Showing 48001 words to 51000 words out of 198792 words

Chapter 17 - ZEE-BABY-1-AND-2 COMPLETE HAUSA NOVEL By hausanovels001.txt

27 Nov 2024

9775

gode da kaunarki gareni inason Dr nah banason abinda zai rabamu "wlh babu abinda zai rabaku insha Allah shima fa saurayine baisan komai ba wayar mashakurah ta dauki ringing ganin Dr ne yasa ta dauka da Sauri tana goge fuskarta"hello my Dr "sweet baby nazo ya fada yana tsinke kiran kallon Laila tayi "kawata mijina yazo bari na ganshi ni nace yazo inason ganinsa wlh yau data muguwar sha'awa nakeji duk ba halina bane amma tunda nadawo nakejin sha'awa fiye da tunaninki Dole zani gun Dr na rabu da jikinsa ko zanji sauki "to kibi asannu fah? " to zan kiyaye tare suka fito tama hajiya sallama suka fito harabar gida dama amota tazo ta shige motarta ta tafi get ta bude yana cikin mota azaune ta bude ta shigo

"aslm my Dr ",wslm amaryata wow kinyi kyau amma na hanaki fitowa haka Ana kallemun ke"yi hakuri mai gidana "to gani nace kibari ayi sallah nazo zance kince kedai yanzu sweet baby kin cika rigima idanu ta zuba masa yadan yayi kyau iskar bakinsa ya hura mata saman idanunta ta Saki dan ihu "wayyo My Dr idona ta fada samansa ta Saki kuka rikota yayi yana kokarin jinyeta ta Kara shiga jikinsa ta rumgumesa tana kuka " oh my God my sweet menene ah idanunki mugani kanta ya tallabo a kirjinsa ya bude idanu yana dubawa yana bushemata "wayyo Dr ka Kara mun zafi wlh abun katone sai yawo yakemun a idanu " to tsaya baby bari kukan na duba miki harshansa yasa a idanu yana lalubawa wani irin dadi taji ta kara rumgumesa ta tura hannuta cikin sumar kansa tana shafawa "my Dr inajin zafi ya gaji da lalube baiji komaiba ya cire bakinsa "my sweet babu komai fah ko kinyi tsuna ne shiru tayi ta kara shigewa jikinsa tana sabke ajiyar zuciya kallonta yaga sai lumshewa takeyi tana mimmik'ewa idanu yazaro dan ya tabatar ya dora, hannusa sama kirjinta kamar zai gyara mata kwanciya jikinsa sai yaji wani Abu mai tauri shahada yayi ya zura hannusa cikin rigarta wata uwar brezia ce mai ciko abin kamar katuwar albasa idanu ya zaro ya janye breziyar ya shafo breast dinta lakwai yaji ba girma kuma ya saki itako ajinta matsa mata zaiyi ta kara shigewa jikinsa tana nishi har wata zufa take keto masa ya janyeta ya zaunar da ita kan kujera idanunta sunyi jajir sai lumshewa takeyi"baby yau kuma jaraba kikeji daga hawa samana ya fada yana gyara mata gashinta to wlh ki farka ni ba dan iskan namiji bane maza ki hadiye jarabarki har ki ISO gidana wlh daga yau ko kusana kika matsu sai na bata miki rai zan baki mamaki zan Nuna miki waye Dr Sardauna kuma karki kuskura ki sake saka wannan shegiyar abar Ashe duk tulin banzane ba jikinki bane abun naki yan yarane kuma sun fara saki ya fada cikin tsawa nutsuwarta ta dawo cike da tsoronsa da nadamar abun da tayi " Dr yi hakuri bazan sake sawaba"kima sa idan kinaso kuka ta fara tana bashi hakuri"baby kinci sa'a ina sonki wlh da fasa auranki zanyi da fatan cikakiyar mace. kike dan wallahi idan kinsan da Martsala tun wuri kima kanki nema tsari da hada inuwa da Sardauna yada naga nonoki na tsorata da lamarin mace" wlh babu abunda na sani My Dr"ok naji bari kukan shiga gida zamuyi waya zuwa dare kiss ya mata agoshi motar ta bude ta fice jikinta yayi sanyi kai ya kada ya fizgi motar ya harbata kan titi yana sharara uban gudu ransa amugun bace sai tsaki yakeja ya kunna sigari yana zuga baki da hanci yake fitar da haki ya murza kan motar cikin kwarewa "baby badan ina Dan sonki ba da banason tozarta Dan Adam wlh da na fasa auran mace breast yawa dumniya tsaki yaja yaci gaba da fesa gudu har ya isu gida a bakin get suka hadu da motar Mahabeer sun fito shikuma zai shiga shigewa yayi sukuma sun tafi Nisha da zee baby tana gaban mota kusan Mahabeer

gudu yake sosai saboda magarib ta kusa " my heart ai karika zauwa muna hira ko? " sosai ma my zee ba wani dadewa zakiyiba ranar monday zaki dawo dariya Nisha tayi"kai brother kabari tamana wata mana "wlh bazan bariba "my heart karabu da my dear nima bazan yadaba "kunga kunsani zanyi sallah acikin gari daide lokacin suka ISO kofar gidansu Nisha dake goruba road akofar gida yayi Parking Nisha ta fito zee ta kalli mahabeer "my heart ka dawo da dare "muje ai ina nan sai nayi sallah dariya tayi ta bude motar suka shigo cikin lokacin Nisha har ta shige parlo da sallama suka shigo parlon hayatu na tsaye yayan Nisha yace " oyoyo matata tazo har gida ya fada yana ma zee baby wani Mayan kallo saboda Riga da siket din atamfane sun kamata kirjinan nata masha Allah dam sai Dan guntun gyale Wanda daket ta yafoshi saida Mahabeer yace wlh zai kurawo Sardauna awaya yazo zata fita ba gyale tunkun ta dauko cikin rawar jiki ta yafa suka taho face mahabeer ya hade" yaro nemi matarka tun wuri dariya yayi ya nufo gun zee wani Dan iskan kallo tamasa ta dauke kanta Aunty hauwa ta amsa"lallai yau munada baki su uwatace hassan ya tari zee ya riko hannuta suka zauna kusan hauwa mahabeer ya gaisheta"ango bakada dama dariya yayi ya Sosa kansa hassan yace"umma ni zan masa kwace ga yaro me zatayi da tsoho "ai gatanan yaro idan zaka iya kwacewa mik'ewa yayi jin Ana kiran sallah "umma natafi masallaci daga can na wuce gida "to ka gaishe da su ghaisha mik'ewa zee tayi ta bishi har kofar get ya shiga mota ta shagwab'e "my heart kadawo "to shiga ciki bari naje nasamu sallah daket ya lallabata ta shiga gida akofa ta hadu da hayatu kanta ta dauke Dan taga bashida kunya kallon kurilla gareshi ta shige tana wata irin shegiyar tafiya kirjinta da hips dinta kawai ya zubama idanu Mahabeer ko yaja motar ya nufi masallaci Dr Sardauna na shiga cikin da mota parking space ya nufa yayi parking ya fito part dinsu yana tafiya cike da jarumta da karfi karfi yake takunsa wayarsa ta dauki ruri amma bai dagaba jin ansake kira yasa ya cirota aljihu ya kalli screen d'in wayar yaga yayansa nuhu ne picking yayi ya Kara akunnesa "babban yayamu barka da dare" Dr Sardauna please kazo yanzu? " OK har ayi sallah ko?? " No Mara lafiyace kazo yanzu ka dubata kayi sallahr anan jin yanayin maganar yayan NASA yasa ya amsa badan ransa yaso ba ya kalli wandon jikinsa 3quarter ne baki ya tab'e ya juya ya nufi gun motarsa ya shiga ya fizgeta da karfi ya nufo get Daddy da shigowarsa kenan ya bishi da kallo yana dariya wai ko wa ya tabo masa Dr oho mai gadi ya bude masa get a guje ya fizgi motar ya fice daga gidan ransa duk ab'ace................. ✍🏻





Yar ilu ce🤪


*💖💖👩🏻‍🦱ZEE BABY👩🏻‍🦱💖💖*



*DAN ALLAH KARKU FITARMUN DA BOOK WAJE*


*👉🏻18*


....gudu yayi sosai bai jimaba sai gashi kofar gidan Nuhu honr yayi aka bude masa get ya shige nan kusa da get yayi parking ya fito gun mai gadi yaje yayi Alwalla sai ga Nuhu zashi masallaci "Dr ka ISO rumgimeshi yayi "babban yaya waye ba lfy wai?? "Muje masallaci mu fito suna rike da hannu juna suka tafi masallaci, can ciki ko a parlo kwance take saman kujera maryama na mata sannu ta kalli hafeeza "ya akayi kinsan bata lfy kukazo tare? " Aunty maryam wlh lfy lau muka fito khalisat ko dama bakida lafiya ne baki nunama dan karmubar ki ke daya? "wlh lfy ta lau yanzune ana maryama tace"ya kikeji yanzu?"da sauki Aunty ta fada tana lumshe idanu sallah su hafeeza suka tafi suyi sai ita da yara meerah na mata surutu ita da mai sunan Daddy Sharifa ta Mike "aunty na tafi nayi sallah kar Allah ya kamani dariya ta kama khalisat ta cije "jeki kiyi kam gaskiya da sallama suka shigo da sauri ta rufe idanunta tana fitar da numfashi da sauri sauri meerah ta tafi gun Dr Sardauna da gudu daukarta yayi yana mata kiss" meerah uwar rigima ina sharifa" tana sallah "brother itako wannan me yakawota har rashin lfy ya kamata"yanzu dai dubata ita da hafeeza sukazo weekend ne baki ya tab'e

ya matsa kusanta "ke tashi fadi inda yake miki ciwo da sauri ta tashi zaune tana matse baki kuma karya ce take lfy ta lau " cikina ne yake ciwo Nuhu yace "d'azu har suma tayi " ya kikeji?? " murdawa yakeyi meerah ya ajiye ya kalli Nuhu "bro muje na baka magani ni bazan dawoba murmushi yayi" hakanma mun gode maryam ce da hafeeza suka fito" Aunty barka da dare" ango ni amarya rowanta akemun tunda ta amshemun kai ko"hmm Aunty kibari kawai zan kawota ya harari hafeeza "ke dan ubanki yawo da, mara lfy idanu ta fara zarowa ta koma bayan maryam ta lab'e Nuhu yace" muje kabani maganin sallama ya ma maryama suka fito khalisat tabishi da idanu kamar ta lasheshi taji dadin magana dashi taso ya tarairayeta ya kaita hospital yada taga, yanama zee baby maryam tace"daure kiyi sallah hafeeza ta kamata suka shiga tayi sallah Dr suna fita kowa motarsa ya shiga hospital suka tafi yaba Nuhu maganin da ya dace ya nufi gida yau ransa ab'ace yake, zee bay bayan sunyi sallah isha zaune suke a parlo anata hira sai surutu zee take zuba musu anashan dariya Nisha cikinta har kullewa yayi da ta basu labarin tsiyar da tawa Abbu Rahaman kakanta lokacin da yazo yanacin fuskar ummi Raiyan hauwa tace"momy dan Allah kibar maganar dariyar ta ishemu Abban su Nisha ne ya shigo da sallama "ah yau mamarmuce agidan dariya tayi"Abba sannu

"Yauwa hajiya dariya tasake hauwa ta Mike ta amshi ledar hannusa tana masa sannu suka nufi bedroom hayatu ya kalli zee baby"kanwata wlh mahabeer yamun shigar sauri Nisha tace"wai yaya meyasa kake hakane"ke zan ci ubanki mace dan namiji daya akayita cikin tsiwa zee baby tace" wlh dan my heart akayini hayata kake kowa wlh kar mufara yar rashin mutumci dakai nafika iyawa ta fada tana mik'ewa ta nufi bedroom Nisha ta bita acan sukaci gaba da hirasu har hussaina yazo kiransu cin abuncin dare, ko akan dining sai harara hayatu takeyi saboda irin kallon da yake mata ana gamawa ta Mike bata tsaya hiraba, kiran mahabeer tayi suke hirasu, Dr Sardauna yana zuwa gida wanka yayi yayi sallah isha ya nufi part d'insu ghaisha duk suna zaune a parlo har mahabeer da sallama ya shigo kusan ghaisha yaje ya dora kansa cinyarta ya rufo idanunsa kansa ta shafa"Dr lfy kuwa fuska ya yamutsa ya shagwab'e mata Daddy yace"Dr wa ya taboka ne"Daddy babu kowa kawai dai banajin dadin jikina ne dariya mahabeer yayi "Dr namu fadi gaskiya banza yamasa ghaisha tace"tashi muje kaci abunci nawwara tace"yayamu sai karika Abu irin na yara idanunsa ya bude ya watsa mata mugun kallo da gudu tabar gurin ta nufi Daddy jikinta yana tsuma Aunty amarya tace"Dr karka firgitamun diya ghaisha ta kamashi ya Mike suka nufi dining sai dariya suke musu dan idan tana tatalinsa ko nawwara auta bata samun haka

serving dinsa tayi ta zauna itace take bashi abaki sai yamutsa fuska yakeyi dan sam yau bayajin dadin zuciyarsa daket ta lallabashi ya dan ci farfesun nama rago kadan dan dama tasan halinsa bayacin abunci da dare mai yauni zaide ci nama kadan yasha frut kadan sai coffee kallonsa tayi cikin sigar lallashi"autana waye ya tabamun kai shagwab'e mata yayi"ghaisha ni auran ne ya fita araina Allah da sauri ta rufe masa baki "haba bokan turai Namijin duniya karkasa azagi mahaifinku mana a garin Katsina meye tamaka yarinya mai hankali dan Allah kayi hakuri mata sai ana hakuri dasu haka tayi ta lallabashi da maganganu masu dadi akan cewa karma yakuma tasa maganar ta janyosa suka dawo parlo lokacin mahabeer na hira da zee baby Dr ya musu sallama ya nufi part d'insu yana shiga yayi zamansa a parlo yana kallon TV yana busa sigari sweet baby ce ta kirasa tsaki yaja saida ta kira sau ukku ya daga cikin masifa ya fara magana"wai uban me zaki bani da wannan daran kibarni zan nemeki haba dan Allah kitt ya tsinke Kiran yaci gaba da kallonsa yanajan tsaki haka mahabeer ya iskoshi yana masa hira sama sama yake amsawa dan yau haushin kowa yakeji neman inda zai huce haushinsa yake, mashakurah tunda ya mata tsawa tayi kwance tana kuka sai kiran sunansa take tana Kiran sunan wani mutum sai tsine masa, albarka take tana masa Allah ya isa duk tafice haiyacinta

su zee suna uwar daka akwance sai hirasu suke ita da Nisha suna dariya har karfe kusan daya na dare bacci ya dauki Nisha zee baby sai juyi takeyi tana lumshe idanu da ta tuno yada ta riko k'ugun Dr Sardauna da yada yasata cikin jikinsa yana mata masifa da kuma da rana yada ya tsotsi bakinta da yada yake murza mata breast yana mata magana cikin zazakar muryasa komai NASA cikin kwarewa ahankali ta furta"Dr Sardauna Jarumin maza ta fada tana lasar baki ta fara matsar kafafunta tana mimmik'ewa har bacci ya dauketa cike da mafarkin Sardauna suna wata irin rayuwa mai dadi, Dr Sardauna kwance yake saman makeken gadonsa sai juyi yake yanajan tsaki yana rike da cikinsa yana cizon lips d'insa na k'asa har karfe biyun dare Dole ya Mike ya sabko daga kan bed d'in yana tangadi ya nemo magani yasha sai zufa take keto masa ta ko ina ya rarafa ya kwanta daket bacci ya sa cesa, Asubah ta gari,

*********************************

*bayan kwana ukku*

tunda zee baby ta dawo gidansu Nisha rayuwarta take hankali kwance babu takura sai hayatu da ya tisata GABA duk inda tayi idanunsa na kanta ko ya rika neman zama kusanta ko yace zai tabata ko kusa bata yada akwai ranar da ta wankeshi da mari tana kitchen tana soya kwai taji ya rikota tana juyowa ta sharara masa mari ta tofa masa yawu tayi masa, kwakwaran kashedi tun ranar bai sake ko kallonta ba sai aboye ita da Nisha yawo suke fita sune gidan zainab gidan kawu saminu gidan Ibrahim yayansu Nisha gidan Nuhu gidan maijidah yayar Dr Sardauna wacce yakebi idan kagansu kamar tagwaye gidan Nuhu suje su hadu da su hafeeza suna iya shege maryama tayi ta musu dariya dan ita batada matsala agidan zainab ne zee baby suka hadu da wata makwabciyar su zainab yan matace mai sunan habiba kallo daya zee ta mata tasan tana shaye shaye aikuwa ta faki idanunsu Nisha tajata gefe tana mata tambaboyi aikuwa nan take ta amsa mata lokacin zee babu kudi agunta nan take takira mahabeer ta kafa masa kuka Dole yazo ya iskota ya tsaya kofar gida duk gidan yana zuwa tunda abokinsa ne hadeem din kudi tace ya bata zata sayi kayan kwalliya nan take ya bata dubu ashirin ya tafiyasa duka taba habibi tace ahado mata kayan maye masu tsada aikuwa habibi taje ta hado mata na dubu goma taci dubu goma to zee cikin dare tasha ta kwale tayi ta haukanta sai asuba tayi bacci ban garan Dr Sardauna ko da mashakurah ya dan sabko saide yanzu baya yawan kiranta irin nada yana bata dai kulawa kadaran kada han ne shi har yau baima san zee bata gidaba
yau ta kama monday tun karfe 7:00am Nisha tayi shirin tafiya makaranta zee na sharara barcinta dan kwana biyu bata bacci saboda kwayoyin da take ci da sirot da take sha, karfe tara Dr ya fito cikin shirin zuwa Office yau cikin suit bakake ya hade Wanda suka fito da asalin farinsa da kyawunsa da kwarjininsa gilashi bakine manne kan fuskarsa sai zuba uban kamshi yakeyi da sallama ya shigo parlon dukansu suna kan dining har mahabeer karasowa yayi ya gaishesu ya yabi iyayansa daya bayan daya ya rumgumesu yaja kujera ya zauna tea ghaisha ta hada masa mai kauri yasha agaugauce ya Mike dan

Jiransa akeyi kiss yama ghaisha"mamana sai na dawo Daddy yace"Faisal nifa gunsa yaje yana sakin murmushi ya masa kiss din nanah tace"yayamu zan bika daukarta yai ya mata kiss" ki zauna dai autarmu nawwara ta dawo daga school kuyi wasa Mahabeer ya Mike Dr Sardauna ya kallesa "bro yau da wuri zaka fitane?? " eh wlh muje ka ajiyeni amotarka yau banajin tuki baki Dr ya tab'e Daddy yace ikon Allah motocin shiga har ukku gareka amma kace motar k'aninka zaka shiga ficewa yayi yana dariya"wlh Daddy zolayarsa Nike ni gun zainab zan biya ma wayarsa ta dauki ruri ajiye nanah yayi ya ficewarsa yana amsa waya Daddy yace"Mahabeer yau kaje ka kawomun momyna? " to idan na taso daga gun aiki zan biya na daukota ya fice shima Daddy ya Mike yaje yayi shirin fita Kamfani Dr Sardauna na fita ya shige mota yau wata Jeef ce fara wuleliyarta ya fita da ita

✨✨✨✨✨✨✨

*Saudi Arabia* Madina gidansu ummi Raiyan Fahad Abbu Rahaman ne zaune awani hamshakin parlo kusansa Aminah ce mahaifiyar Raiyan tasasa GABA da kuka shiko babu abin da yake daga masa hankali irin kukanta lallashinta ya fara dan yayi mamakin yada ta sabko lokaci daya take bukatar yarta da jikarta ayanzu Hassan ya kalla "ku tashi maza yanzu zamu tafi makkah gun umminku fuska Hassan ya yamutsa maganar ido Abbu Rahman yamasa shida hussaini suka Mike kallonsa tayi"dani za'a tafi azafafe yace"ba gidan uban da zaki bini yanzu zanje nazo dasu kuma yar iskar diyar nan tata aure zan d'aura mata da Fahad karami idan taki wlh zan iya yin abinda ba'a tsammani ni yamike yana bala'i ya fice zuwa shirin tafiya makkah dan sunada labarin kaurata abinda yasa suka sani kuwa shine washe garin tafiyarsu zainaba ta saka a samo mata wani gidan acikin Aziziya ta bar khalidiya wani narkeken gidane daga ita sai mai aikinta suke rayuwarsu tasa asanya yan haya agidan itama kuma hayarce take. to abinda bata saniba mai gidan abokin Fahad ne shine yabasa labari, da misalin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login