Showing 132001 words to 135000 words out of 135756 words
yayi yana murmushi,"
*Hanna* tana isa da gudu tafad'a jikin ammma murna kamar tayi yaya, haka tayi farin cikin ganinsu karima sosai."
Nan aka shiga jajanta maiyafaru, kowa sai alhini yakeyi, kowannen cikinsu yakwana da zullumin abunda zai faruu gobe mafii yawancinsu basuyi bacci ba, sun kwana sunakai kukansu wajan ubangijinsu,"
Washe gari da sassafe *hanna* dasu karima suka wuce court tareda marshalll" anan sukarima suka kalli yayarsu rauda wacce take kasar waje tana aure," marshall ne yasanarda itaa cewa k'annenta suna raye."
Sosai tayi murnar ganin k'annenta hadda kukan murna."
Bawata shari'a mai tsayi akayiba kasancewar marshall yad'ade da gabatarda shaida, basuda wani abunda zasu kare kansu," Mafii ywancinsu an yanke musu hukuncin kisa yayinda wasu daga ciki aka d'auresu rai da raii, ayau su karima sunyi farin ciki duk da kasancewar bawai angabatarda sharia akan mahaifansu da aka kashe bane tunda bawai sunada wat kwararriyar shaida bane, amma hakan yayi mata dad'ii tunda sunga, wanda sukeson gani awulakance."
Haka suka tattaro suka dawo gida kowannensu cikeda farinciki."
Kilishi ce zaune ad'aki tarasa wacce shawara zatabi, tarasa mekeyi mata dad'ii." shin tatashi taje tasanar dasune komai zai biyo baya ya biyo kokuma tajira tagani koda gaske boka yakeyi mata."
To be continued
Ur's
Z33iiyyb3rw3r
[8/16, 4:07 PM] 6ta Abuh: *BIBIYATA AKEYI*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Writing by
*©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*
_Like my page on Facebook=zaynab BAWA novels_
_Join my group on Facebook= ZAYNAB BAWA NOVEL'S_
```Wannan shafin sadaukarwane ga duk wani mai karanta BIBIYATA AKEYI dakuma fan d'in buk d'in kai koda ace baka karantawa ko sunan littafinne yayi maka dad'i nasadaukar da wannan littafi gareka." kusani kune abun alfaharina."```
*
*continuation of page 99*
Bacin raii sosai labba tashiga, dan rashin samun visa da batayi ba, har sai nanda kwanan biyu," gashi tayi fushi bazata k'ara kiran kowa ba, saidai kawai su ganta." haka kuwa akayi dan share kowanne daga cikinsu tayi bata k'ara kiransu ba, tazauna zaman jiran visa."
Bayan su *hanna* karima da labba sun koma gidane aka shiga jajjaba abubuwanda suka faru, sukuwa karima abida rauda twince da kabir, ransu yayi dad'i kasancewar, ayau an hukunta masu laipy, iyayenta kuwa sai dai suyita binsu da addu'a sannan suroqa musu gafara awajan ubangijinsu."
Ranarda yamma danginsu karima suka iso kar6ansu, dan dama ansanarda su cewa yaarn suna raye."
Koda sukazo kamar yadda akayi zato sun bukaci da abasu yaran," bbu wanda yak'i musu hakan dan dama sukeda ikon riqesu, sai dai ran mama kamar wuta takejin sa, tarigada tasaba, da yaran jitakeyi kamar ita ta haifesu,"
Hakanne tafaru wajen yaran, sa6anin karima, da abun bai mata ciwo sosai, tunda ta tabbata ba dad'ewa zata k'arayi agabansu ba, hasalima ita tafiso daga anzo tambayar auranta abayar, mahaifanta ba'araye suke ba, tasan bawani dad'in zaman gaban dangin nata zatayi ba, kasancewar ba shakuwa sosai sukayiba."
Abin tausayin kannenta tafiji suna wanda dole sai sunzo sunkoyi saboda su."
Godiya sukayiwa su mama sosai ta fatan k'ulla zumuncin da bazai rabu ba." suna kuka haka aka tatttarasu aka tafii dasu."
Najeeb ne zaune da takarda a hannunsa yarasa farin ciki zaiyi kokuma akasin haka, da farko dai farin ciki ne, na abunda yakeso zai samu, amma kuma damuwarsq d'aya itace, bai santaba baikuma san wacece itaba, ko sau d'aya bata ta6a tsayawa ta saurareshi ba."
Amma kuma yanada yak'inin yarinya ce mai tarbiyya, kuma yanada tabbacin tanada alaqa da *hanna* dan haka kawai bazata zo gidansu tazauna ba."
Kumada tatashi bashi adreshi akano ne, kuma bataso yawuce nan da kwana biyu." miqewa yayi sannna yace da zafi-zafi ake dukan karfe." shashin mahaifinsa yanufa koda ya shiga da sallam akishin gide yasameshi."
Bayan ya gaidashi kai tsaye yasanr da mahaifinsa abunda ke tafe dashi, dan shi yanzu gaskiya baya shakkan akan abunda yakeso, rasa *hanna* dayayi yatabbat yayi asara babba yanzu kuma gashi Allah yacanja masa da alhairii, bazaiyi sake yarasa wannan bama,"
Ga mamakinsa murmushi mahaifinsa yayi sannan yace,"
Yanzu barina sanarda en uwana in sha Allah zuwa gobe za'aje kajii." d'aga kai yayi sannan yafita yana godiya, dakin mahaifiyarsa yaje yasanarda ita, itama tayi murna sosai."
Washe gari kuwa iyayen najeeb suka d'auki Hanyar kano," dafarko gidan mai martaba suka fara sauka, dan nan takwatanta masa, hannu bibbiyu mai martaba yakar6esu, nan yasa akayi musu jagora har Zuwa danginta, anan aka dai-dai ta komai dake sukkaninsu y'ay'an mutuncine aka bada sadaki awajen dama da goron tambayarsu sukazo, da kayan nagani inaso, ran ne kawai ba'a tsayarba sai daga baya."
Jin haka washe garii najeeb yataso yazoshi tad'an sake masa alokacin sabo yad'an shiga tsakaninsu."
Bai boye mata komaiba gameda soyayyarsa da *hanna* , eyeyer tausyi yabata ta jajanta masa, murmushi yayi Sannan yace, yanzukam bagashi Allah yacanjamun dakeba," kuma duk tq dalilinta Allah yabiyata, dole mugode mata." alokacinne takeasanar dashi cewa ai ta haihu sannan kuma tadwo, kafin najeeb yatafii sanda yaje yaga *hanna* da baby, gafararta ya nema akan magan ganunda yayi mata, bata nuna damuwa ba tace masa bbu komai, nan yasanr da ita tsakaninsa da karima, fatan alkhairii tamasu, sannan marshall yazo shima suka gaisa, sannan yatafii."
Yaya jalal ne ya iso dan dawowarsa kenan daga tafiya aikuwa bai zarce ko inaba sai gidan *hanna*
Sosqi *hanna* tayi murnar ganinsa, nan yake sanarda ita cewa, aii yakira amaiira yafad'a mata tananan zuwa gobe, kuma goben yakasance suna."
Murna tayi kasancewar ta dad'e bata gantaba, dawowarta kuma takirata baishiga ba."
Sai ranara suna kafinnna labba ta iso da sassafe su yaya hajjah ma duk sunzo, amira itama ta iso, lallai wannan suna yaga dangii dayawa," kasancwar an had'a sunan da walimar dawowar *hanna*
Ba'ayi almu bazzarancii ba, hasalima masu karamin karfi akabi anata bawa sadakaa dakuma mabuk'ata yaro yaga gata sosai yayinda yacii sunan maddiibo."
Su hafsa da hameeda kasancewar kowa ankaita gidan mijinta suma duk sunzo." akwati biyu najeeb ya aiko karima dashi d'aya na baby d'aya na mamansa." yaya jalal ma ba'a barshi abaya ba, shima haka yajido kaya, shikam marshall ba'a zancensa, kasancewar irin kayan dayayi idan yafitar dashi adangi zai zama abun magana shiyasa ya ajiyeshi agidansu, duk ranarda tadwo shashinsa saita samesu." ummii kuwa da mai martaba idan kagansu kamar alokacinne aka farayi musu jika," koda yake aii wannan ne nasu shine suekda iko dashi sauran duka na arone😜."
Kaii tun ina irga kayanda y'an `` *`BIBIYATA AKEYI FAN```* sukayi har nagagara nadaina, dan sunyii kokari, haka *ZAINAB BAWA NOVELS* ma dana facebook dana whataapp duk sunyii bajinta Dan ba'a barsu abaya ba."
Duk wannan biki da akeyi kilishi ko sau d'aya bata leqo ba, kuma bbu wanda yadamuu da hakan y'ay'anta kam komai dasu akeyi awajan."
Washe garin suna da sassafe saiga danginsu karima nan, hassana da husaina sunki zama duk yadda akayi sunqi bbu irin lallashin da ba'ayi musu ba dakuma gatan da ba'a nuna musu ba." amma abun yacii tura."
Daga bayama sai d'aya tadauki zazza6i sannan itama d'ayar takama ala dole aka dawo dasu wajan mama, hakan kuwa yayi mata dad'i."
Dan itama washe garin suna tatafi itada hassana da husaina taso abata *hanna* sutafii amma kunya tahanata tambaya haka tatafi batareda tatambaya ba."
Aikuwa kilishi ganin har kwana uku da fad'in boka bbu abunda yasameta yasakata, ishishishrewa tace dama karya yakeyi."
takira hajiya hadiza tamata tastas."
*BAYAN KWANA BIYU*
Kilishi na zaune ad'aki jitakeyi gabaki d'aya d'akin yafara juya mata."
Rasa yadda zata saka kanta tayi nan danan ta yanki jiki tafad'i bayan ta farfad'o bata sake sanin yadda kanta yake ba," ssai wani irin surutai da takeyi, wanda bazaka fahinmci nai take fad'i ba, ahaka y'ay'anta sukazo suka sameta, mai martaba suka aika aka kira, koda yazo sai bakinta ya bud'e duk wani abunda tayiwa *hanna* sanda tafad'a ran mai martaba abace yafice yabar da'in batareda ya furta ko kalma d'aya ba."
To be continued
Ur's z33iiyyb3rw3r
[8/27, 6:35 PM] 6ta Abuh: *BIBIYATA AKEYI*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Writing by
*©zaynab bawa*
*(Z33iiyyb3rw3r)*
_Like my page on Facebook=zaynab BAWA novels_
الحمدالله
*Alhamdulillah en uwa barkanmu da sallah, Allah ya mai-maita mana* عيد مبارك
*Page 100*
Jikin kilishi dai abun ba'acewa komai dan sai k'ara gaba abuu. yakeyi."
Yaranta gabaki d'aya hankalinsu atashe yake kana kallOKnsu gabaki d'aya sunfita hayyacinsu, away'anna ranaku suna kallon tashin hankali, kokadan basuyi zaton haka daga wajan mahaifiyarsu ba." ahalin yanzuma kilishi tbii shawarar kawqce, tabbas acikin kawaye baduka aka taru aka zama d'ayaba, akwai 6ata garii Acikin su, kamar yadda akwai nagarii cikinsu, akwai masu bada mummunan shawara akwai kuma masu bada kyakkaywan shawara, sannan bakowace irin shawara bace yakamata ana baka kadauketa, bakuma kowacce shawara bace zaka yada ita, aduk lokacinda akace anbaka shawara toh ana bukatar ka nutsu, kayi amfani da kwakwalwarka wajan taceta, haiqaqq akwai bata garin kawaye wanda, afuska zasu numa suna sonka amma azuciya kuma, suna kinka da'ace wani abun farinciki zai sameka cikin zuciyarsu suna bakin ciki." tabbbas kilishi tahad'u da irin wannan kawaye, wanda ayanzu waye garii yawaya, tana cikin wani mumuunan hali duk ta dalilin munannniyar abota."
Kasancewarta abaya mace mai tsoron Allah, saukinsu daya shine duk cikin masarautar bbu wanda yasan cewa kilishi batada lpy, hatta da kuyangu da jakadai an dakatar dasu dag shiga shashinta, wanda yaranta ne kwai sukayi hakan, babban tashin hankalinsu shine shirun da mai martaba yayi."
Tun ranarda yashigo yaganta sannnan yajii irin magan ganunda take fad'i bai kara komawa ba, kuma har yanzu baice komai akan wannan al'amarin ba, yaran kilishi harsunyi zarya sun gajii,"
Zai zauna dasu suyi mgana amma daga zaran sun d'auko masa zancen mahaifiyarsu zai 6ata rai sannan kuma bazai kara cewa komai ba, harsu tashi subar wajan, abun yana matuk'ar damunsu ga abuu sai gaba yakeyi." awannan lokacii su affan suka fara tunanin naimo mai maganii tunda sunjura harsun gaji."
Ranarda kilishi tacika satii d'aya da fara rashin lpy, aranar duka yaranta suna zaune afalo yayinda ita kuma kilishi ke kulle ad'aki, shashekan kukan intisar ne yacika falon, yayinda mafii yawqncii haushinta sukeji, dan dasaka hannunta mahaifiyar su tashiga wannan hali, tsaki affan yaja sannan yace, nifa gaskiya nasamo mafita wadda hakanne kawai zaiyi mana kyau sannnan yayiwa umman ma kyau, zama shirun mufa bazai haifar da komai ba, sai abunda yake gaba ma."
Yaya khadija ce ta amshe maganar ea cewa eh nima fa haka naganii, dan yanzu haka basa anyi mun magana damai maganii, affan ne yayi saurin cewa a'a yaya, nazauna nayi tunani kan hakan fa, baidaceba ace mun shigoda wani mai magani cikin wannan masaurauta bada sanin abba ba, ikilima tayi saurin katseshi da kai dallah rufe mana baki ni ahalin yanzu bansan wani dacewa ba, lapiyar mahaifiyarmu kawai nasanii, shii abban yayi shiru yak'i cewa komai, karfa ka manta duk mugun halinta ita ta haifemu, kuma duk cikinmu bbu wanda yau zaice tata6a daurashi wata mumminar hanya, nasan da wannan arfan yace sannan yakara da cewa" yaya koda aynzu ace umma tasamu lpy, wallhy aikin banza mukayi idan har bamu nema mata lahirarta ba."
Kamar yaya suka tambaya, gyara zamansa yayi sannnan yace abunda bake nufii, yanzu duk cikinmu bbu wanda abunda tayi yadawo kanta ba, dabakinta tafad'i dan haka ita wacce akayiwa abun zamuje munema mata gafara agunta, sannan ayi zancen neman magani,"
Kana ganin hakane nafita, kuma ita hanna zata yarda ta yafee mata?" hava yaya wallhy nasan *hanna* sosai tanada tausayi sqnnan ga hakurii, duk hakurin yaya yariima da kike kallo Allah tafishi."
Gabaki d'aya batada riqo arayuwarta, jijjiga kai sukayi sannnan sukai na'am da cewar sa."
K'arfe takwas na dare 8:00pm su affan suka nufii shashin ummmiii."
Tunda aka gama suna *hanna* takeson tafiya gida, ean tafiso saitayi arba'inn sannan tadawo, da tasamu marshall da maganan yakii fiirr ganin haka yasakata, samun ummii tasanar da ita, ummii bataki mata ba, amma har cikin ranta bawai tanason tafiyanta bane." halin yanzu irin shaquwarda tayi da *hanna* ta dabance, balle yaronda kullum yana gunta, idan kaganshi wajan mahqifiyarsa to tabbas yunwa yakeji, gashi yanada hakurii saiya ini currr ma baiyi kuka ba."
Ummii tasamu mai martaba da zancen tafiyan *hanna* gida, amma shii bai k'ii ba baikuma ce tatafii ba."
Zaune suke ummii da *hanna* a falo, sai labba dake d'aki dauke da jariri, suna cikin zaune marshall yashigo, dan tunda yafita dasafe dawwarsa kenan, ummii ne tayi masa sannu dadawowa sannan tashige ciki, *hanna* ganin ummii tatashi dasaurii tanufii fridge tadauko mai ruwa mai sanyii 6arewa tayi sannnan tabashi ruwan yaja." ajiyar zuciya yasauke sannan yace aikuwa kamar kinsan da ishin ruwa nadawo, nasanii mana tafad'a takaice, ina tare dakaiifa, murmushi kawai yayi bai kara furta komai ba su affan suka shigo da sallama, cikin sakewar fuska suka amsa musu,"
Zama sukayi sannnan suka ta6a hira kad'an, sannan yayya khadija tashiga zayyane musu abunda ke faruwa kafin sugama bayani hanna hawaye ya wanke mata fuska," nan suka had'a da nemanan gafara, kokadan *hanna* bata riqeta ba, alokacin tashaida musu tayafe mata, godiya suka runga yi tareda matsanancin kunyarta data kamasu."
Shikuwa marshall baice komaiba tunda har wanda akayiwa tace tayafe, baiga dalilin dayasa shii zai dauki zafii ba."
Cikin nuna al'ajqbi marshall yace yanzu wayake yimata nagani, bbuu suka bashi amsa atakaice, dan haryanzu abba baice komaiba," aikuwa yakamata yace, marshall yafad'a dan zama hakan ba mafita bane yana gana fad'in haka yajuya ya kallii *hanna* sannnan yace jeki sqnarwa ummii sannnan tafito mutafii baki d'aya muje duba cikin ummma dasauri ta miqe tajeta tasanarda ita abun yacika ummii da al'ajabii, amma haka tafito suka fice, koda suka isa *hanna* kuka tarinka yii ganin jikin kilishi har ummii sanda ta zubda hawaye." dagudu *hanna* tafice bata tsayya ko inaba sai shashin mai martaba, tsugunnawa tayi kan guiwowinta tana kuka tana cewa, abbba mun tuba kamana raii wallhy abba umma najin jiki, kayi hakurii kanema mata wanda zai mata magani, nikam abba nayafe mata, har indai dannii kaki cewa komai."
Tsayawa kawai yayi yana
Kalllon *hanna* , wannan yarinya wace irin zuciya gareta haka, duk wanda zaiyi mata sharrii ita da alkhairii zata bita, ajiyar zuciya yasauke sannan yace" *hannatu* diyata share hawayenki, kinjii kidaina kuka, wannan abuu baiyi dadii bakam nikaina ina neman gafararki, ni abbab bakayimun komaiba itama har cikin zuciyata na yafe mata."
In sha Allahu daga yau za'a fara yimata magqnii zan sanarda madibboo, amin ta amsa sannnan tatashi tafice."
Aikuwa kwanan kilishi biyu dafara magani, tasamu lpy aikuwa tana kuka tanemi gafarar *hanna* kamar yadda hanna tashaida wa kowa tayafe, haka itama ta shaida mata."
Zama sosai akayi agidan yadda mai martaba zafff yayiWa kilishi Sannan yashaida mata dalilin dayasa bazai saketa ba dalilin yaranta ne, anan kuma yasaka intisar ta fiddo da miji."
Aikuwa bata dad'e ba tafito dashi, cikin kwana biyu akayi auran, mijinnata yanada mata d'aya da yara hudu, yanada dukiyarsa, bai nuna bambamcii tsakanin ta da matarsa, zaman lpy sukeyi sosai."
*Hanna* kuwa tatafi gida saita tayi kwanaki arba'in 40 curr acan dan saida akayi auran najeeb da karima kafin tadawo." har tagama kwana arba'in dinta bata ta6a tad'awa wani Kan abunda kilishi tayi ba."
Aranarda zata dawo marshall da kansa yazo d'aukanta,"
*BAYAN SHEKARA BIYU*
*Hanna* tagama karatunta, alokacin kuwa amiira ra yaya jalal shekaransu d'aya da yin aure sannnan tanada tsohon ciki, lokacin labba itama tayi aure dan dangin mahaifiyarsu ta aura, dan haka vatama kasaar."
Hemeeda tahaihu yarinyarta kykkyawa, yayinda hafsat ma tahaihu tahaifii yaro,"
Itakuwa rabi'a haryanzu shiru da zaran saurayi yazo anacewa yafito zai gudu, tun abun yana damun amma har tadaina damuwa dan ta tabbata abunda tashukane ke bibibyarta."
Saukan *hanna* kenan daga k'asar india daga wajan d'aurin auren abiid da fariisa wanda ya aurii matar shahid, matarsane da kanta tasaka ya aurii matar abokinnasa bayan rasuwarsa, dan tana tunanin wanda zai riqeta tsakni da Allah, da mijinta kawai ta yarda shiyasa ta roqeshi, ita kuwa fariisa dafarko ansamu matsala daga wajanta, dan tana kallo kamar tacii amanar mijinta da kuma kawarta ne, sai dakyar kafin ta amince."
Agajiye sosai *hanna* take dan dakyar ta iya k'arasawa falonta nakasa tayi shame-shame, dakinta ma sai marshall ne yak'arasarda ita, aikuwa nan tashiga zazza6i mai zafin gaske gwajin farko yanuna tana d'auke da cikin wata uku, murna wajan dangin marshall baya misaltuwa, bayan wata tara ta haifo yarinyarta mai kamada ita sakk, gar rashin hasken fatarsu ma d'ayane."
Ansha suna sosai yayinda tacii sunan mahaifiyar *hanna* suna kiranta da ainihin sunanta har su inne sunzo sunan tareda isshaq da matarsa wacce ya aura, itakuwa hussentu vata samu damar zuwa ba, sakamakon ciki da takedashi tsoho haka akayi suna aka gama cikin kwanciyar hankali."
*BAYAN SHEKARA BIYAR*
*Hanna* na hango tazama mtashiyar mata wacce bazata wuce shekara ashirin da bakwai ba."
Sai Abdulaziz yaronta nafari dakuma amina mai sunan mama, sai kuma hindu itace ta ukun sannann najeeb d'an karamun yaronda yake d'auke ahannunta."
Dasaurii tashige gidansu bayan tafaka motarta, yaran suka bita abaya, gida naganii acike damm da alamu biki akeyi, Cikin saurii *hanna* tashige d'akin amma tana cewa," hava yaya rabi'a kuyi saurii fa ku fito, ke kince bazakiyi komai ba sai walima, walimar ma yanzu lokacii yanata k'urewa, owwhh *hanna* idan kikayi hakurii yanzu zamu tafii cewar hafsat dake shirin fitowa, aigaradai dabata amsa, ita kuwa *hanna* dakin mama takora yaranta, tawuce wajan walima, washe garii kuwa da sassafe aka d'aura auran isshaq da rabiat