiya ne?
Kai tsaye ta ce"Eh mana ai ciwo ne babba ma kuwa, ku yi ta masa addu'an Allah ya ye masa." Suna ta dariya Inna Meri na faɗin su daina dariya ba abun dariya ba ne.
Yaya Amina na gidan har bayan la'asar sai da su ka yi sallar sannan Amina ta ce Walida ta raka ta su je gidan Bintu.
Walida ta ce ita makaranta za ta je Yaya Amina ta ce to su je in ta rakata sai ta wuce makaranta daga nan.
Inna Meri na zaune ta na jan casbaha tace"Ku gaishemin da Bintu, ku ce mata nan fa ba gidan Baba Inna ba ne ta kwantar da hankalinta ya yi mana ma yaji."
Dariya ta kara ka ma su Walida su ka fita suna yi Inna na gimtse fuska,.Da ya ke yau Yaya Amina ita kaɗai tazo yara duk suna makaranta har sun fita Inna ta kira su, bayan sun dawo ta kalli Amina tana fadin"Amina ki shiga bangaren su Gaje ki gaishe su, sannan ki shiga ɗakin Magajiya itama ki gaisheta ba ta jin daɗi."
Yaya Amina ta amsa da toh Inna sannan su ka fita ɗakin Magajiyan su ka fara shiga ta na kwance Jummai ta zo gidan ashe tana ganin Amina ta washe mata baki su ka gaisa
Aminan ta gaida Magajiya ta amsa mata fuska ba fara'a Walida ma duk da ta shigo da Safe sai da ta kara yi mata ya jiki ta amsa ta na wani haɗe rai ita dai Magajiya ba ta san zaman lafiya ciwo ya rafketa Mariya na gidan Zuwaira ba ta dawo ba Inna Meri ke yin abinci yanzu ta ke ba ta kuma safe da rana da yamma Inna Meri za ta shiga ta duba ta amman ko da rana ɗaya ba ta taɓa gode mata ba. ita dai Inna Meri komai take yi domin Allah ne.
Hiran da Walida da Yaya Amina suka riƙa yi kenan a kan hanyarsu ta zuwa gidan Bintu, da suka shiga shashen su Gaje ma har ana faɗa musu mgana kiri kiri Gaje ta ce ma Amina ba'a ganinsu ko sun zo suna ɗakin uwarsu Meri to ka da su manta suma ɗaya suke da Meri a wajen su.
Walida ko ta bata rai a ranta ta ce ba ɗaya ba ne, Amina kuma sai ta ba ta hakuri Harira ce ma yar ba ruwanta ba kamar Gaje da kamar halinsu ya zo ɗaya da mijinta wajen kallon rayuwar wani.
Sun je sun iske Bintu ita kaɗai a gida su Hassan sun bi babansu gidansu, abokiyar zamanta ba ta nan suna biki a gidanu, ta yi murna da ta gansu sai ga shi ta kawo musu ruwa da zoɓo daman ta na saida wa.
Ta zauna kusa da Yaya Amina tana faɗin"ki ce yau a gida kika yini"
Yaya Amina na shan ruwa ba ta amsa ta ba, sai Walida ne ta ce"E, ke ai kin gudu jiya."
Bintu ta ce"Uhm na yi gudun gara ne Walida yau da safe Baban inna ya kirani a waya ya zazzageni Walida."
Walida ta zaro ido Yaya Amina kaɗan ta ƙware da ruwa ta ɗago tana faɗin"Kai! me ya ce miki kuma?
Bintu ta yi tagumi kafin ta ce"Kawai da safe muna cikin karyawa da Bashir sai ga kiransa ni fa tunda na ga kiran Baban Inna nasan ba na alheri ba ne na tashi na yi ciki ina ɗaukan waya ko gaisuwata bai amsa ba ya fara min masifa wai mu munafukai ne ni da Walida me ya sa da Inna ta ce ga inda za mu rakata ba mu kirasa a waya a ɓoye mun faɗa masa ba? da ina masa rantsuwan ni ma ban san inda za mu je ba ya dakamin tsawa yana faɗin duk sai yaci ubanmu me ya sa da ta ce mu rakata ba mu ce ba za mu je ba? Kuma sannan mun yi masa ƙarya da ya kira mu ka ƙi gaya masa in da mu ka je, yace wlh wannan ƙaryan da munafuncin da mu ka yi masa sai mun raina kanmu."
Walida ta yi fiki fiki da ido ta kasa mgana Yaya Amina ta ce"To ke ba ki ba sa hakuri ba ne?. Bintu ta ce" Wani hakurin? Ya tsaya ne ma ina cikin mgana ya yi tsaki ya kashe wayarsa walh Baban Inna ya cika masifa"
Yaya Amina ta ce"To ai jiya ma yazo zai yi ma Inna ta balbaleshi da masifa shi ne ya koma gida ya kira Mu'azzam ya sauke a kan shi."
Bintu ta ce"Kai jqma'a shi ya yi hakuri da rayuwa mana, ni fa ban ga wani abu acikin zuwa gaisuwan da muka yi ba"
Walida ta ce"To ni ma dai shi nagani."
Yaya Amina ta ce"To shi gani zai yi ba kwa kishinsa ban da abunsa da mai rai ake fushi ba da wanda ya mutu ba."
Nan su ka cigaba da tattaunawa Walida ta shantake ba ta je islamiyan ba Bintu na ba ma Amina labarin yadda Hajiya da Mimi da su ka yi ta rawan jiki da su ka gan su.
Yaya Amina ta ce"Allah Sarki Itama kila har yanzu ta na son shi."
Bintu tace"To daman mana, shi ma duk wannan kumfar bakin na Soyayar ne."
Gabaɗaya suka saka dariya ba su suka baro gidan ba sai shidda saura na yamma.
Suna komawa gida Inna ta ga Walida ta dawo da wuri cikin faɗa ta ce" Amman dai ba ki je makarantan ba ko?
Walida ta sosa kai ba ta yi magana ba Inna tace "Ya yi miki kyau."
Yaya Amina ke labartama Inna yadda Baban Inna su ka yi da Bintu sai da Inna ta yi dariya amman ba ta ce komai ba acikin ranta tana son ganin yadda lamarin zai kasance. Shi dai kahaifin Mimi da ya fara ja Ubangiji ya karɓi kayanshi sauran Baban Inna shi kuma sai ta tsaya ta ga ina wannan bakar zuciyar za ta kaisa.
Kamar Inna ta sani yaji ya yi musu sai da ya kusan kwana goma sannan ya zo gidan Sun dai ji kabarin ya na kaduna sun je buga wasa daga bakin Mu'azzam shi tuni har sun shirya kansu. Sai da ya dawo ya zo gidan shima bai daɗe ba, Walida daman tana nemansa nan ta gaya masa an fara biyan Jamb ta na so ta biya nan ta ke ya ba ta kuɗin har da na abun hawa ya ce kuma in akwai wata matsalar ta kirashi ta wayar Inna ta gaya masa.
Duk kuma wannan abun bai zauna ba ya na tsaye a kofar ɗakin Inna Meri.
Ita ko ta yi masa banza kamar ba ta gansa ba, har ya tafi kuma sai ya dawo ya kira Walida yana tambayanta ina Mariya? Ita ba za ta yi jamb ɗin ba ne? Domin suna aji daya ne SS3 Kuma tare aka biya musu kuɗin jarabawar fita.
Sai take faɗa masa Mariya ta daɗe ba ta nan ta na gidan Yaya Zuwaira, Inna ya kalla kafin yavce"Inna me ta je yi can kuma?
Inna na tankaɗen garin tuwo ta juyar da kai kafin Ta ce"Ina zan sani, shiga ɗakin Magajiya sai ta faɗa maka"
Cikin Kallonta ya ce" Innarmu."
Ko kara kallonsa ba ta yi ba sai kawai ya kaɗa kai ya fice bai kara magana ba ta bishi da kallon tausayi a ranta ta na masa fatan Allah ya yaye masa wannan bakar zuciyar.
Da daddare Mu'azzam ya kira wayarta yana faɗa mata Babanta ya kawo masa ƙaranta.
Tana mirmishi ta ce"Me kuma na yi ɗan Inna? Ckin dariyan shima ya ce" Ya ce ya zo kin yi kamar baki gan shi ba ,yana mgana kika yi banza da shi sannan ko abinci bavki ba shi ba." Inna Meri ta ce"Ban ba shi ba sai ya zo ya ƙwata, ko auransa na ke yi da zai zo ya tsaya a saman kaina yana min wani cin magani? Ɗan Inna rabani da Baban Inna ba na iyawa da fitinarsa."
Cikin magiya ya ce"Haba Innarmu maganin kukan mu, a yi masa afuwa in kina fushi da shi ina zai saka kansa Inna?
Ya faɗa cikin wani yanayi sai ta ji tausayin duka ya'yan nata ya kamata amman ba ta huce ba cikin gatse ta ce"To shi ba shi da bakin da zai zo ya ce in yi hakurin ne?
Mu'azzam sai da ya yi dariya kafin ya ce"Allah ya huci zuciyarki Inna"
Ta amsa mai da Amin bayan sun yi sallama ba jimawa Baba Ɗanjuma ya shigo.
Shima sai da ya yi mata mganar cikin Lallashi ya ce"Meri fushi da Baban Inna ba naki ba ne a wannan lokacin, ki yi hakuri ki fahimce sa don Allah."
Inna ta gyara zama kafin ta ce"Au kai ma ƙaran nawa ya kawo maka?
Kai tsaye ya ce"Ko ɗaya ni na fahimci yau ya na cikin bacin rai ya shigo gida ya fito ban gansa cikin yanayi mai daɗi ba, ki yi hakuri tunda har mu fahimcesa sai mu yi ma rayuwarsa uzuri kin ji ko?
Ba za ta iya yi ma mallam gaddama ba sai ta amsa masa. Shi ya sa bayan kwana biyu da ya zo Innar ta sakar masa amman ba sosai ba da kanta ta kawo masa abinci ya zauna yaci sosai tausayinshi ya kama inna har sai da ta ji taruwan kwalla acikin kwarmin Idanuwanta. Bai yi wani doguwar mgana ba da zai ta fi ya ijiye mata kuɗi yana faɗin "ki yi hakuri Inna."
Daga haka bai kara cewa komai ba sai ta ɗauki kuɗin tana saka albarka kafin ta ce"Ka leka ka duba Magajiya ba ta ji daɗi ba kwana biyu."
Sai ya amsa mata da to, yana fita sai ya ganta nan kofar ɗakinta kamar ta fito daga makewayi ne. Mariya na cikin ɗaki ta dawo shekaranjiya ta na jin muryansa yana faɗin" Magajiya ya jiki?
Dakyar ta amsa shi kuma cikin yanayinsa ya ce"Allah ya kara lafiya"
Bai ji ta amsa ba Mariya ce ta leko tana gaishe shi ya amsa yana kallonta har ya wuce sai ya sake dawowa yan faɗin"Ke me ya sa kika tafi wani waje kika bar zuwa makaranta? Kafin ta yi mgana Magajiya ta yi zaraf ta ce"Ba wani waje ta je ba gidan ƴar'uwanta ne ko za ka hana ta ne? Ko bangaran magajiya bai kalla ba ya cigaba da faɗin "Walida ta biya Jamb ke me ya sa ba za ki yi ba?
Da sauri ta ce"Ina son na yi Yayanmu Baba ne ya ce ba shi da kuɗi Yaya Auwalu ma na yi masa mgana ya ce ba shi da kudi."
Hararanta ya yi kafin ya ce"Daman su suka saba ɗawaniyar makarantar ki? biyo ni ki karbi saƙo a waje." Ya wuce cikin takunsa na gif gif Magajiya sai ta kasa mgana saboda ya lna mata ƙwarjini wani lokaci.
Jiki na rawa mariya ta zari hijabin Magajiya da ke saman kofa ta bi bayanshi da mota ya zo sai da ya shiga ciki ya ɗauko kuɗi ya bata na farko ya ce ta biya Jamb ta yi ma Walida magana ta rakata. Ta karɓa da sauri tana godiya sai ya mika mata wani kuɗin yana faɗin"Ki kaiwa Magajiya."
Har sai da ta ramkwafa wajen amsa masa acikin zuciyarta ta na jin wani iri, gida ya ce ta shiga sai ta shige ta laɓe sai da ta ga shigarsa mota da tafiyarsa sannan ta koma tana dafe kirji ita fa tun ba ta gane ba har ta zo ta gane cewa tun tuni ashe son Yaya Mansoor take yi ba ta sani ba.
Jiki na rawa ta je ta na nuna ma Magajiya kuɗin ta ba ta nata tana faɗin "Ya ce in ba ki" Magajiya ta taɓe baki ba ta ko karɓi kuɗin ba ta shige cikin ɗakinta lokaci ɗaya tana faɗin" Shi ne kike ta wani rawan jiki kamar ya ba ki wata duniya"
Kuma acikin ranta ta ji daɗi bashi ake bin ta ko ta samu ta biya daman in ba shi ko Mu'azzamu ba ina take samun kuɗi? Sai dai fa taƙi godema Allah.
*Shafukan kyauta sun gabda ƙarewa. Ku yi hanzarin biyan kuɗin karatun ku domin kar mu ɓata lokaci da zaran mun gama book1, mu ɗora da book 2and3 in sha Allahu*
*BOOK 1 FREE NE, 2,3 PAID NE REGULAR N500, VIP 1K NE, KU BIYA KUƊIN KARATUN KU TA WANNAN ASUSUN BANKIN 0552179550 JAMILA UMAR GT BANK, SANNAN SAI KU TURA SHAIDAR BIYA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.*
*09069067488*
*80032773332*
*Ƴan kasuwa masu bukatar a tallata musu hajojinsu cikin farashi mai sauƙi, ku yi min magana ta wannan lambar*
*09069067488*
*NA GODE.*
*Janafty*
*IDAN AN CIZA..!*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Arewabooks:Jamilaumarjanafty*
*Mallakar:Janafty*
*SADAUKARWA GA HAJIYA AISHA AHMAD IYA*
*BONANZA*
Kana naka 500.
Ta fita zakka 500.
Gidanmu 300
Sadaukarwar so 200
Malika malik 200.
Zaman gidanmu 200
Ra'ayi ne ko buri? 300.
Tsaka mai wuya 500
Mr bello 200.
Sillar Hallaci 200.
Saifudden 500.
Zainazain 300.
*Bonanza za ta ƙare a gobe in sha Allahu, in ba ki karanta ba, wannan wata dama ce*
Ina kuke mata yan kwalisa.. *KHADYS EMPIRE* Ta Kawo muku kayan mata masu kyau da saukin kudi💃🏻 kamar haka.
*Zumar Matsi Guarantee 3500*
*Maganin sanyi komai nacinsa 4k*
*Zumar kacha kacha 2500*
*Zumar kiba 4k*
*Setinn kayan mata na yar gata 8500 Me abubuwa har kala Takwas a ciki*
*Dahuwar kaza ta manyan mata 8k*
Zaku sameta a Kan Lambar waya 08147832783 tana garin kano tana aikawa da kayanta ko ina da yardar Allah. Dadin dadawa kuma tana bada sarin komai cikin farashi me rahusa yadda zaki sami Alheri. Wani ƙarin jin daɗin ma free delivery withn kano take yi, koh ba yanzu zaku siya ba kuyi saving numbern ta dan nan na gaba Na gode. https://wa.link/pd4ie0
*Page 19*
*Bayan Wata Ɗaya*
Bayan wata ɗaya da ya yi dai