Showing 339001 words to 342000 words out of 375662 words

Chapter 114 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7898

Muhammad saboda

baki yan uwansa in sun zo. Na amince da

abinda tace, sai ta hada da kayan

kwalliyar da kayan lefen da aka kawo daga

gidan su Muhammad da kuma kayana da

na hada na gida wadanda zan tafi da su ta

bawa su Salima Hassan ya kai su suka kai

min gidan Muhammad.

Ni dai tunda muka yi maganar kaya da

Mommy ban kuma bin ta kan su ba, sai

dai duk wanda yazo yayi min godiya sai

inyi masa murmushi kawai. Da dare

Muhammad ya dawo kamar yadda yace

zai dawo. Ina tare da Daddy ya kira ni

yace yazo yana waje a mota. Na dan j

faduwar gaba amma na danne na saka

hijab dina na fita. A motar na tarar da shi

a zaune a seat din driver sai na zagaya na

zauna a gefen sa, na gaishe shi yayi shiru

bai amsa ba sai na dago kai muka hada

ido na sake mayar da kaina kasa, ya kira

sunana "Safiyya" na dago kai da sauri dan

ba zan iya tuna ranar da ya kira sunana

haka ba. Sai ya juyo ya kama hannayena duk biyun ya rike "look at me" na sake

dago kai muna kallon juna "me yake

damun ki?" Na dan kirkiri murmushi "ni

kuma? Nothing fa. Kawai abubuwa ne dai

suka dan yi min yawa" ya girgiza kai "ban

yarda ba. Ba zaki fada min ba?" Na sake

mayar da ido na kasa ina jin kamar zanyi

kuka.

"Ba kya son rabuwa da Daddy? Shine

damuwar ki" nayi saurin gyada masa kai

tunda hakan yana cikin damuwata. Yayi

ajiyar zuciya "ba zaki rabu da Daddy ba

kinji? Insha Allah kullum zamu ke zuwa

muna gaishe shi. Nayi miki wannan

alkawarin. Ki saki ranki ki daina damuwa

kinji?" Na sake gyada masa kai sai yace

'to kiyi min hira. I really miss the sound of

your voice " na danyi murmushi nace "to

me zance? Dazu ma ba muni magana

ba" yace "nayi magana dai. Ni kadai nayi

magana ta dazun ma. Kuma na san gobe

ba lallai in samu ganin ki ba. Ko inzo in kai

ku gurin gyaran gashin?" Na girgiza kai

"muna da yawa ai, ba zaka ji dadin shiga

cikin mu ba. Hassan sai ya kaimu ko mu

dauki driver" ya dan yi murmushi "ko dai

kina kishin kar a gane miki miji?" Na

harare shi tare da kwace hannuna in

kishin nake yi ma ai babu laifi

Miji na mai kyau ne kuma ina son sa" yaji

dadi sosai sai ya saka dan yatsa ya dago

haba ta yana kallon cikin ido na for some

seconds sannan yace "kina da kyau sosai

Piya. Ina son ki sosai",. Na danyi murmushi

sai yace "I am glad ba za'a yi taron da

maza ba, yadda kike ta kara kyau din nan

bana so maza su ganki ballantana ace

kinyi kyalliya" na dan yi dariya "ohh and

you are calling me sarkin kishi ko?" Ya

daga kafada "I wasn't complaining ai. Ina

son kishin ki sosai. Yana kara kin

confirming kina so na" nace "to yanzu su

friends din naka babu abinda zaka shirya

musu kenan?" Yace

"kamar kin san da zu

muka gama rigima. Sunce wai ban

gayyace su daurin aure na ba ballantana

in shirya musu reception and I told them

ni ma ba'a gayyaceni daurin auren na wa

ba. Haka suka zauna suka tsuye ni wai

nayi musu karya nace kin mutu" na bude

ido "what! Yaushe kace musu na mutu?"

Yayi dariya "lokacin wancan daurin auren

ne suka dame ni da tambayar ya akayi ba

ke zan aura ba, and su ba su san irin

heartbreak din da nake going through ba

a lokacin, Ni kuma nace musu kin mutu"

dariya nayi sosai sai ya tsaya yana kallona

kawai yana murmushi. Sai kuma naga yayi

sauri ya dauko wata leda a baya ya miko min "Har na kusa mantawa, I bought you

chocolate slurry, irin wadda kike so" na

dan bude ido kadan sannan na bude ledar

na dauko dan karamin cup din ina kallon

sa sannan na kalli Muhammad "a hana ni

sha fa, kai fa kace min in ban daina sha ba

zan zama katuwa" ya dan daga kafada

"yau dai kadai. Daga yau ba zaki kara sha

ba" na bude cup din na dauko dan

karamin spoon din da yake makale a jikin

cup din na diba na saka a bakina ina jin

dadin narkakkiyar chocolate din da aka

chakuda da madara kuma ba'a saka sugar

ba, na kwantar da kaina a jikin motar tare

da lumshe ido na memories din rayuwata

da Muhammad yana dawomin kaina. Na

bude ido naga idon sa yana kaina, na sake

diba da spoon din na kuma sha sai yace

"babu tavi ko?" Ban ce komai ba na dibo a

spoon din na mika zuwa bakinsa. Mai

makon ya sha sai ya kama hannu na ya

dawo da shi baya ya mayar da spoon din

cikin cup din sannan ya saka dogon dan

yatsa na a cikin chocolate din ya

dangwalo sannan ya kai bakin sa, na

lumshe ido ina jin wani irin feeling na

yadda yake yi wa finger din nawa a cikin

bakinsa, nayi kokarin karbe wa amma yaki

saki, sai ya sake mayar da shi ya kuma

dangwalo wa ya sake mayarwa bakin sa,

"hmmm" yace "chocolate din nan akwai dadi fa" ya sake kokarin mayar da yatsan

nawa cikin cup din for the third time sai na

janye cup din, "zaka shanye min ai'" na

fada trying to make him stop, yace "rowa

ko? To shikenan, ki rike taki chocolate din

in rike tawa" ya fada tare da mayar da

hannuna zuwa bakinsa. Sai da yabi

fingers din daya bayan daya kamar wanda

ya samu sweet din gaske, sannan ya juya

hannuna ya manna min kiss a tsakiyar

tafin hannun. Nayi saurin janye hannuna

tare da boye shi a bayana trying to hide

yadda yake saka ni nake ji. Ya sake cewa

"rowa ko?" Na mika masa cup din gaba

daya,

"gashi na bar maka" yace "taki ce

wannan ai, ki bani nawa kawai" na girgiza

kai sai yace "okay to bana son wannan

din, ki sha kayar ki kawaj" na dauki spoon

din na cigaba da sha da sauri da sauri, ina

son in rage wa zuciya ta bugawar da take

yi. Sai da nayi nisa da sha sannan ya

karbe cup din daga hannu na da hannun

sa daya, daya hannun kuma ya kamo

fuska ta ya juyo dani gare shi and

unexpectedly ya hade bakin mu guri daya.

Sanda ya sake ni babu sauran taste din

chocolate a bakina, ya shanye tas, abinda

ya rage min a bakin kawai taste din sa ne,

wanda nake jin sa kamar ba'a iyakacin

bakina kadai ya tsaya ba, kamar dukkan

jijiyoyin jikina ya zagaya. Na bude idanuwa na da suka yi min nauyi na ssuke su a

kansa, har lokacin fuskarsa tana kusa da

tawa, idanun sa a cikin nawa, murmushi

mai fadi akan fuskar ta sa yace "nima na

sha tawa" sannan ya daga min gira yace

"and mine is sweeter" na tura baki tare da

saka hannu ina goge lips dina nace "kai

kazami ne Allah kuwa" ya danyi dariya

"kar ki damu, da sannu zan jaki zuwa

class dina, watakila ma ki fini kwarewa"

na murguda baki ina magana kasa kasa

sannan na

bude kofar motar na fita nace masa "kayi

wa kanka, na fasa yin hirar da kaj" na rufe

kofar sai kuma na sake budewa na dauki

cup din chocolate dina nace

"kuma ba

zan bar maka chocolate dina ba" yayi

murmushi "na sha tawa ai" har zan rufe

kofar sai yace "hey Piya" na tsaya sai

yace "I love you" na danyi murmushi ina

jin har na huce nace "I love you too Baby".

Na rufe masa kofar amma sai ya cigaba

da zama a motar har na shiga cikin gida

sannan ya tafi,

Na danyi kokarin calming kaina down a

compound amma shima da mutane dan

haka na wuce cikin gida, ina shiga sai nayi

sauri na wuce kitchen na wanke fuskata gabaki daya dan duk dankon chocolate

take yi, sai kuma na zauna a kitchen din

na cigaba da shan chocolate dina ina ta

zabga murmushi ni kadai.

Washegari da sassafe muka tashi muka

shirya zamu tafi gurin gyaran gashi, na

shiga yiwa Mommy sallama na tarar har

lokacin rabon kaya take tayi, har zan fita

sai ta kira ni "Safiyya, ni kuwa yaron nan

bai yi miki maganar yadda yake ciki akan

Safina ba?" Na danyi shiru ina kallon ta,

trying so hard kar in nuna bacin rai na, sai

kuma kawai na girgiza mata kai nace "a'a.

Bai ce min komai ba" sai nayi sauri na fita

daga dakin kar ta sake yi min wata

maganar. Ni bana son jin duk wani abu

daya shafi Safina da Muhammad, bai taba

yi min maganar ta ba nima kuma ban taba

tambayar sa ba. Duk wani hukunci da ya

yanke ko zai yanke a kanta abinda ya

shafe su ne bana son shiga ciki kuma

bana son a shigar da ni.

Muka je tare da Salima aka yi mana

gyaran gashi, sannan aka yi min pedicure

da manicure, aka kuma yi min teeth

whitening sannan saloon din suka yi min

massage for free a matsayin wedding gift din su. Daga nan muka dawo gida muka

tarar mai kunshi har tazo, nan da nan na

zauna aka fara rangada min jan lalle,

bayan an gama akayi baki shima amma

kadan as adon jan, sai ya fito yayi kyau

sosai, har yamma bamu gama ba. Tun da

rana kawayena na kano suka karaso, naji

dadin zuwan su sosai dan akwai da yawa

daga cikin su da mukayi shekaru rabon da

muyi magana sai da bikin nan ya tashi na

neme su kuma sai gasu sun zo. Ko dan

nima na san I was quite popular a

makaranta kuma da yawa kawayena suna

sona.

Lokacin yan gidan mu suna ta shirye-

shiryen zuwa gidan su Muhammad wunin

da aka gayyace su, sai a lokacin na lura

ashe tare da garar da akayi min zasu tafi

su kai musu, ni kuma ana gama min na

shiga wanka nayi da special man wankan

da mai gyaran jiki na ta bani, ina fitowa ta

zo ta kuma turarani da turaren ta mai

kamshi da kama dukkan sassan jiki, cikin

sauri na saka rigar da na tanada for

today's occasion sannan nay sallar

magrib din da ake yi a lokacin sannan

muka zauna zaman kwalliya,

Sanda aka gama kwalliyar ni kaina zaman

kallon kaina nayi a gaban madubi, lallai da

gaske Muhammad yake da yace yana murna babu maza a bikin, dan ni kaina sai

nayi kishin nunawa mazan da ba nawa ba

wannan kwalliyar da kyan da nayi. Sai

kuma naji ina son ya gani shi, ba wai a

hoto ba, dan haka na dauki waya na kira

shi "hey baby" duk yammatan gurin suka

juyo suna kallona, nay musu fari da ido

bayan naji ya amsa "kana ina?" Yace "ina

gidan ki. Kin san ni yau nake tarewa. I am

here busy arranging ny things" nace

"zaka iya zuwa nan yanzu?" Ya danyi

shiru "is everything okay?" Nace "komai

lafiya. Nayi kwalliya ne nayi kyau, and I

want you to see me" ya danyi murmushi

mai sauti. "I won't miss this for a thing.

Zan ajiye komai in taho. Sai in kaiki gurin

taron. Ki ce suyi gaba zamu taho tare"

nace "okay, sai kazo" na katse kiran ina

kallon kawayena da suke bina da kallo,

Nan da nan suka kama surutu "ba tun yau

ba na fada, mijin Fiyya zai sha iyayi"

"wannan soyayyar in da ace kina da

kishiya ai sai ta hadiyi zuciya ta mutu" "ni

kam zan so inje gidan ki watarana in ga

yadda za'a ci wannan soyayya " "in dai

mijin bai yi a hankali ba Safiyya will have

him licking at her fingers" na sake juya

idona nace "na nawa kuma? An wuce

wanna gurin ai". Haka suna ji suna gani suka shiga motoci

suka tafi nace ba zan tafi da su ba, Salima

ma data makale sai ta bini wai ai ba'a

barin amarya ita kadai haka na kora ta

nace in dai bata tafi tare da su ba sai dai

ta tafi ita kadai dan ba zata shiga motar

mijina ba. Sauran mutanen gidan ma babu

wanda bai yaba da kyan da nayi ba dan a

lokacin suke dawowa daga event din

gidan su Muhammad hannunsu cike da

abin arziki. Suka yi ta daukan hotuna da ni

har sai da Muhammad yace yazo sannan

twins suka raka ni na fita wajensa.

Bridal gown na saka fara sal, silky material

a ciki mai karamin hannu sai kuma aka

dora lacy material a sama shi kuma da

dogon hannu, aka kuma yi dogon trail

yana jan kasa sosai a baya na. A dai dai

waist din rigar kuma anyi ago da flowers

different colors an zagaye ni da su, sai

kuma gashi na da aka gyara aka zubo min

da shi ta side din kunnen hagu na sannan

ya sauka har kafadar hagun ya kuma

nannade a bayana, Anyi wa gashin ado da

pins masu different colors kamar na

flowers din jikin rigata. Sannan aka lullube

gashin nawa da farin lacy veil, Takalmi da

jakar hannu na duk sunyi matching da flowers din jikin rigata. Ya fito daga motar

yana kallona baki a sake. Daga kallon

kawai a san kwalliya ta biya kudin

sabulu.

[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Sixty Six : Avenged

Not completely edited 😁 I am tired as always.

Tun daga fitar Aunty Hajjo sai na koma

nayi shiru, tun kawayena suna tsokana ta

har suka ga ina neman saka musu kuka

sai suka rabu dani suka cigaba da

hirarrakin su da shewa, suna ta labarin

gida na da yadda komai na gidan yayi

kyau ya kuma da ce da inda aka ajiye shi.

A lokacin naji Farida tana tambayar "ku

wai da gaske wadancan sababbin

motocin da muka gani da bow a jiki gifts

ne aka kawo mata?" Salima tace "eh fa.

Kanin baban sane ya kawo musu ita da

angon as wedding gift" Hasina tace

"gaskiya mutanen nan suna da Naira, Kin

san kuwa tsadar motar nan? Guda biyu

just like that wai wedding gift?" Salima ta

dan tabe baki tace "in dai kudi ne gidan

su suka zo" sai muka hada ido na girgiza

mata kaina, dan ni idan akwai abinda bana

so shine bragging da arziki, in ka sani kawai

ka sani in kuma ba ka sani ba bana

bukatar ka sani sai dai in ta kama dole.

Suna nan dai har suka yi sallar isha' i,

kawayena da suka zo min from outside of

Abuja duk gidan mu zasu koma su sake

kwana sannan washegari su koma gidajen

su. Around 8:30 sai ga kiran Muhammad,

ban dauka ba sai na mika wa Salima, a

zuciya ta ina tuna cewa tun safe rabon da

inji muryar sa, da ta dauka sai naga tana

murmushi tana kallona sannan tace "ba

ita ba ce ba. Salima ce. Kunya take ji wai

ba zata dauki wayar ba" sai kuma tayi

dariya, sannan tace "okay, gamu nan

zuwa" ta miko min tana murmushi "yace

suna first floor, mu sauka mu same su".

Muka tashi gabaki daya, suka sake gyara

min laffaya ta suka rufe min koina har kafa

ta, sannan suka kara min turare suka

kama hannu na muka sauka zuwa falon da

yake a hawa na biyu. Ni dai jana kawai

suke har suka kaini kan kujera suka ajiye

ni. Sai da na zauna sannan na fahimci a

kusa da mutum aka zaunar da ni. Sai

kuma naji muryar Ya Amen yana amsa

gaisuwar da kawayena suke yi musu, tare

da muryar wasu mazan amma kamar basu

da yawa ba zasu fi su uku ko hudu ba.

Daga nan kuma aka gabatar da addu'a

aka shafa sannan Farida kawata tun

primary school sarkin surutu ta fara zuba,

har da yin speech akan wai sun bawa

Muhammad amana ta, sai tazo ta kama

hannuna ta dora akan nasa tana lissafa

masa irin kyawawan halaye na, ta kara da

cewa "amma fa sai kayi hakuri, akwai iyayi

da taurin kai" ina jin Muhammad yana

dariya. Sai kuma Usman abokin sa shima

ya gode wa kawayena for hidimar da suka

sha a lokacin bikin, ya kuma koda abokin

na su da lissafa irin kyawawan halayen sa

shima, sannan ya tabbatar wa da

kawayena cewa abokin su zai rike amanar

da suka bashi.

Daga nan kuma sai aka fara cinikin

fuskata, kawayena suka dan ware gefe

daya suka yi meeting sannan suka yanki

kudi mai tsoka suka fada, abokan ango

suka fara jayayya, sun jima suna to and

fro sannan suka daidaita akan price din da

kawayen suka ki sauka daga kansa, daga

nan abokai suka ce a bayar da account

details din da za'a basu kudin, suka fadi

account aka tura musu, sai da kudin ya

shiga sannan naji kawayena sun hau

shewa da hun murna, kudin da aka basu

har yafi wanda suka tambaya da farko.

Daga nan Salima tazo zata bude fuska ta

ango ya hana, kiri kiri yace babu wanda

zai ga fuska ta a cikin abokansa a ranar, ai

kuwa nan rigima ta kaure tsakanin sa da

su, suka yi masa gorin dama babu abinda

ya shirya musu a bikin nasa, kuma fuskar

amaryar ma yanzu ya hana su gani. Anan

na jawo shi na rada masa cewa ya gaya

musu ina gayyatar su cin taliyar amarya

nan da kwana uku, amma da Muhammad

ya tashi fada sai yace next week.

Haka dai aka gama komai cikin raha da

walwala sannan suka tashi suka yi min

sallama suka tafi, duk wadda ta leka

fuskata sai inji kamar in rike ta in hana ta

tafiya amma ina ji ina gani suka tafi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login