Showing 39001 words to 42000 words out of 135756 words
shi gida zaikoma, bayadda basuyi ba ganin haka yasa abba yi musu driving komawa garin bauchi, "
Itakuwa labba tana komawa duk aburkice yasa ummii tamabayarta mai yafaru tana fad'a mata taga ummii tafita birkicewa, tsayawa kallonta tayi, ummii ya haka menene ya faru,
Ai batad'au lokaci ba ta shaida mata tanaga kamar itace yarinyar da yayanta yakeso dukda bata da tabbaci amma tanada yak'inin hakanne, ai labba najin haka tafashe da kuka dakyar ummii ta rarrasheta, kiran wayar amira tayi tana d'auka tafara tambayarta *hanna* shaida mata tayi batajin dad'i ne yasa ta koma gida da wuri amma yanzu tayi bacci. "
Aikuwa sassafe labba tashirya zuwa gaida ita, sallama tayiwa ummii tafita jitayi kamar ta bita taga jikin amma dai haka sukayi sallama tabata aika takai mata."
Haka aranar tare suka inii da *hanna* ko awajen walima ma hannunta yana jikin na *hanna* . "
Yau takashance Saturday ranar d'aurin aure sai shirye shiryen d'aurin aure akeyi inda k'arfe 11:30 za'a d'aura."
To be continued
Ur's
_z33yyb3rw3r_
[12/2, 9:32 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*
_
_Bismillahirahmanirrahim_
_
Writting by
© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )
My first novel
_Fans ga garon sallan ku, gaskiya yau bansoyin typing ba amma naga yakamata abaku garon sallah eid mubruq dearest_
Page 38
*
Yau takasance ranar asabar, ranar d'aurin auren samha da Abubakar. "
Wanda za'a daurashi k'arfe 11:30."
Tun safe hankalin *hanna* yake tashe sakamakon kiran da abba abokin najeeb ya mata, " yashaida mata cewa najeeb nakwance a asibiti bbu yanda yake dan ko mutane baya iya ganewa."
Bata k'arasa jin mai zai fad'a mata ba takashe wayan kuka tayi sosai wanda har fuskanta da idanuwanta sun kumbura, sunyi jazir fuskan ta yayi luhu luhu. "
Tun safe ko abinci bata iya cii ba ko ruwa batasa abakinta ba."
Muryarta gabaki d'aya ya dashe dan kuka gabaki d'aya tausayin Najeeb ne yacikata tasan ko meye yasameshi itace sanadi. "
Kuka takeyi ad'aki kamar ranta zai fita, tana kuka tana cewa kayafemin dear wallhy nayi danasanin saninka har nasaka acikin wannan halin, kayafemin."
Har kusan k'arfe goma 10 umma tashigo tasameta Ahaka, dkayr ta rarrasheta,
Umma najeeb ba lpy umma natsani kaina najeeb yashiga wani halin ta dalili na. "
Shhhh my doughter bakene sanadii ba Allah yarubuta hakan sayya faru."
Maza tashi kije ki k'ara yin wanka maza kinji 'yata Ahaka tayi ta rarrshinta hartayi wanka tafito, kaya ta za6o mata tabata ta sanya amma ko powder batasa afuskanta ba. "
K'arfe sha daya da rabii 11 :30 aka d' aura auren samha yusuf dambam da Abubakar umar waziri akan sadaki duba dari lakadan ba ajalan ba."
Bayan and'aura can na hango MG kusada ango kaikace shine wannan ango a irin kyau da yayi, fararen kayane k'all ajikin sa, sai fara'a yakeyi yasan yau tabbas mai martaba da moddibbo zasu nema masa auren *hanna* abinda ya dad'e yanajira shekara kusan goma. "
Bayan angama d'aurin auren, mutane sun watse sosai saura d'ai-d'ai ku,
Moddibbo ne ya kalli baban *hanna* wanda ko ba'afad'abaa sunsan shine mahaifinta danshi yakar6i auren samha ma."
Cikin mutumtawa suka k'ara gaisawa, sannan ya d'aura da cewa, in sha Allah hu akwai maganar da nakeso muyi amma kuma tun da mune masu nema nafiso mubika zuwa chan Bayan kakoma. "
Dan murmusawa baba yayi sannan yace ai tunda Allah yahad'amu anan sai muyi kawai basai kunje ba aikomai sauki ake nema,
Da mamakin su mai martaba ne ya amshe maganar wanda a iya saninsu saidai dogarawa suyi magana amma shi baicikayi ba."
A'a dakun bari dai mubiku tunda mumuke neman arziki sai mubika har mazuninku mu nema yafad'a had'eda fad'ad'a fara'ar fuskarsa. "
Jin haka yasa sukasan maganar mai matukar mahaimmacii ne."
Abba ne yad'an gyara zamansa akasan dayake sannan yace, Allah ya huci zuciyar ranka shi dad'e bawai naja da maganrkaba ba amma ai anan d'in zqifi sauki, Allah yahuci zuciyar ka,
Shiru mai martaba da moddibbo sukayi wanda sukansu sunfi san hakan amma hakan dasukayi shizai nuna damuwarsu da abun. "
Moddibbo ne yayi gyaran murya sannan yace to hakan ma yayi, amma sai mud'an sami wajenda bbu matane."
Tashi sukayi dukansu da waziri da mai martaba da moddibbo suka wuce gidan Abba, kai tsaye falon Abba suka wuce. "
Zama mai martaba yayi shida moddibbo akan kujera yayinda Abba da baba suke kokarin zama ak'asa."
Saurin tsaresu mai martaba yayi A'a katashi kuzauna a kujera kada kud'aukeni a matsayin shugaba ko wani mai mulki ku d'aukeni qmatsayin ubanda yazo nemawa d'ansa aure. "
Had'a baki Abba da baba sukayi suna tambayar aure?"
Moddibbo ne yace kwarai kuma a yarima mukazo nemawa auren d'iyarku, gaba ki d'aya tunani nasu ne yatsaya a iya tunaninsu sunsan d'ansa yarima shine sojan da duk kasar guda d'aya akedashi, kuma kakansa ne mai shagon gwala gwalan dasukafi kowanne ak'asar dubai (abu-dhabi). "
To kuma me zayyi da d'iyarsu?? Mutuminda saninsu ko'yar sarkin saudi yanema zai samu."
Kansa ne ya d'aure, shirunda sukayine yasa moddibbo tamabayar ko kunyi mata miji ne??"
Girgiza kai Abba yayi gumina tsattsafo masa, dan yanzu baba yafara tunanin hameeda akazo neman aure. "
Bayaninda da moddibbo yafara ne yak'ara hargitsa musu tunanin,"
Idan kun amince muna nema masa auren yarku *hannatu* wanda yad'au tsawon shekaru yana dakon sonta, adalilin tana yasa har yanzu baiyi aureba. "
Koda anahaka maganar aure yakan shaida mana yanada wacce yakeso tun muna d'aukan abin awasa harmuka dawo tunanin ko aljance ta aure shi Iya addu'a da rokon Allah munyi amma ko sau d'aya baita6a budan baki yace mana ga garinda yarinyar takeba. "
Koda sunanta bai ta6a ambata ma wani ba."
A'ina gayanta shikadai yabarwa kansa sanii dan baima zauna da wani yayi labari ba balle ya fad'a masa, abinda muka sani shine kawai yana matuk'ar sonta, ak'alla shekarunsa 35 aduniya amma har yau baiyi aureba da'an masa magana zaice lokaci yake jira."
Kuma bana tunanin yarinyar tasani. "
Abba da baba sunrasa awani yanayi suka tsinci kansu farinciki ne kokuma akasin haka."
Shiru Abba sukayi sai can yace hakika wannan lamarii akwai rud'ani aciki, baznce kunyi batar kaiba amma fa yarima kukace da d'iyarmu. "
Allah yaja ran mai martaba, kunsan cewa dai yafi k'arfinta kokadan shiba sa'an auranta bane ina yariima ina *hanna*."
Mai martaba akan yaji zafin maganarsu sai ma sanyi dayaji aransa, dan ba kowa bane za'a ce sunje neman aure yafad'ii wannan maganar ba, " Sai marassa son abun duniya,"
Gyara zama mai martaba yayi sannan yace, har inde kun amince ku kira yarinyar mujita bakinta. "
Shiru sukayi dan tunda dakansu sukazo bbu dad'ii ace basu amince musu ba."
Abba ne afili yace Allah ya za6a mana mafi alkhairi, hakan kuwa yafaranta musu rai alamun sun amince. "
d'aga waya yayi yakira umma cemata yayi kuturomin *hannatu* ina falo na yanzu, sannan yakashe."
Umma dake gefen hannatu ne tajuya ta kalleta,tashi kije abbanku nakiranki yana falo. "
Ba gardama ta tashi ta zura k'atoton hijabinta har k'asa sannan tafice."
A k'ofar shiga falon ta tsaya tayi sallama ciki ciki, amsa mata akayi sannan tasa kai tashiga kanta akasa hango Abba da tayi agefe yasa tanufeshi dan batayi tsammani akwai wasu afalon ba ko kadan bata lura ba. "
Gaban Abba tanufa taje ta zauna sannan tace abbana gani,"
Tunda ta shigo falon mai martaba waziri da moddibbo suke kallonta hak'ik'a yarinyar nada hankali kodaga tafiyarta ya nuna hakan mai martaba ne yaji yarinyar ta kwanta masa arayi sosai, " kqllon fuskanta akumbure yasa ya riqo hannunta 'yata mai yasameki?"
Jin haka ne yasa baba kallonta tabbas fuskanta akumbure yake alamun tayi kuka, "
Sunkuyar da kai tayi Abba kai nane kemin ciwo, kinsha magani ya tambaya gyada masa tayii,"
Ga baba fa yazo nan baki gaidashi ba, "
Azatonsu murna dasu kallo tayi amma saitaki d'agowa ta kalleshi, dan tasan tabbas idanta tad'ago zai fahimcii tana Cikin damuwa," *hanna* bakiji mai nace bane ahankali tace ina wuni baba sannu da hanya, " bai amsaba yaci gaba da kallonta, moddibbo yak'ura mata ido akwai abinda yake tunani akwai abunda yakeso ya tabbatar agame da ita."
*Hanna* babanta yakira sunanta d'agowa tayi ta kllashi, kinga wayannan mutanen sai a lokacin ta d'aga ido ta kallesu, gaishesu tayi suka amsa da fara'a, "
Neman aurenki sukazo, ai a lokacin kukan da take maqalewa ya kufce mata, Cikin kuka ta rarrafa gaban babanta, tariqo hannunsa, tana kuka tafara cewa baba kayi hakuri karkasa wasu acikin damuwa kawai kabarni nazauna Ahaka kamar yadda takeson ganina baba kacikaa mata burinta kawai, kar wani yak'ara cutuwa ta dalilina, tunda ta fad'a baba kabarta ta aikata kawai tana fad'in haka kuka tacii k'arfinta aguje ta tashi tafice moddibbo ne yatashi yabi bayanta aka bar su baba da tarin tambayoyi aransu. "
To be continued
Ur's
Z33yyb3rw3r
[12/2, 9:31 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*
_
_Bismillahirahmanirrahim_
_
Writting by
© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )
My first novel
Page 39
*
Bata nufi ko ina ba sai garden tazauna akan resting chairs, sai kuka takeyi, kamar wanda danshi aka aikota duniya. "
Ganin yanda take yasa moddibbo nufan wajen, tsayawa yayi ya gama nazari akanta, dafa kanta yayi, daogowa tayi takalleshi farine soll tsoho mai farin gemu yanada tsayi madaidaicii,"
Sunkuyarda kanta tayi dan wani irin kwarjini yamata, "sunkuyawa yayi ya zauna da nishi alamun tsufa ta kamashi,"
Cikin sigar kwantarda hankali yafara magana irinnasu na dattawa,"
Jikata nasan kina Cikin damuwa amma kisani kuka ba shine mafita ba. "
Akullum ki yawaita addu'a shine maslahar damuwarki, sunkuyarda kai tayi ta cigaba da wasa da yatsunta,"
Murmushi irinnasu na manya yayi sannan ya cigaba da cewa, mai nene dalilin da zaisa iyayenki su za6a miki miji amma ki bijre musu? "
Sunkuyarda kai tayi hawaye d'aya nabin d'aya sai yanzu take danasanin maganganun data fad'a musu kuma agaban wa'yanda sukazo neman auranta."
Baijira amsarta ba yaci gaba da cewa, "
Kinsan cewa bbu wanda yake da mahimmanci a rayuwa irin mahaifa, kikasance Akullum mai san faranta musu," girgiza kanta tafarayi hawaye d'aya nabin d'aya, " ahankali ta furta ba haka bane,"
Toh menene Jikata?"
Yatambaya Cikin sigar lallashi, "
Girgiza masa kai tayi, Murmushi yayi dan tabbas yasan akwai abunda take boyewa."
To kifad'amun dalili har inde bakyaso nazargeki akan kin yiwa mahaifanki biyayya, " bansan cutarda wanda yake tareda nine ko kadan banso wani yasake cutuwa kamar yadda najeeb yacutu,"
K'ura mata ido yayi nasan gaskanta abinda yake tinani,"
Cikin hikqma yace kidaukeni matsayin kakanki, danni nadaukeki ajikata kifada mun duk wani abinda yake faruwa da rayuwar ki karki boyemun komai, in sha Allah tare zamu nemo mafita, "
Cikin yarda da tsohon tafara bashi labarin duk wani abinda yafaru har izuwa kwanciyar najeeb a asibiti, dogon numfashi yaja sannan yace mata, jikita tunda naganki nasan kina tareda sihiri ajkin ki saidai baida k'arfii dan atunanina yawan addu'a da kike ya ne yasa abin baiyi karfii ba amma in sha Allahu da addu'a zamu yakesu bbu wani abinda yafi karfin addu'a, " _mutane musani bawai dan kinada damuwa sai jitafi wajen wani yace zai miki aiki awarware sihiri shine masalaha ba A'a akwai addu'oii dayawa acikin qur'anii mai girma wanda su kadai sukan iya samawa dan adam waraka dan Allah mukiyaye zuwa gun wasu malaman yawancinsu bokayene suke k'arya dasunan malamai Allah yakare_
Nasiha yamata sosai sannan yace ga addu'a kiringa karanta ta kartabace abakinki da yardar Allah duk wani mai nufan ki da sharri zai koma kamsa ```waraddal lahul lazina kafaruh bigaizihim lam yanalu khaira wakafal lahul mu'umininal qital wakanal laahu qawuyan azizan hakima```
Wannan addu'a hakika tana maganin sharri dakuma mai nufinka da sharri ahaka yayita mata nasiha sannan yace taje tasamu mahaifanta tabasu hakuri, "
Jikata d'agowa tayi tayi kalleshi, gobe kizo gidana ki kar6i sauran addu'oiin, sannan zansa ayita saukan alqur'anii,"
Sannan abu na karshe bawai danna fito a dangin abadallah ba yakasance yaro mai hankali, duk duniya banda mahaifanki banga wanda zaisoki sama dashi ba, "
Yasoki tun baki mallaki hankalin kankii ba, yasokii tun bakisan kankii ba inatunanin duk wanda zaki aura abayansa yake amma inaso kiyita addu'an zabin alkhairii,"
Allah ya miki albarka amin ta amsa d'an hira suka ta6a sannan yatshi har bakin kofan tarakashi dake yatsufa ahankali yake tafiya sanda suka isah bakin falon taja tatsaya alamu yamata akan tashiga bbu musu tashigo shima yabi bayanta abakin kofa tatsaya ta durqusa guiwaowainta duka biyu sannan ta sunkuyarda kanta, "
Cikin rawar murya ta ce abba dan Allah kuyafemun nayi kuskure amma in sha Allah bazankara maimaita kamarsaba."
Mai martaba ne yayi magana wanda dama tun maganarta tafarko Bata 6ata masa raiba yasan dole da dalili, gashi yanzu yanda tatsuguna tana neman afuwarsu yasa yarinyar k'ara shiga aransa, Cikin sigar gamsuwa yace tashi kice d'iyata baki mana laipyn komai ba Allah yamiki albarka ahankali ta amsa sannan tatshi sum sum tafice, " mai martaba suka fito sun tsaida zancen su na iyaye kowa ya amince amma sunaso yaran su dai-dai ta kansu, godiya mai martaba yayita musu Ganin haka yakarasa suka tabbatar lallai wannan al'amari nada mahimmancii."
Karfe hud'u aka fara shirye shiryen d'aukan amarya Motoci ne nagani na fad'a akalla sun kai motoci ashirin kowacce baka ne wulik sunyi parking suna jiran fitowar amaryarsu,"
Itakuwa tana ciki ana mata nasiha sai kuka takeyi, kamar wanda akayiwa mutuwa dakyar aka fita da ita da matanda sukazo daukan amarya mamane riqeda ita suka shiga, "
Fada suka wuce dan anan zata zauna zuwa gobe akaita gidanata,"
*Hanna* kuwa nad'aki iyakacin hameeda ne tabisu, iya karrama an karramasu, a shashin waziri umar iyayen abubakar aka ajijeta kafin agama biki, shashin yahad'u sosai, site d'in abubakar aka ajiye amare. "
Sannan wa'yanda suka kawota suka koma gida."
Karfe kusan 6 labba taga bbu *hanna* bbu dalilin zatajo gashi, bayan magrib za'a fara shirin dinner, "
D'aukan motanta tayi ta nufi gidan dakyar ta lallashi *hanna* tabiyota dan itada tace bazata ba."
Da'akazo wajen shiryawa ma sanda akayi rikici ce tace bazatayi kwalliya ba kuma su hud'unsu sanda ummii ta d'auko musu makeup artist,
Sanda suka addabeta ne yasa tayarda aka mata light makeup amma bakaramin kyau tayiba."
9 aka fara tafiya wajen dinner, su *_hanna_* sune k'arshen tafiya alokacinda motarsu tatsaya a katafaren hotel d'in alokacin motocin MG suka danno hancinansu Cikin hotel d'in. "
Fitowa sukayi amotan
_ Suka nufi ciki shima MG Fararen kaya yasa manya bakaramin amsarsa su kayi ba gabaki d'aya sai daukan idanuwa yakeyi, "
Amfara gudanar da event kowa yana sha'aninsa banda hanna data takure agefe bayanda ba suya tafita ba amma tak'i."
Shikuwa MG gabaki d'aya ya gundura da zaman wajen gashi ba kalli *hanna* ba kuma andameshi da kallo barin 'yan matan dake wajen, " duk da akayi akwai wasu daga Cikin sojojinsa a wajen amma hakan bai hanashi takura ba,"
Sanda event yakai tsakaiya aka kira k'annen amarya kowa yaje amma banda ita ganin yanda amaryar ta 6ata rai take kollonta yasa ta d'anji bbu dad'ii jakar kud'in tadauko ta nufi gun amaryar liki tafara mata sai alokacin MG yaganta yashagala da kallonta ga wanikyau da tayi sai dai fuskarta akwai alamun damuwa duk sai yaji bbu dad'ii ganin ta Cikin damuwa atunaninsa ko zancen auransa da aka mata ne yassata Cikin wannan damuwar. "
Bata ankaraba sai ji tayi kawai anfara mata ruwan kud'ii na liki kamar itace amaryar."
To be continued
Ur's
*Z33yb3rw3r*
[12/2, 9:32 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*
_
_Bismillahirahmanirrahim_
_
Writting by
© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )
My first novel
Page 40
*
Juyawa tayi dan ganin wayake yimata manni ganin ya jalal yasata sakin murmushimurmushi ahankali tace," yaya ina kashiga?"
Bana ganinka, dan ta6e baki yayi, "
Banason hayaniyane yasani barin gidan,"
Sai kun gama bikinku zandawo, "
Harda saleem ko?"
*Hanna* tace eh yace mata atakaice,
Sanda yazo dai-dai kunnenta ya rad'a mata kinyi kyau d'an murmushi takarayi, yad'an kama ha6ansa🤔 ya kalleta kamar maisan gano wani abu a tattare da ita amma kinrame kad'an, mai yake damunki? "
Narai narai tayi da fuska alamun batasan tambayan,"
Ganin haka yasashi jan gyalenta ya nufii wata kujera da ita."
Alokacin ran MG inyayi dubu ya6acii har wani hucii yakeyi gashi idanuwansa sunyi jazirr. "
Jiyake kamar yaje ya shaqe jalal,"
Murmushin data masa yatsaya masa arayi gashi yawani ja mata gyalenta ita kuma tabishi. "
Runtse idanuwansa yayi kawai yana fitarda hucii mai tsafii."
Dakyar ya iya fita ya yiwa ango da amaryarsa liki, "
Yana tashi kallo yadawo kansa."
Daga nesa mutane keta d'aukansad'aukansa a photo dan wanda basubasu ta6a kallonsa bama yau sun kalleshi ba'a TV ba, balle masu pics wanda sunsan dasu samu kud'ii kowane mai photographer, burinsa ya d'aukeshi."
Dakyar yatsaya suka d'auki pics da couples d'in amma yahad'e girar sama data k'asa. "
Kusan 12 akagama diner, hanna tace ita dole gidan su zata wuce dakyar labba ta rarrasheta tayarda ta bisu shshin ummii suka nufa lokacin dare yayi sosai yasasu wucewa d'akin labba,"
Wanka suka fara yi sannan suka kwanta. "😴
Najeeb an sallameshi a asibiti jikinsa yad'anyi sauki saidai damuwace fall arayinsa danko abinci baya iyacii balle magana,"
Iya tambayoyin duniyarnan ammasa amma bbu amsa