Showing 93001 words to 96000 words out of 375662 words

Chapter 32 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7983

mutu, Alhaji Haladu ma ya

mutu, Menene kike so zaki yi yanzu?" Tayi

shiru tana tunani sannan tace "ni ban sani

ba, Ni ban taba yanke wa kaina hukunci ba.

Yanzu tunda kazo kai zaka gaya min abinda

zanyj" ya kalli su Safiya da suke gefe suna

wasa yace "ki hado kayan ki ki taho mu tafi,

kina da sauran yarintar ki wata kila Allah zai

baki wani mijin sai ki sake yin auren ki" ta

danyi tunani sai ta gyada kai da sauri

"shikenan yaya, dama nima ba jin dadin

zaman gidan nan nake yi ba, zamu hada

kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai. kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai

yana kallon ta yace "ki hada kayan ki nace

ba ku hada kayan ku ba. Wadannan yara ba

da su kika zo gidan nan ba, ki bar su a inda

kika same su nan ne gidan uban su. Ke kadai

ce nauyi na, da ke kadai zan tafi, su nauyin

dangin ubansu ne, su zasu kula da su".

Ta bude ido tana kallon sa sannan ta kalli

yaran nata da suke ta wasan doki a tsakar

daki, Safiya tana yiwa Khadijah doki Sauda

kuma tana binsu a baya. Jabiru ya mike yace

"zan kara kwana biyu a garin nan saboda ki

samu ki shirya a nutse, jibi zan shigo in

dauke ki mu tafi". Ya dauki sandarsa ya juya

ya fita.

Ta zauna ta dafe zuciyar ta tana kallon

yaranta. Kamar yadda ta fada, bata taba

yanke wa kanta hukunci ba a rayuwarta, sai

dai duk hukuncin da aka yanke mata ta bi

shi, yanzu kuma gashi an yanke mata

hukuncin rabuwa da yayanta, yaran da basu

da kowa kaf duniya sai ita. Ya zata vi ta tafi

ta barsu? A gurin wa zata tafi ta barsu? Me

zai faru da su in ta tafi ta barsu? Ita bata da

ilimi, bata san abubuwa da yawa na rayuwa

ba amma ta san cewa duk duniya babu

abinda take so sama da wadannan yaran

guda uku,

15

A

4

P

8:16 PM

Kwana biyun nan haka tayi su cikin rashin jin

da din zuciya, har sai da matar Jabiru da

take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar. take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar

ta abinda yake damunta amma sai ta dauka

kewar mijinta ne, a rana ta biyun Jabiru ya

dawo daukan su, ya fita da kayan iyalinsa da

suka zo dasu ya dawo yace da Hadiza ina

nata kayan? Ta girgiza kanta tana goge

hawaye daga idonta tace "bazan iya rabuwa

da su ba. Ba zan iya tafiya in bar su ba. In

har na rabu da su to a cikin makara nake

za'a kai ni kabari na, ko kuma sune a cikin

makara za'a kai su nasu kabarin" ya kalle ta,

ya kalli yaran da suke zagaye da ita suna

rike da zanin ta amma duk da haka bai ji

cewa ya kamata ya tafi dasu gabaki daya ba

shi a iya fahimtar sa ta rayuwa gani yake yi

yara, musamman yara mata dole ne su

zauna a gidan uban su, a ganinsa haka shine

dai dai.

Yace "shikenan. Ki zauna tare da su din,

amma ki sani in kina zaune a gidan nan tare

da yaran nan babu namijin da zai aure kj" shi

babbar damuwarsa akanta ita ce kar ta rasa

mijin aure, Har zai tafi kuma sai ya dauko

kudi daga aljihunsa a kulle a leda ya mika

mata sannan ya juya ya tafi. Ta bishi da kallo

tana tunanin ko zasu sake haduwa ko kuma

shikenan?

A ranar yadda Hadiza taga rana haka taga

dare da yayan ta a gabanta tana lissafin

yadda zata fara wannan rayuwar amma ta

kasa yanke shawara. In ta kalli yarn ta tuna

cewa yanzu dukkan nauyin su yana wuyanta

sai taji toro ya kamata. In sun tashi da safe

ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin. ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin

karyawa, da rana ma haka, suturar

sakawarsu makarantar su, magani in basu

da lafiya, ga kuma overall tarbiyyar su. Ta

kirga kudin da Jabiru ya bata "dubu goma"

su kadai ne abinda ta mallaka a yanzu. Ta

ina zata fara?

Hayaniya ce ta tashe ta da safe da yake sai

da assuba ta samu bacci, a cikin hayaniyar

ta taji ana ambaton sunanta, ta mike da

sauri taga yayanta su ma duk sun tashi suna

kallon ta fuskokin su cike da toro. Ta kuma

fahimci hayaniyar a kofar dakin ta ne, Ta

tashi ta bude kofa tare da tura yayan ta baya

tana kare su da jikinta yadda ko ma menene

ita zai sama ba su ba. Matan gidan ne da

yayan gidan mata wadanda basu koma

gidajensu ba suke ta masifa. Kusan duk a

lokaci daya suke maganganu amma ta tsinci

was daga cikin maganganun nasu

'"wallahi ba zamu yarda ba, abinda akayiwa

baban mu ba za'a cigaba da yi mana shi ba"

"tunda yan'uwan ta suka fara zuwa, Allah

kadai ya san me suke kawo mata"

"wanda yazo jiya ina kallo ya mika mata wani

abu a leda, jikina kuma ya bani asiri aka

kawo mata zata binne mana a gida mu ma ta

mallake mu"

Hadiza ta fara kokarin kare kanta "wallahi

babu abinda suka kawo min, kudi ne kika ga

ya bani", ya bani"

Amma babu wanda ya saurare ta, aka jawo

ta ita da su Safiya aka fito da su waje

sannan aka fara watso musu kayan su

wajen, tana kuka tana rokon mutanen nan

amma basu barta ba, sai da makota da

sauran yan unguwa suka shiga cikin

maganar amma aka kasa sasanta su, su

haushin duk abinda Alhaji Haladu yayi musu

ne suke kokarin hucewa akan Hadiza da

yayanta suna gain cewa sune sanadi,

bayan su kuma a nasu bangaren basu da

laifin komai musamman ma yaran.

Daga karshe dai aka tafi gurin dagaci aka

sanar da shi, ya aika aka kira su har yara

mazan dan a sasanta su amma abu yaki

yiyuwa sunce su ba zasu zauna da ita a

gidan ba, a karshe dagacin yace to ai itama

Hadiza ita da yayan ta suna da gadon Alhaji

Haladu, dan haka ya umarci limamin

unguwar su da yaje ya raba gadon Alhaji

Haladu a bawa Hadiza nata ita da yayan ta

dan su samu gurin zama da kuma abinda

zasu rike kansu.

Amma sai dai da aka zo rabon gadon sai

babban dan gidan yaya Malam yace ai Alhaji

Haladu duk ya siyar da kadarorinsa kafin

rasuwar sa yay wa Hadiza da yaran ta

hidima, yanzu abinda ya rage kawai shine

gidan da suke ciki, Wannan ya sa gidan

kawai aka raba a matsayin gado, shima

kuma gidan su ka nemi cewa a fitar wa da

Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son. Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son

zama da ita. Shima kuma limamin sai yayi

hakan dan in ba'a raba su din ba ba za'a

samu kwanciyar hankali ba.

6

3

8:16 PM

Hadiza da yayanta sun samu dakin soro,

inda nan ne da dakin Alhaji Haladu, tare

kuma da rabin soron dan su samu hanyar

shiga dakin nasu. Dakin ciki da falo ne da

bandaki a ciki, sai dai kuma matsalar shine

dakin nasa yafi ko ina tsufa a gidan, ginin

yafi na ko'"ina lalacewa. Amma duk da haka

Hadiza taji dadin samun seclusion daga

jama'ar gidan. Ta gyara dakin ta jera

furnitures dinta da kayan sakawarsu da

sauran tarkacen ta. Suna cikin gyaran kayan

nasu ne suka ga anzo da kwano irin wanda

ake rufi da shi an raba soron biyu dai dai

yadda liman ya raba musu, wato hanyar ma

ba zasu hada da su ba. Bata gama mamakin

hakan ba sai ji tayi ana buga musu wani

kwanon a windows din su wadanda suke

tsakar gidan. Wannan ya sa dakunan nasu

suka yi tsananin zafi tunda babu taga ko

daya kuma kofar ma gashi an saka musu

kwano an rufe inda iska zata shigar musu,

Kuma tunda basu da kitchen zai ya zamana

a kofar dakin su suke hada wuta suyi girki.

Wannan shima ya taimaka gurin kara zatin

dakunan.

Farko sauran kudin hannunta suka fara

cinyewa, daga nan ta koma daukan kayan

dakin ta daya bayan daya tana kaiwa gurin

dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya. dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya

musu abinci. A haka har suka cinye duk

samiru da kwallayen ta na aure, a lokacin ne

kuma ta fita daga takaba. A lokacin da take

lissafin inda zata samu wasu kudin ne Safiya

ta kawo mata shawara "Baba Hadiza ki ringa

dafa min wake da shinkafa ina yi miki talla,

sai muke samun kudi muna ajiyewa" Sauda

tace "nima zan ringa yin tallan, nima zan

¡ya" Khadijah tace "Baba Hadiza nima zan

yi".

Hadiza ta tsaya tana kallon su sai ta girgiza

kai, "ba zan dora muku talla ba, in kun tafi

talla ta yaya zan kula da ku? In wani abun ya

same ku a can kuma fa? In kuna zuwa talla

kuma a wanne lokacin ne zaku je

makaranta?" Safiya tace "in mun dawo daga

makarantar zamu ke zuwa tallan ai" Baba

Hadiza ta sake cewa "ba za kuyi talla ba" sai

kuma ta kara da cewa "ni zanyi. Zamu ringa

yin abincin siyarwa ku ku tafi Makaranta ni

kuma in tafi talla, a haka zaku yi karatu har

ku girma kuje babbar makaranta ku samu

babban aiki ku gina babban gida sai ku zo

ku dauke ni ku kula da ni, yanzu amma ni ce

zan kula da ku".

Washegari ta kira dillaliya har daki ta sayi

gadajen ta gida biyu tun na aure, ta sauke

musu katifun kasa tace sun she su kwana,

Kudin kuma da su tayi jari. Daga nan sana'ar

wake da shinkafa ta fara, kullum zata shirya

Safiya da Sauda su tafi makaranta ita kuma

ta dafa wake da shinkafa ta goya Khadijah ta

dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da. dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da

tasha talla, su kuma in sun taso zasu zo suci

abincin da ta ajiye musu sannan su yi wanke

wanke su gyara musu dakin su sai su tafi

makarantar islamiyya, kafin su dawo ita

kuma ta dawo sai tayi musu wanki ta

shanya akan langa langan kofar dakin su

dan ko shanya ba'a yarda ta shiga cikin

gidan tayi ba. Sannan tayo cefanen abinda

zasu dafa gobe. In dare yayi kuma anan

soron su suke shimfida tabarma su zauna

suyi ta hira tana basu labarai, wani lokacin

na babansu wani lokacin na nata yan uwan,

wani lokacin kuma lissafin abinda take so su

zama nan gaba.

Farko ba sa samun wata riba, except that

suna samu su ci abinci kuma jarin su bai

karye ba, daga baya kuma sai Allah ya buda

musu sana'a ta kankama sosai har jarin ya

ishe su suka fara yin awara da daddare a

kofar gidan. Tun a ranar da suka fara dora

kaskon awara Dauda yazo wucewa ya gani

yace "ba zaku mayar mana da kofar gida

dandali ba, ko ku sauke kaskon nan ko kuma

duk ranar da na kuma ganin sa in barar da

shi". Safiya ta tashi zata yi masa rashin

kunya Baba Hadiza ta hana ta, sai suka

janye suka koma kofar gidan makota suke yi

a can,

Shekarun su biyu a cikin wannan yanayin, a

cikin wadannan shekarun sun kuma

shakuwa da junan su sosai, Basu da wani

tension zasu ci su koshi sue makaranta

kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi. kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi

amma suna da junan su kuma suna gain su

kadai sun isi kansu.

12

8

2

8:16 PM

A lokacin ne wata rana suna tafiya a kasuwa

zasu yi cefanen abincin siyarwar su sai

Safiya ta ga gidan hoto "Baba Hadiza dan

Allah mu shiga muyi hoto muma" Baba

Hadiza tace "wanne irin hoto kuma dan bata

lokaci? Muyi sauri mu tafi gida kar lokacin

dora awara yayi azo nema bamu fara ba"

Safiya ta kara rike hannun ta "dan Allah

Baba Hadiza mu dauka, kinga yanzu Baba

ko hoton sa bamu da shi". Wannan ya karyar

da zuciyar Baba Hadiza, tabbas ko hoton

Alhaji Haladu basu da shi. Sai ta amince

suka shiga suka dauki hoton. Not knowing

wannan hoton shine zai zama memory din

su.

The first tragedy struck shekaru biyu da yan

watanni da rasuwar Alhaji Haladu, ranar

Khadijah ta tashi da mugun zazzabi lokacin

tana da shekaru shida a duniya, Baba

Hadiza ta bata magani ta kwantar da ita a

daki amma har su Safiya suka dawo daga

makaranta zazzabin bai sauka ba sai ma zafi

da jikin ya kara yi, aka sake bata wani

maganin har zuwa washegari amma zazzabi

bai sauka ba, a lokacin ne kuma suka lura

cewa wuyanta ya sankare bata iya juyashi

gefe, sannan kuma bata iya hadiyar abinci.

Sai kuka take yi "Baba Hadiza wuyana ciwo

yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar. yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar.

Babu shiri Hadiza ta kaita chemist aka duba

ta aka ce sai asibiti, suka je asibiti a take aka

kwantar da su aka ce sankarau ce ta kamata

saboda rashin wadatacciyar iska a dakin da

suke kwana. Aka rubuta musu ma gunguna

da allurai ga kuma kudin gado, babu shiri

hadiza ta fasa bankin da take fara ribar

sana'ar ta ta biya duk kudaden da ake

nema. Kwanan su biyu a asibitin jikin ya sake

ta'azzara aka tura su asibitin Gusau, a

lokacin Khadijah ko magana bata iya yi. A

can sai da duk abinda Baba Hadiza ta tara

suka kare wajen magani, dama ba wani abun

kirki ta tara din ba. Da kudin hannun ta suka

kare ta shigo mota ta dawo Kura ta ringa bin

gidajen yan uwa da yayan Alhaji Haladu

akan su taimakawa yar uwarsu Khadijah su

cece rayuwar ta amma babu wanda ya

taimaka mata, haka ta ranci kudin mota a

makota ta koma Gusau, kwanan ta biyu da

komawa Allah yayi wa Khadijah rasuwa.

Mutuwar Khadijah ta taba Baba Hadiza fiye

da sauran mace macen da akayi mata,

yayanta sune treasure din ta, zata iya bada

ranta a saboda su amma ita mutuwa bata

tambayar zabi wanda lokacin sa yayi shi

take dauka. Su Safiya sunyi kuka kamar

idanun su zasu fado kasa dan suna matukar

kaunar kanwar ta su amma Allah ya fi su

santa. Sai dai ta tafi ta bar wani rami a

zukatansu wanda babu wani wanda zai iva

cike shi. zukatansu wanda babu wani wanda zai iya

cike shi.

Daga nan kuma sai rayuwa ta komawa su

Safiya baya, babu jari babu riba babu abinda

za"a siyar a samu jarin sai tarin basussuka

da suke kansu, ga kuma kewar Khadijah. A

neme nemen jarin da Baba Hadiza take yi ne

taje gidan Hajiya Kyauta.

Hajiya Kyauta macece yar kasuwa, tana

dillancin manyan kaya kuma tana kasuwanci

zuwa garuruwa da yawa a Nigeria wani

lokacin ma har kasashen waje take zuwa.

Baba Hadiza ta nemi ta bata aron kudi ta

sake tayar da jarin wake da shinkafar ta

amma ita kuma sai ta nemi ta bata jinginar

wani abu kafin ta bata jarin. Baba Hadiza ta

gaya mata bata da komai sai tsofaffin

katifun da suke kwana akai sai kuma kayan

sakawar su. A lokacin ne Hajiya Kyauta ta

bata shawara "kina da yammatan yara

kamar wadannan, ki bani ko da babbar ne in

tafi da ita wani garin in kaita aikatau, duk

wata za'a ke aiko miki da kudin da zai isa ki

kula da kanki ki kuma kula da karamar, ita

kuma kin ga an dauke miki nauyin kula da

ita" Baba Hadiza ta juya tana kallon Safiya

da duk ta fita daga hayyacin ta saboda

wahala, tace "aikatau kuma Hajiya, Satiya ba

zata iya aikatau ba" Hajiya Kyauta tace "to ai

koya zata yi. Na kai yara da yawa kuma

sunyi arziki iyayen su ma haka. Baki san a

inda arzikin ta yake ba" Baba Hadiza ya

girgiza kanta "ba zan iya yi mata haka ba. Ba

zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar. zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar

ta ba. Ni ce mahaifiyar ta. Ni zan kula da ita.

In aikin ne ma ni ki nema min in ringa yi ina

samun kudi ina kulawa da su".

14

5

8:16 PM

Hajiya Kyauta tace "to ai in dai zan dauke ki

in tafi da ke sai dai ki barsu anan ke nan.

Kina da wanda zaki barwa su?" Hadiza tace

"bani da kowa sai Allah. In kina da hanya

dan Allah ki samar min aikatau din anan

garin yadda ba zan rabu da su ba. Sai in

ringa yin aikin ina tara kudi har in samu jarin

da zan dawo da kasuwanci na".

Haka ce ta kasance, aka samo wa Baba

Hadiza aikatau take yi a gidan wasu masu

hannu da shuni, kullum da safe su Safiya

zasu fita makaranta ita kuma zata tafi gurin

aikin ta bayan ta dafa musu abinci ta ajiye

musu, in sun dawo zasu ci abinci suyi

ayyukan su a gida sannan su taflislamiyya,

da daddare zata dawo ta taho musu da

abinci daga can. Albashin ta dashi suke

samu suke cin abinci da kudin sabulun

wanka da wanki da littattafan makaranta,

dan duk talaucin su Baba Hadiza ba ta yarda

sun daina karatu ba, Suttura kuma mostly

kwance ake basu a gidan aikin ta da kuma

makotan su, A haka suka sake yin wasu

shekaru biyun, Baba Hadiza ta dan tara jari

kadan sai ta dawo da yin awarar dare tunda

da rana tana gidan aiki babu damar tallan

wake da shinkafa.

A lokacin ne kuma second traaedv va faru. wake da shinkafa.

A lokacin ne kuma second tragedy ya faru.

Lokacin Safiya ta yi jarabawar kammala

primary school, Sauda kuma


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login