Showing 99001 words to 102000 words out of 375662 words

Chapter 34 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7921

/>
Baba Hadiza da irin burukan ta akan su,

hirar Khadijah da surutun ta, da kuma hirar

rayuwar su a yanzu. "ni dai Safiya bana so

mu rabu, ko kin girma kin yi aure ma sai na

biki gidan ki, duk inda zaki je sai na biki"

Safiya ta ce mata "babu inda zanje ai na

gaya miki. Kuma ni ba zan yi aure ba. Zan

zauna da ke har sai kin gama karatun ki, kin

samu aiki kin gina babban gida sai ki zo ki

dauke ni muje mu zauna tare" Sauda tayi

dariya "ina kewar Baba Hadiza. Ina so inje

gurin ta" suka yi shiru sai kuma tace "ni

kuma so nake in kin kara girma kin yi aure

kin haihu, ina so yar da zaki haifa ta zama

duk abinda Baba Hadiza take so mu zama.

Ta zama yar gayu mai tuka motoci masu

kyau, ta zama mai ilimi da turanci kamar

baturiyar ingila, sannan ta zama kyakkyawa

kamar Baba Hadiza" Safiya ta jawo ta ta

kwantar da ita tace "duk ke zaki zama haka,

Zan cigaba da yin wankau da suyar awara

har sai kin zama haka" Sauda ta rungume ta

tare da cusa fuskarta a wuyan ta tace "bacci

zanyi yanzu, na daina jin toro yanzu. Kiyi

mana addu'a. Sai da safe" safiya tace "to. mana addu'a. Sai da safe" safiya tace

"to

shikenan. Kiyi baccin ki. Sai da safe" sannan

ta karanta adduoin kwanciya bacci ta shafa

musu.

Da assubar fari Safiya ta farka. Amma ba wai

kiran sallar asuban ne ya tashe ta ba. Ji tavi

kamar ana kiran sunan ta cikin baccin ta, ta

zare hannun Sauda daga jikinta ta mike

zaune, sannan kuma ta tashi tsaye ba tare

da ta san me take yi ba. Ita ba ido biyu ba ita

ba a farke ba. Kamar mai sleepwalking. Ta

bude kofar dakin ta fita sannan ta cigaba da

tafiya ba tare da tasan inda take saka

kafarta ba. Sai da ta kai tsakiyar tsakar

gidan su sannan taji wata kara daga bayanta

"yif!" Karar da ta farkar da ita daga baccin

da take yi, sannan kuma lokaci daya tun

kafin ta juya bayan nata jikin ta ya bata

abinda ya far sannan kuma zuciyar ta ta

tabbatar mata da cewa Sauda ma ta tafi ta

barta.

Ta juya da sauri ta kalli dakin da ta fito daga

ciki just few seconds ago, tun daga cikin

dakin har falon har toilet din har soron

gabaki daya katangunsu sun afka ciki, sun

fada akan Sauda,

Tayi wata irin kara wadda gabaki daya

unguwar babu wanda bai ji ta ba, sannan ta

fita a guje ta hau kan tarin kasar ta fara

kokarin daga kanukan rufin da suka rufe

kasar, Kusoshi biyu ta taka a lokaci daya

amma babu wadda taji zafin shigar ta cikin

kafarta, Kuka take yi da iyakacin karfin ta. kafarta. Kuka take yi da iyakacin karfin ta

tana kiran sunan yar uwar ta "Sauda, kar ki

tafi ki barni", Makota ne suka fara shigowa,

wadansu dama already sun tashi da niyyar

zuwa masallaci, daga baya jama'ar gidan

suma suna fito, da kyar aka samu wani

makocin su ya rike Safiya, hannayensa biyu

ya saka ya rike ta gam a jikinsa yana tofa

mata adduoi sannan aka samu ta nutsu ta

tsaya a guri daya yayin da matasa suka hau

aikin hakar kasar. Gini ne irin na da katangar

mai kauri ce sosai gashi ta sha ruwa dan

haka suma mazan da kyar suke dauke ta.

Ba'a samu tono Sauda ba har sai da gari ya

waye rana ta fito sosai. Tun kafin a dauko ta

dama duk wanda yake gurin ya fitar da ran

samun ta da rai. Sanda aka fito da gawar ta

shi kansa wanda yake rike da Safiya gagara

sa tayi. Tayi kan Sauda tana wani irin kuka

mai ratsa zuciyarsa da ruhin duk wanda

yake sauraronta. Ta rungume ta kamar zata

tsaga kirjinta ta saka ta a ciki. "kar ki tafi ki

barni, dan Allah kar ki barni ni kadai"

A ranar hatta yan'uwan Safiya da basa ga

maciji da ita sai da suka zubar mata da

hawaye, Da kyar aka banbare gawar Sauda

daga jikin Safiya aka yi mata suttura aka yi

mata sallah aka dauke ta a makara zuwa

gidan ta na gaskiya, A lokacin da ake fita da

gawar kowa a gidan kuka yake yi, ba kuma

wai kukan mutuwar Sauda ake yi ba ko kuma

kukan sabo da ita ba, kukan tausayin Safiya

ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi

rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi. ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi

rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi.

A lokacin mutane da yawa sun fadi

albarkacin bakin su akan dalilin faduwar

dakin da kuma mutuwar Sauda

6

8:47 PM

'"wannan sabon ginin da akayi shi ya kashe

dakunan"

"to da ya akayi ma aka barsu suke kwana a

wannan gurin su kadai?"

"Ai ruwan cikin gidan gabaki daya cikin

katangun dakunan yake shiga"

Amma kuma babu wanda ya daga maganar

ballantana har a dauki matakin shari'a akai.

Daga nan Safiya ta sake bude wani yet

another page na rayuwa.

She became totally depressed, ta daina cita

daina sha ta daina wanka ta daina magana

da kowa, babu abinda ta so a lokacin kamar

mutuwa, da ana siyan mutuwa da tabbas

zata nemi kudi ta siya wa kanta, Ta koma

dakin Inna Gaje da kwana, tunda bata da

wani gurin zuwan idan ba can din ba, ita ma

kuma Inna Gajen ta dan sassauta mata

yanzu dan bata saka ta aikin komai kuma ko

ta saka tan ma babu tabbas din cewa zata

yi.

Wata daya bayan nan tana kwance a inda. Wata daya bayan nan tana kwance a inda

take kwanciya kamar kullum taji shigowar

yaya Malam, yazo ya shige ta ya shiga gurin

mahaifiyar ta sa a gaishe ta sai safiya taji

Inna Gaje tace "dama jira nake kazo, gwara

ka san yadda zaka yi da yarinyar can kar ta

mace min a daki azo a barni da salati" yace

"me ya same ta?" Tace "bata ci bata sha,

yadda ka ganta din nan a kwance haka take

wuni take kuma kwana. Ni fa ba zanyi jinyar

ta ba. Ku da take yaruwarku ubanku ya bar

muku wahala sai ku san yadda zakuyi da ita,

ni nayi na Allah kuma na gaji haka". Yaya

Malam yace "to Inna ni ai bani kadai ne

yayan ta ba, dan ina babba shikenan komai

sai ace ni? Ba ga su Namadi nan ba su da

suke birni ai sun fi ni arziki" Inna Gaje tace

"to ai ba zasu yi ba, in ta mutu kuma ba za'a

zage su ba kai da aka sani kai za'a zaga.

Dole ka san yadda zaka yi da ita"

Yayi shiru sannan yace "na san me zanyi a

kanta. Ni ba zan kaita gida na ba wallahi in yi

ta rigima da iyali a kanta. Aure zanyi mata.

kwai tsohon hedimastern mu da yayi retire

kwanan baya, dama ya taba yi min maganar

ta yace ko zan bashi ita sai na mayar da

maganar wasa, gwara inyi mata auren kawai

in taje gidan mijin zata warke a can. Gobe in

na hadu dashi zanyi masa magana in har

yanzu yana son ta yazo kawai ay"

Inna Gaje tace "hakan ma yayi, Kace masa

sadaki kawai zai kawo ba sai yayi hidimar

komai ba in yaso sai yayi mata kayan daki,

dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai. dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai

ta je itama tayi irin zaman da uwar ta tayj"

Baba Gaje tace "to Allah ya sa dai kar a

maimaita, kar taje ta kwantsama yaya shima

ya mutu ta debo yayan ta sake dawo mana

nan".

Safiya ta bude idonta, sannan ta tashi zaune

tana kare wa dakin kallo sai kuma ta mike

tana jin kamar kafafuwan ta ba zasu dauke

ta ba. Waje ta fita, taje ta hau kan tudun

kasar da yake nan ne dakin su a da, inda tayi

rayuwa da iyayen ta da yan'uwan ta. Ta

kwanta ta sake rufe idonta tana jin iskar

damuna tana kada ta, tana shakar kamshin

kasar da take kwance akai. Anan ta yanke

hukunci. Anan ta bude sabon babi a rayuwar

ta.

Ta mike kafarta ko takalmi babu tana tafiya

iska tana yawo da ita, tiryan tiryan ta taka

har gidan da tayi niyyar zuwa, gidan Hajiya

Kyauta. Hajiya Kyauta tana zaune a tsakar

gidan ta sai gain yarinya tayi kamar aljana

ta shigo mata, kafarta da ciwon kusar da ta

taka garin tono gawar yaruwarta, Hajiya

kyauta ta mike a tsorace, sai kuma ta tsaya

tana kallon yarinyar ta a tunanin a inda ta

san fuskarta,

Safiya tace "sunana Safiya, Dan girman

Allah ina so ki taimaka min" sai a lokacin

Hajiya Kyauta ta gane ta, ta koma ta zauna

tare da cewa "ke ce yarinyar nan Safiya yar

gidan marigayiya Hadiza, bana gari ta rasu,

sai da na dawo sannan aka bani labarin. da na dawo sannan aka bani labarin

abinda ya faru da ita. Ina yaruwar ta ki?"

Safiya tace "ta mutu, duk gabaki dayan su

sun mutu. Ni kadai na rage. Ni kadai suka

bari", Hajiya Kyauta taji wani iri a zuciyar ta,

yanayin yarinyar kadai ya isa ya bawa

mutum tausayi ballantana abinda ta fada,

tace "Allah sarki. Allah mai iko. Yanzu to ni

me kike so in taimaka miki da shi? Abinci

kike so ko kudi?"

fan 11

2

1

8:47 PM

Safiya ta girgiza kanta "so nake ki dauke ni

daga garin nan. Bani da sauran abinda zanyi

a garin nan. Bani da iyaye bani da yan uwa

bani da kakanni, ban san dangin uwata ba

dangin ubana kuma basa so na, aure suke

so suyi min, so suke yi in maimaita rayuwar

wahala irin wadda Baba Hadiza tayi, so suke

yayan da zan haifa su maimaita rayuwar

wahala irin wadda ni da yanuwana muka yi.

Ba zan yarda hakan ta kasance da ni ba. Ba

zan bari hakan ta kasance da ni ba. So nake

ki kaini garin da zanje in nemi kudi, kudi

nake so inyi irin wanda yayan da zan haifa

ba zasu taba fuskantar rayuwa irin wadda na

fuskanta ba, kudi nake so in yi yadda ni ce

zan zamanto mutum ta karshe a zuri'a ta da

zai san dacin talauci",

Hajiya Kyauta tayi shiru tana kallon yar

yarinyar da take gabanta tana kuma jin

yadda take zarar magana kamar wadda kae

yiwa wahayi. Tace "ke yarinya ce Safiya. Shi

arziki da talauci ai duk na Allah ne shine

kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya. kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya

tace "Allah kuma shine ace mu roke shi zai

amsa mana, zan roke shi ya bani, na kuma

tabbatar zai bani din".

Kyauta tace "to ke yanzu kima da jari ne? Da

me zaki nemi kudin?" Safiya tace "bani da

jari, amma ina da rai na ina kuma da lafiya

ta, da su zan nemi jarj".

Hajiya Kyauta ta sake yin tunani tace "kina

da rai da lafiya amma baki da karfi. Da ke

namiji ce sai in kai ki Kano can ne cibiyar

kasuwanci, sai in kai ki kiyi dako da

laburanci ki samu jari" ta juyo tana kallon

Safiya tace "amma ke macece, yarinyar

mace. Aikatau zan kai ki gidan masu kudi,

Abuja zan kai ki a can masu kudin suke.

Suna bada albashi kuma mai kyau in dai

zakiyi musu aiki mai kyau. Tunda baki da

nauyin kowa kinga zaki tara kudin ki ne

kawai. Daga nan zaki samu jarin da kike

nema" tayi shiru tana cigaba da kallon

Safiya, sai ta sake cewa "gidan Hajiya

Maryam zan kai ki. Yar kasuwa ce sosai

kuma bata da matsala, Zata baki ci da sha

da sutura da magani kuma zata baki albashi,

Sannan zaki koyi dabarun kasuwanci idan

kina zaune da ita, Sai dai akwai yarjejeniya

da zamuyi ni da ke" Safiya ta gyara zama

tace "kome kike so in dai ina da damar yi

miki zanyi mikj" Hajiya Kyauta tace "bana

bukatar ko kwandalar ki, zan taimaka miki ne

saboda girman Allan da kika hada ni da shi.

Amma idan yan uwanki suka kama ki kina

kokarin gudu, ko kuma bayan kinje can suka. ko kuma bayan kinje can suka

gano inda kike, babu sunana a cikin

maganar, bana son shiga cikin rigima".

Safiya tayi murmushin takaici tace "ba zasu

neme ni ba ko sunga bana nan. In sun gano

inda nake ma kuma ba zan dawo ba. In na

bar garin nan na bashi kenan har abada".[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: . EPISODE TWENTY TWO

owner

12:54 AM

Safiyya

Episode Twenty Two: A Green Snake

Bara mu bar Safiya ta huta haka nan......

Let's go back to Fiyya

Naga kunyi missing Malam Muhammadu da

"'Yaya, Yaya, Yaya!"

Naji ana fada ana kuma jijjiga ni. Duk da ban

gane muryar me magana ba amma na san

mutun biyu ne duk duniya suke ce min yaya,

either Hassan ne ko Hussain. Nayi kokarin

bude ido a amma sunyi min nauyi da yawa,

naji ina jin haushin ko ma wanene yake

kokarin tashina, I wanted to go differ into

tunanin Ammi na da yanuwanta, maybe

watakila in nazo gurin da take tafiya ta barni

zata tafi dani wannan karon,

Naji an sake taba ni, wannan karon kuma

muryar macece, muryar Mommy "Safiyya?

Bude idonki ki kalle ni, talk to me" na bude

ido na kamar yadda tace amma dishi dishi

nake ganin ta, na bude baki zanyi mata. nake ganin ta, na bude baki zanyi mata

magana kamar yadda tace amma sai bakin

ya furta "Baba Hadiza" ta kalli wanda yake

kusa da ita? Zaka iya daukan ta, go and look

for someone ko Mustapha" "Mustapha yana

gurin Daddy" ya amsa mata "Daddy " na

maimaita sunan.

Naji an dauke ni, naji kuma an saka ni a

mota, daga nan sai maganganun mutane

mostly muryar Mommy ce tana fada duk da

ban san me take cewa ba.

Sanda na dawo hayyaci na a asibiti na samu

kaina, a kwance akan dago da ruwa a jiki na.

Na kare wa dakin kallo sai naga Daddy a

gefe a zaune akan electric wheelchair dinsa

da dan karamin Alqur'ani a hannunsa. Na

jima ina kallon sa kafin ya fahimci na farko

sai ya rufe qur'anin ya karaso kusa da ni.

"hey there" na kirkiri murmushi "hey"

"ya jikin? Akwai inda yake miki ciwo ne?"

Kusan komai na jikina ciwo yake yi min

amma sai na girgiza kaina nace "babu

komai, Babu abinda yake damuna" yayi

ajiyar zuciya yana kallo na, and once more

na saka gain disappointment a fuskar sa,

Na sunkuyar da ido na kasa, "Doctor ya baki

bedrest amma baki huta din ba ko? You

were supposed to be resting 24/7 amma

shine kika fita" na da go ido na kalle shi sai

na sake mayar wa kasa, ya cigaba "yes,

twins sun gaya min kin fita, kika yaudare su

cewa gurin dinner zaki je, and you ran away. cewa gurin dinner zaki je, and you ran away

daga gurin dinner din suka neme ki suka

rasa. The poor kids have been looking all

over for you. Ina kika je?" Na cigaba da shiru

na "gurin sa kika je ko?" Still shiru.

Ya ja kujerar sa baya "ya Rabb. What should

I do. What should I do ya Rabbi. Safiyya aure

ne akan ki fa yanzu"

Mommy ta bude kofa ta shigo, Esther a

bayan ta da baskets na abinci. Ta kalle shi ta

kalle ni sannan tace "wannan ba lokacin

fada bane ba. Wannan yarinyar da kyar aka

dawo da ita duniyar mu, she called me Baba

Hadiza. Sai kace ta san Baba Hadizan" ya

juyo yana kallo na "Baba Hadiza huh? In ita

take kiran ki tell her ban gama da ke ba. She

took all her kids with her nima ina so ta bar

min tawa" ya karasa yana murmushi.

Mommy ta fara kokarin hada min abinci shi

kuma ya cigaba da magana "Safiya loved

them with everything in her. A lokuta da

dama har kishi nake yi cewa ni bata damu

da ni ba ni da nake da rai kamar yadda ta

damu da su su da basu da rai, And I was

angry at her when she chose death over life,

I thought ta zabi zama da su akan mu ni da

ke. I thought she chose to left us because

she did not love us enough, Sai da na huce

sannan na fahimci gaskiya, she lost

everything sanda ta rasa su, she couldn't

save either of them, and then she got you

and you were her everything, she could save

you so she did. I am sure she didn't even. you so she did. I am sure she didn't even

had a second thought before she jumped

into that water to save you because without

you her life would have been meaningless.

All their lives would have been meaningless.

You are their legacy. You are their dreams"

Na rufe idona ina hango fuskokin su a cikin

hoton da shine kadai abinda na mallaka na

su. Duk da talaucin su but they looked so

contented and happy a cikin hoton.

Mommy ta ajiye farfesun naman da ta zuba

a bowl a gaba na ta fara kokarin tashi na

zaune, na tashi ina rike cikina kamar mai

kokarin hana dinki na budewa. Ta bini da

kallo sannan tayi tsaki "ba kya jin maganar

Fiyya. Ji yadda kika koma dan Allah.

Skeleton ma ya fiki kyan gani. Ba zan kai ki

gidan miji a haka ba wallahi.

16

15

12:56 AM

Sai kin dawo hayyacin ki. Kuma ba zaki dawo

hayyacin naki ba sai kina cin abinci".

Mustapha ya bude kofa ya shigo tare da

sallama, Mommy ta juya kansa "daga ina

kake? Ka barni ina ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login