Showing 291001 words to 294000 words out of 375662 words
Chapter 98 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx
a hankali, jin
karatun ta ne ya saka ya karasa shigowa
tunda ya tabbatar a suturce take sai ya
zauna acan gefe yana kallon ta. Bata dago kai ba duk kuwa da zuciyar ta tana son gain sa musamman tunda an gaya mata bashi da lafiya. Haka suke yi
yanzu, tunda aka sallamo shi daga asibiti
take yin fushi da shi akan laifin dukan
matarsa da yayi, amma kuma zuciyarta
tana matukar tausaya masa halin kuncin
da tasa zuciyar take ciki kuma tana neman hanya mai kyaun da zata bi ta saka dan lelen nata a farin ciki in dai hanyar ba haramun bace ba kuma ba zata cutar da shi in the future ba. Sai dai ta cigaba da
tsare gida ne dan jikinsa ya gaya masa ya
san cewa abinda yayi ba dai dai bane ba
kuma ya bata musu rai sosai saboda ya
kiyayi gaba. Plan dinta shine sai yayi
laushi sosai ya bada hakuri sannan ta
saka shi a gaba yaje ya bawa Safina
hakuri a gabanta sai kuma ta hada su su
koma gida tunda alhamdulillah jikin su duk
su biyun yayi sauki sai abinda ba'a rasa
ba. In yaso ita sai da daukarwa safinan
yan aiki tunda Mommyn ta tayi fushi ta
kwashe nata. Kuma ita ta fahimci
Mommyn sosai, dan idan ita ce in her
shoes aka yi wa Mufida abinda akayi wa
Safina ta tabbatar sai tayi abinda yafi
wanda Mommyn tayi. Sai dai kuma ba ta
jin zata kasance in her shoes din, dan
halin Safiya da na Mufida ba daya ba ne
ba. Sannan yanayin auren Mufida da na
Safina ba iri daya bane ba. Amma kuma yau duk plans din na ta sun ruguje…..... She is no longer sure about
what to do, Not after what Safina told her
da yamman nan and also what Hajjo told her
"Mama" Muhammad ya kira sunan ta a
hankali bayan ta kai karshen surar da take
karantawa. Ta dago kai ta kalle shi,
gabanta ya fadi tayi sauri ta dauke kanta
ta kalli gefe, kuka yayi, maybe tun dazu
ne yayi ba yanzu ba but yau yayi kuka, Ba
zata iya tuna ranar da taga dan nata yana
kuka ba tun bayan girmansa. Wannan
kam shine limit dinta, Already kullum
zuciyar ta a karye take in ta ganshi cikin
dakuwa ballantana kuma ace wai yana
kuka? Muhammad Gidado? She can walk
to the end of the earth to prevent that.
She can walk to the end of the earth to
put a smile on his face.
"Mama" ya sake kiran sunan ta. "Mama
dan Allah ki daina fushi da ni. Kiyi hakuri.
In dai akan Safiyya ne na riga na gaya wa
Abba cewa na hakura da ita. Tunda ba
kwa so shikenan. I will accept duk abinda
kuke so. Ni dai dan Allah ku daina wannan
fushin" ta dawo da dubanta gare shi, ta
sauke idonta akan abin karin ruwan da
yake makale a hannun sa, yayi kokarin
boye hannun, ta dauke kanta tace a
hankali "kayi sallah?" Yace "eh nay)" yana
mamakin yadda har yau bata daina yi
masa irin wannan tambayar ba. Tace "kaje
kaci abinci. Me zaka ci? Akwai tuwo kana
so" ya dan bata rai, shi yadda yake jin
makogwaronsa a rue baya jin ruwa ma zai wuce ta cikin sa ballantana tuwo, Ya girgiza kansa "na koshi" ta dauke idonta daga kansa sannan tace "ta shi ka je" ya mike ya fita yana hada hanya, amma a
ransa yasan maganar bata kare anan ba.
Ta bi bayansa da kallo har ya fita sannan
ta sauke ajiyar zuciya. Kowa da irin
kaddarar sa. This is not what they had
planned for him, aure suka so suyi masa
na gata, a lissafin su auren da wuri zai
saka shi ya kara zama responsible mutum
kuma ya kara masa himma gurin kafa
roots din sa ya yi nasa family din and live
happily ever after. Amma plans din su
gabakidaya ya rushe sanda suka fahimci
yarinyar da suka jima da sanin yana
matukar so ta yaudare shi. A lokacin ne
suka yanke shawarar samun wata su aura
masa dan gyara barakar da suke ganin
Safiyya tayi wa rayuwar sa, not knowing
jefa su sukayi a cikin ramin da har yanzu
ya kasa fito da kan shi. Amma yanzu ta
dauri aniyar ganin ta saka igiya ta jawo
kayanta da kanta, ko da kuwa duniya zata
vi mata tofin ana tsine akan hakan.
Sai da ta gama duk abinda zata yi sannan
ta saka kayan baccin ta ta dora dogon
hijab akai ta tafi kitchen, da kanta ta hada
masa abinci marar nauyin da take ganin
zai ya ci, noodles irin dahuwar da yake
so, sannan ta hada masa hot chocolate yana tiriri. A’isha da ta tayata yanka vegetables din tana murmushi tace “Gaskiya zance da yaya karami (haidar) shima yayi rashin lafiya dan ake hada mashi wannan delicious din” murmushi kawai mama tayi bata ce komai ba sai kuma tace mata ta dauka ta kai mata kofar dakin Muhammad din. Ita kuma ta bita a baya.
Sai da A’isha ta ajiye ta juya sannan Mama tayi knocking kofar, shiru ba’a yi magana ba, ta sake knocking shima shiru sai ta tura kofar ta shiga da sallama da tunanin ko yana toilet ne amma sai ta ganshi a zaune akan study table din sa da laptop a bude a gabansa. Hankalin sa gabaki daya yana kan screen din laptop din. Kasacewar ya juya mata baya ne ya saka itama ta tayashi kallon abinda yake kalla.
Safiyya ce akan screen din, kamar video ne yayi mata tana zaune akan swing shi kuma yana tsaye a gefen ta yana dan tura ta da hannun sa kadan. Daga dukkan alama hira yake yi mata mai dadi dan sai murmushi take yi Amma Mama bata jin abinda yake cewa daga inda take tsaye. Yayi zooming fuskarta a lokacin da ta dan kwantar da kanta jikin igiyar swing din tare da lumshe idonta alamar hiran yana mata dadi. Sai a lokacin Mama ta kara tabbatar kyawun halittar Safiyya
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: Safiyya ce akan screen din, kamar video
ne yayi mata tana zaune a kan swing shi
kuma yana tsaye a gefenta yana dan tura
ta da hannun sa kadan kadan. Daga
dukkan alama hira yake yi mata mai dadi
dan sai murmushi take yi amma Mama
bata jin abinda yake cewa daga inda take
tsaye. Yayi zooming fuskar ta a lokacin da
ta dan kwantar da kanta a jikin igiyar
swing din tare da lumshe idonta alamar
lilon yana yi mata dadì. Sai a lokacin
Mama ta kara tabbatar da kawun halittar
Safiyya. Kyakkyawa ce ajin farko and she
has a unique kind of eyes masu melting
zuciyar duk wanda ya hada ido da ita, and
her smile is contagious, da wahala tayi
murmushi wanda yake tare da ita bai taya
ta yi ba. Ya jima a haka yana kallon
fuskarta Mama da take bayansa tana taya
shi. Sai dai a cikin videon without warning sai
Gidado ya tura swing din da karfi, ta dan
yi karamar kara tare da bude ido cikin
toro, ta kuma kankame igiyar a lokacin
da lilon yayi sama da ita. Daga inda Mama take tana iya jiyo dariyar Gidado daga cikin laptop din, dariyar da ta jima bata ji yayi irin ta ba.
Ta danyi gyaran murya, yayi sauri ya kife
fuskar laptop din amma kuma bai juyo ba
dan ya tabbatar ta gani. Sai data kira
sunansa "Gidado" ya juyo da kujerar da
yake kai amma bai daga ido ya kalle ta ba.
Tace "kazo ka dauki abinci gashi nan a
bakin kofa" ya taso ba tare da yace komai
ba ya zo ya dauka ya koma kan kujerar ya
zauna yana kallon abincin tare da jin
soyayya mahaifiyarsa tana karuwa a
ransa, "ka tabbatar ka cinye kuma ka sha
maganin ka. Zan dawo in gani" yace "to"
da murmushi a fuskarsa, yana mamaki
kuma yana son yadda Mama take bashi
umarni tare da treating dinsa kamar dan
primary.
Har ta juya sai kuma ta tsaya ta yi masa
tambayar da dazu ta manta bata yi wa
Hajjo ba "how did Safiyya's mother die?"
Tambayar ta zo masa a bazata. Ya daga
kai yana kallon ta amma kuma bai ga
alamar wasa a fuskar ta ba. Sai a amsa, a
ransa yana yiwa Safiyya godiya da ta gaya
masa komai "she drawn" ya fada, sai
kuma ya yi tunanin kara mata bayani
"Safiyya ce ta fada cikin water reservoir
when she was 2 years old, Her mother jumped in to save her. Ta fito da ita, ita kuma ta mutu a ciki",. Ta cigaba da kallon sa kamar ba ta fahimci abinda yace ba, amma ya fahimci maganar ta taba zuciyar
ta sosai. Ta juya masa baya da sauri,
maybe trying to hide her tears, sai kuma
ta ce "goodnight" sannan ta fita.
Part din mai gidan ta ta wuce direct, ta
bude kofa ta shiga ta tarar da shi yana aiki
akan computer, ya juyo yana kallon ta sai
kuma yayi murmushi tare da daga hannun
sa yace "na daina, na daina" ya san ta
saka dokar cewa dare lokacin iyali ne da
hutawa da kuma ibada, duk wani abu da
za'a yi na neman duniya to ayi shi da rana.
Amma sau da yawa ba bin dokar tata yake
yi ba sai dai in ta kama shi ya bada hakuri.
Bata kula shi ba dan abinda yake ranta ya
fi wannan, sai ta wuce kan lounging chair
din da take dakin ta zauna, yayi wheeling
study chair din tasa zuwa gabanta ya
tsaya yana kallon ta. Da karyayyiyar
murya tace "dazu naji kace Gidado bashi
da lafiya, me yake damun sa?" Abba ya
dan yi mata murmushi "he will be okay
kamar yadda na gaya miki, Rigima ce da
taurin kai da ya dorawa kansa kwanan
nan" ta gyada kai tana kara fuskantar inda
maganar ta saka gaba "akan Safiyya ne
ko?" Abba yace "yes. Kamar sun samu matsala ne I think. He told me wai sun rabu tunda bama so. Ita ma kuma wai babanta baya so. Amma na san fada
kawai yake yi ba wai rabuwar suka yi ba"
ta danyi murmushi, ita taga abinda ta gani
yanzu a dakin sa.
Ya danyi gyaran murya sannan with
serious voice yace "kince zamu yi
magana akan Muhammad. Wacce
magana ce?" Ta danyi ajjiyar zuciya tare
da cewa "kai ma ka fadi haka ai. You first"
ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"yaron nan ba zai hakura da yarinyar can
Safiyya ba. I think we need to look into
other options than rabasu da karfi. A
shawarce zan saka a yi min bincike akan
yarinyar, sannan zan je inga mahaifinta inji
shi menene take dinsa on all this tunda
Gidado yace min shima ya hana yarinyar
haduwa da shi. Ma'ana yasan abinda ake
ciki kenan. Amma sai mun fara bincike
akan yarinyar dan a lot of things don't add
up about her",
Mama ta dan girgiza kanta a hankali tace
'"ba ka bukatar yin bincike, I have got all
the informations we need about yarinyar"
yayi shiru yana kallon ta da mamaki "how?
When?" Ya tambaya dan ya san bata boye
masa komai. Tace "dazu nayi magana da
Safina, akan zancen komawarta gidan mijinta tunda jikin su duk yayi sauki. She told me wadansu maganganu da suka razana ni sosai" ta fada da karyayyiyar zuciya, ya bata rai, baya son bacin ran
matar ta sa ko kadan, yace "wadanne maganganu kenan?" Ta girgiza kai "maganganun basu da muhimmanci. Surikar muce still.
But she is not the right choiceor Gidado."
Ta danyi shiru kamar yadda shima yayi
yana kokarin fahimtar ta, sai kuma ta
cigaba "sanda Hajjo tazo garin nan tazo yi
mana murnar bikin su Muhammad ta ga
pictures she told me ta san Safina, she
told me they are family friends, and dazu
maganar da Safina ta gaya min akan
Safiyya ta daga min hankali har na fara
mummunan tunani akan Gidado so l
called Hajjo and asked her a favor, nace
dan Allah ta gaya min duk abinda ta sani a
kan Safiyya step sister din Safina. Farko
kamar ba zata fada min ba, sai da ta
fahimci hankali na a tashe yake kuma na
gaya mata abinda yake tsakanin Gidado
da Safiyya da kuma abinda Safina tace
min akan safiyyan wanda har ya tayar min
da hankali nake neman gaskiyar lamari,
Sai ta saka nayi mata alkawarin ba zan
gaya wa kowa a duniya ba, har kai, sai da
nayi mata wannan alkawarin sannan ta gaya min komai".
Ga mamakin sa sai yaga hawaye yana bin
fuskarta, ta saka hannu ta share sannan
tace masa "na riga nayi mata alkawari, bana son in karya alkawarin da nayi mata. Amma abinda zan gaya maka shine yarinyar nan Safiyya ta sha wahalar da
ban taba gani ko jin labarin wadda ta sha
irin ta ba. Ta fuskanci kaddara mai zafi. Kaddara kuma irin wadda zata iya fadawa a kan kowacce ya mace" ta danyi shiru still idonta yana kasa sannan ta sake cewa
"ni mace ce, kuma ni uwa ce, watakila ku maza ba lallai ku fahimta ba amma ni na fahimta. Tunda har Allah ya sarke zaren kaddarar Gidado da na Safiyya har yanzu ta zamanto ita ce farin cikin sa, ni na amine kaje ka nema masa auren Safiyya ko dan mu samu ladan yarinyar nan sannan kuma mu samar da farin ciki ga dan mu".
Ya dan girgiza kai cikin mamakin maganar
ta yace "amma ba kya ganin this will be
too much for him? I mean mata biyu at his
young age? Kuma mata biyun ma
makusantan juna? Zai fuskanci crises
sosai a gidan sa" ta danyi murmushi
"wannan kuma zabin sane, zama da su
gabakidaya ko aka sin hakan zabin sa ne, mu namu shine mu sauke nauvin sa da Allah ya dora mana sannan muyi musu addu'a baki daya".
Tana gama fadar haka ta mike ta cire hijab
din jikinta ta rataye tare da hawa kan gado
ta fara gabatar da addu'ar kwanciya
bacci. Ya bita da kallo abubuwa da yawa
suna yawo a cikin ransa. Duk da cewa
shima tun dazu zuciyar sa ta fara karkata
zuwa da wannan barin amma bai dauka
tata zata chanja akala a lokaci daya ba.
Me Safina tace mata? Me kawarta Hajjo
tace mata? Baya son ya matsa mata har
ta gaya masa tunda tace alkawari tayi
cewa ba zata fada wa kowa ba har shi. Shi
kuma zai so matarsa ta kasance mai cika
alkawari.
Sai dai in dai har zai aikata abinda ta
ambata na aurawa Muhammad Safiyya, to
dole ne sai ya san abinda taki gaya masa
din, ko da kuwa ba'a wajenta ba ne ba.
Da maganar ya kwana da ita kuma ya
tashi, Da ita yaje office da ita kuma ya
tashi, Wannan ya sa daga office din bai
tafi gida ba sai ya gayawa driver dinsa ya
kai shi gidan Alhaji Adam Muhammad, Ya
san address din gidan ne sanda yana
bincike game da Safina lokacin auren
Muhammad. Mai gadi ya bude musu cikin sauri saboda gain kamalar sa, sai kuma ya tsaya yana kallon sa bayan ya fito fuskar sa tana nuna alamar ya gane shi,
ko kuma ace ya gane waye shi.
Ya kara gaishe shi cikin girmamawa sai ya
gaya masa cewa gurin mai gidan yazo.
Take ya ga fuskar sa ta dan saura cikin
yanayin jimami sannan yace "baya jin dadi
kam. Bashi da lafiya. Yau kuma kamar jikin
ya matsanta masa dan tun safe babu
wanda aka bari ya shiga gurinsa. Amma
bara in fada a cikin gidan na san zasu san
abinda za'a y" ya fada yana dosar
Hussein da ya fito daga cikin gida da key
din mota a hannun sa daga alama fita zai
yi, suka dan yi magana da Hussain sai
kuma Hussain din ya kalli Abba sannan ya
koma cikin gida da sauri.
Sai Abba yaji babu dadi a ransa, tunda
bashi da lafiya bai kamata ya zo ya dame
shi ba, Wannan ya sa ya sake kiran mai
gadin ya gaya masa "zan koma kawai.
Allah ya bashi lafiya, Zan dawo gobe ko jibi insha Allah" mai gadin ya gyada kai cikin fahimta sannan
cikin girmama wa yace "zan gaya masa
insha Allah, da zarar na samu ganin sa zan gaya masa" driver din Abba ya bude masa kofa ya shiga sannan suka fita daga gidan a nutse kamar yadda suka shigo.
Hussain ya shiga cikin parlour da sauri,
Mommy tana zaune tana waya da sister
dinta da take aure a Kaduna "wallahi har
yanzu bai ce min komai ba Sakina. Na
rasa yadda zanyi. I tried all I can possibly
do amma babu wata amsa. Yau ma
gabakidaya ya kara rikicewa, ya ki ganin
kowa ya hana kowa ganinsa sai Dr
Ma'aruf. Shima kuma duba lafiyar sa kadai
yayi amma bai ce masa komai ba".
Tana cikin maganar Hussain ya shigo, ta
lura magana yake son yayi mata sai tayi
masa alama da hannu cewa ya fadi abinda
yake son fada, yace "baban yaya
Muhammad ne yazo, yana waje wai yana
son ganin Daddy" cikin sauri tace "Sakina
zan kira ki later" ta katse kiran tana kara
kallon Hussain da shima yake tsaye yana
jiran abinda zata ce "baban Muhammad
kace? Wanne Muhammad din?" Ya dan
bata rai "Muhammad din Safina mana,
Shine yazo gashi can a waje yace yana
son ganin Daddy, gashi kuma kinga
Daddy tun safe yace kar wanda ya shiga
gurinsa shine nazo inji me za'a gaya
masa?" Ta mike da sauri kamar zata fita waie sai kuma ta dawo da baya "je ka sake duba Daddyn naku ka ga ko ya bude kofar" ya fita amma bata iya hakura ba sai
ta bi bayansa tana jin dadi a ranta, at last iyayen Muhammad sun yunkuro da niyyar yin maganar da zata gyara auren