Showing 375001 words to 375662 words out of 375662 words
Chapter 126 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx
wanda na gani
a Kura faranta min rai, Yayun Baba Hadiza
guda biyu Jabiru da Audu suna garin a
lokacin, Shi Jabiru shekaru ne suka yi
masa yawa and he chose to spend the
last of his days a inda iyayensa suka rasu.
Shi kuma Audu wanda shine Baba Hadiza
take bi ashe tun zagayowar sa garin ta
farko wadda yayi musamman dan kanwar
ta sa sai kuma yazo ya tarar da munanan
labarai a jere, babu Hadiza kanwarsa
babu yayanta. An dai ce babbar
haukacewa tayi ta bi duniya saboda
tashin hankalin abinda ya faru. Wannan
shine last labarin Ammie da yaji. Ya kuma
yi kuka tare da takaici mai yawa akan
hakan dan yana son kanwarsa Hadiza
sosai kasancewar ita kadai ce yar war sa
mace, Daga nan bai kara barin gari ba,
Dagaci ya bashi guri a bayan gari ya kafa
ruga suka zauna shi da iyalinsa yana fatan
watarana Safiya zata dawo kuma zata z0
ta neme su. Lokaci zuwa lokaci ya kan je
Kura ko zal samu labari, amma babu
labar in komai kuma shi bal ma san gurin
wanda zai nemi labarin ba. Bai san kowa
ba sai Alhaji Haladu sai kuma wani kanin
sa. Shima kuma kanin ba'a jima ba ya
rasu.
Daga baya ma sai ya tarar babu gidan
Alhaji Haladu an rushe anyi masallaci. Ya
kan shiga masallacin duk sa da yaje yayi
sallah ya fito amma bai san komai gane da
masallacin ba. Shima ya manyanta, amma
da kwarinsa kuma da yake jikin fulani ne
babu kiba sai ya kasance girman bai kama
shi sosai ba.
Nayi kukan ganin su, kamar yadda suka yi
nawa. Jabiru har sai da na tausaya masa
na koma ni nake bashi hakuri, duk ya
dauki laifin abinda ya samu Baba Hadiza
ya dora akan sa, gani yake laifin sa ne
tunda yazo gari lokacin mutuwar Alhaji
Haladu. Amma ya tafi ya barta da kananan
yara bayan ya san bata da mataimaki sai
Allah,
Sai da aka gana koke koke kuma aka fara
murna. Fulatanci suke yi suma sai hausa
jefi jefi, a lokacin na fahimci fulatanci
dialect daban daban ne dan nasu ya
banbanta sosai da na Muhammad. Suna
gane juna amma ba sosai ba, Sai an dan
hada da hausa wani lokacin kuma sai an
kara bayani, shi kuma sai yayi min bayanin
abinda ban fahimta ba. A haka akayi
communication din. Sai inno matar Audu
ta saka ni a gaba da tsokana wai
maimakon ni zan ke fassarawa mijina
tunda gidan mu aka zo amma shi yake
fassara min. Sai kuma ta tafi wani abu da
ya saka shi murmushi tare da yi min
gwalo. Na harare shi sannan na tambaye
shi abinda tace sai yace cewa tayi ya fi ni
kyau. Ai kuwa na dage nace kishi take yi
tunda ni jika ce a wajen ta tana son ta
kwace min miji.
Sai a fahimci Muhammad yafi sakewa da
su akan a Kura. Nan da nan aka yanka kaji
aka soya mana su aka dama mana kunun
nono, kunun yayi min dadi sosai har sai da
na tambayi Khadija autar Baba Audu ta
koya min yadda ake yi. Muka ci sosai
muka koshi. Muhammad da kansa ya ce
wa dan rakiyar mu ya koma anan zamu
kwana, naji dadin hakan sosai, suma
kuma mun raba dare da su muna hira. Sai
naji nafi sakin jiki da su, na basu labaran
duk abinda ya faru da kuma rasuwar
Ammie na tare da matsayina a yanzu.
Sunyi mamaki sosai sun kuma yi jimami
tare da godiya ga Allah. Sai na basu
labarin Daddy na da halin da yake ciki na
rashin lafiya. Baba Audu yayi shiru sannan
ya tambaye ni abinda yake damunsa, na yi
masa bayanin cutar duk da bansan sunan
ta da hausa ba ballantana da fulatanci. Sai
yace "dan zaku tafi zan bi ku in ganshi.
Zamu warkar da shi da ayar Allah tare da
sauyoyin mu na daji"
Maman Maama✍🏻