Showing 327001 words to 330000 words out of 375662 words

Chapter 110 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7955

agogo, nayi sauri na bude ido.

"shikenan zaka saka gobe in tashi da

kumburarrun idanu. Go and sleep Mr

Man" yace "duk wanda yace miki me yasa

baki yi bacci da daddare ba ki ce masa

nine na hana ki yin baccin, in kika ce haka

zasu kawo ki da wuri" nayi murmushi

kawai "good night" yace "sai dai good

morning kuma yanzu ai. But just one more

thing please, Tambaya ce da n'" nace "Allah yasa na sani" yace "Akwai abinda ya damyi confusion dina, lissafina bai tafi dai dai ba gaskiya, dazu ma muna

maganar da Mama sai naga kamar ta

share maganar bata son y" na danyi shiru

ina jin sa ina tunanin wanne lissafi ne, sai

yace "date din da kika gaya min uncle

Ahmad ya kawo sakon takardar nan. Har

zuwa yanzu a lissafina ba'a yi wata biyu

ba ma ballantana uku. I thought sai kinyi

wata uku tukunna or somewhere close to

that. I know you and Daddy all have the

Islamic knowledge concerning that so

dole akwai explanation" yayi shiru nima

nayi, na gane abinda yake nufi na kuma yi

realizing yadda yake avoiding mentioning

sunan Mukhtar.

Jin nayi shiru sai ya sake cewa "kin gane

abinda nake nufi? I just want to know

why" direct na bashi amsa "saboda banyi

masa idda ba. Babu iddar sa a kaina" ya

danyi shiru kamar bai ji me nace ba amma

na san yaji, sanda yayi magana naji relief

mai yawa a tare da muryar sa "and hakan

yana nufin me kenan?" Nace "ni ma ban

sani ba. Sai dai a tambayo" yace "wa za'a

tambaya? Bayan gaki nan ina tambayar ki

Kawai ki fada min abinda hakan yake nufi

n ban sani ba" nace "to ni ma ban sani ba, Good night" yace "zaki fada ne, Zaki yi min dogon bayani ne in details…..." Na katse shi "good night" sai na katse kiran na ajiye wayar ina murmushi duk kuwa da

cewa kaina yayi min nauyi sosai saboda

baccin da yake cikin sa.

Sai bayan da nayi sallar asuba sannan

nayi bacci mai nauyi, ban tashi ba sai

around 12 shima kuma dan ina son inje

inga Daddy ne tunda jiya ma ban samu

ganin shi da daddare ba. Da sauri nayi

wanka na shirya cikin doguwar rigar

atampa na fito as usual banyi kwalliya ba,

ina fitowa Esther ta shiga ta fara hidimar

gyaran dakin dama jiya duk na hargitsa

closet din.

Dakin Daddy na wuce direct, na tarar da

shi tare da uncle Ahmad suna magana,

ina shiga suka juyo suna kallona suna

murmushi "amarya" uncle Ahmad ya fada,

nayi kamar zan koma da baya dan kunya,

sai Daddy ya miko min hannunsa "come

here" na karasa na saka hannuna cikin

nashi sannan na zauna a kusa dashi tare

da gaishe shi, ya amsa na gaishe da uncle

Ahmad shima ya amsa tare da cewa "ya

shirye shire?" Sai nayi kamar banji ba sai

yace "umman ku zata shigo in anjima ai,

Salima zata zo itama kuyi magana. Duk

abinda kuke bukata sai kuyi magana kinji? Ko ba zaki fada min ba ki fada wa Salima

sal ta gaya min" a gyada kai idona a

kasa, Daddy ya dan matsa hannuna a

cikin nasa na dago ido na kalle shi sai

yace "kin shiga gurin Sa'adatu?" Na

girgiza kai "yanxu na tashi, na fara zuwa

wajen ka ne amma yanzu zanje wajenta"

ya gyada kai "alright ki shiga. And be nice

to her" nace "to" har zan tashi kuma sai

na sake cewa "Daddy kunyi magana da

Hajiya? Ta sani?" Yace "eh, I told her tun

kafin a daura. And I will call her yanzu in

gaya mata an daura din, jiya na manta ne"

uncle Ahmad yace "kar ka dora wa kanka

laifi yaya, ai ba kai ya kamata ka gaya

mata ba, Sa'adatu ce zata gaya mata" ni

dai sai ya zame hannu na na tashi, ina jin

Daddy kamar kar ya saki hannun nawa,

sai naji zuciya ta wani iri, he is already

missing me.

Har na kai bakin kofa kuma sai uncle

Ahmad ya sake kira na, na juyo sai ya

nuna min gurin zama dan haka na dawo

na zauna sai yace "na manta ba muyi

maganar ba. Akwai kayanki na gidan

Mukhtar, naje na gansu an hada komai a

waje daya, na saka yau za'a kwaso su a

kawo su nan gidan, ban sani ba ko akwai

abinda zaki yi amfani da shi a ciki.

Kayan sakawar ki da kika bari a can ma na

saka Salima ta hado miki su, tare da lefen

ki ashe duk baki yi amfani da komai ba, in

anjima in zasu zo zasu taho miki da su",

Na danyi ajiyar zuciya sai kjma naga

kamar ni duke jira suji abinda zance,

Daddy zainiya fadar abinda za'a yi ko ya

gaya min abinda zanyi amma Daddy baya

min haka, baya taba yanke min hukunci

sai dai ya tambaye ni abinda nake tunani

in na fadi abinda ya san ba dai dai bane

ba sai ya gyara min zuwa abinda yake dai

dai ta hanyar bani shawara.

"Ni sam ban saka lissafi da su ba. Banyi

tunanin komai a kansu ba. Abubuwa da

yawa ba'a taba using ba except for kujeru

da aka dan zauna akai. I don't know ko

za'a ajiye wa Salima tunda babu abinda

zasuyi har Allah ya kaimu bikinta. In ma

kuma bata son colours din ko design din

za'a iya siyarwa a siya mata wasu"

Uncle Ahmad ya fara girgiza kai, "kayan

masu tsada ne sosai, abubuwa da yawa

ba sai an sake siya miki ba. Kayan suna da

yawa sosai" ya yi ta fada irin ka rasa abin

cewa din nan. Ni kaina na san kayan masu

tsada ne dan sanda Mommy tayi order din

su sai da na jinjina kudin amma tace su

suka fi dacewa da ni. But there is trauma attached to them and I cannot use them.

Kuma wanna kyautar ina ganin zata kara

bonding zumuncin da ya fara samun

baraka tsakanin mu. Daddy yana

murmushi yace "kai da ba kai aka bawa

ba ina ruwanka? Kanwarta ta bawa ai" jin

hakan sai nasan yayi accepting decision

din nawa, na sake mikewa sai uncle

Ahmad ya sake cewa "at least ki karbi

kayan lefen to. Ni na siya dama ai ba shi

ya siya ba, sai ki kara akan dinkunan da

zaki yi na zuwa can gidan" na gyada kaina

nace "zan karba, Thank you Uncle" na

fada dan bana son inyi jayayya da shi kar

ya dauka wani abun ne daban.

Dakin Mommy na wuce duk kuwa da

yadda Esther take bina da cup din coffee

a hannun ta, bata falon ta, babu kowa a

falon dan haka na wuce bedroom din ta

ina fatan kar mu hadu da Safina a can.

Nayi knocking na tura kofa tare da

sallama ina jin yadda gaba na yaje

faduwa, ina cherishing relationship dina

da Mommy sosai ina kuma kokarin

avoiding abinda zai lalata shi. Tana

kwance akan gadon ta amma idonta biyu,

ta dan juyo ta kalle ni sannan ta mayar da

kanta ta kwantar, na zagaya ta side din da

fuskarta take na zauna akan carpet nace

"good morning mommy" ta bini da kallo

tare da dan motsa bakinta kadan ba tare

da naji abinda tace min ba, Banji dadin yanayin fuskar ta ba dan idanunta sun

nuna bayan kukan da tayi jiya bata yi

cikakken bacci ba. Na cigaba da zama a

gabanta amma bata ce min komai ba har

wajen mintuna goma, ina so muyi magana

dan haka nace "I am sorry Mommy" a

hankali tace "for what? What are you

sorry for?" Na danyi shiru ina tunani,

menene abinda nayi wa Mommy ne? Sai

kawai nace "I am sorry for whatever I did

that made you cry" ta dafa gadon ta mike

zaune tare da jingina bayan ta da

headboard. Tana kallona tace "tell me

something Safiyya. Tunda Allah ya hada ni

da ke akwai abinda na taba yi miki that

made you feel I am not your mother?" Na

danyi tunani kadan, I can mention a few

things but I didn't, sai na girgiza kaina

"babu" ta cigaba "but you still think I am

not good enough to be your mother ko?

Ke ma irin ta mahaifin ki ne ko? Kullum

kina tunanin zan cutar da ke ne ko? Kina

kallona a matsayin kishiyar uwa, bayan

kuma da ace Safiya tana da rai da ba zan

taba zuwa gidan nan ba" na girgiza kai

"ko tana da rai Mommy dole zaki zo ai.

Twins kuma fa?" Tayi shiru tana kallona

"you are always smart, with your words

with your actions and with your choices.

You have no idea how much hard it was to

raise you, especially with idanun babanki

da ko kallon banza aka yi miki sai ya chanja fuska, especially with idanun

mutane akai suga me zanyi, Wannan ba

yar ta bace ba wadancan ne yayanta.

Kuma bana taba yin dal dai. Adam will

criticize, Ahmad will criticize, Hajiya will

always have something to say. But I did

my best, Through it all I did my best. Idan

ku baku gani ba Allah ya gani ai. Ban taba

cutar da ke ba kuma ba zan fara daga yau

ba. Yes naso Mustapha ya aure ki amma

ban tura shi yaje ya ci zarafin ki ba. 12 1d AM

Tabbas ina son Safina amma ba zan goyi

bayan ta rabaki da saurayin ki ta aure shi

ba. Ni bana son yaron ma. Har yanzu ma

da kike matsayin matarsa still bana son

sa. Ban sani ba ko nan gaba zaiyi abinda

zai saka in so shi. Amma ina so daga ke

har Adam ku sani cewa it hurts so much

that you do not trust me after all these

years, that you treat me like an outsider

ba wai uwa ba da ya kamata ace ta fi

kowa kusanci da ku, ba zaku bude baku

ku gaya min magana kuyi min bayani ba."

Ta karasa hawaye yana bin fuskarta. Naji

zuciya ta ta kara karyewa, na tashi na

zauna a bakin gadon nace "kiyi hakuri

Mommy, dan Allah ki daina kuka. I am

sorry, I never meant to hurt you wallahi

ban so na saka ki kuka. Ke kadai ce

uwata, ke kadai na sani uwata kuma ke

zaki cigaba da zama uwata. Dan Allah ki

yale min" ta girgiza kanta "there is nothing to forgive ai. Kawai yana yin

tunanin ki akaina nake so ki gyara. In ma

da akwai na yafe miki. Allah ya ji kan

Safiya" nace "Amen. Nagode Mommy"

sai kuma na zagaye ta da hannayena na

rungume ta ina jin wani iri a raina. Nayi

missing our hugs and kisses. Nayi missing

yadda muke zama muyi hira muyi wasa da

dariya. Nayi missing dinta. Ta zagaye ni

da hannayenta ita ma sannan ta dan buga

bayana kadan sai kuma ta sake ni.

Na tashi na fita daga dakin ina jin nauyin

zuciyata ya dan ragu akan issue din. Ina

gama breakfast a kasa su Umma suna

zuwa tare da Salima da uban lodin

kayana, kayan sakawa ta da kuma

akwatinan lefe na da har yau Allah bai

bani ikon bude su na ga menene a ciki ba.

Aka shigar da su wani daki a ka ajiye su.

Sai a lokacin Mommy ta sauko still kana

ganin ta ka san tana cikin damuwa. Suka

gaisa sama sama da Umma, a raina ina ta

addu'ar kar Umma ta ce zata gaya mata

magana kuma sai naga bata yi din ba.

Daga nan Umma tace uncle Ahmad yace

suyi maganar shire shiryen tariya ta,

amma already Daddy yace baya son biki,

baya son duk wani abu da zai jawo

attention din mutane, nima dama banyi

lissatin yin biki ba, Ina dai tunanin shirya

walima for my friends da sukayi ta mitar na watsar da su tun lokacin wancan bikin,

Nan na gaya musu cewa ni walima kawai

dan shirya for my friends, Umma tace to

suna nasu Mutanen sai su zo walimar

kawai, a take Salima tace ba zai yiwu a

kawo mana tsofaffi cikin walimar mu ba,

suna ta musun su sai ga Aunty Hajjo nan

tazo itama. Na gaishe ta nan take ta shige

cikin maganar itama, ita ta goya wa

Salima baya. "A'a ba zaku shiga walimar

su ba. Kinga Salima, ku chanja wa event

din naku suna daga walima zuwa wani

sunan da zai nuna na yammata ne kawai,

in ba haka ba har da kakanni sai kun

ganj"

Ni dai ban ce musu komai ba. Mommy ma

few words kawai take dan sakawa dan

hankalin ta gabaki daya kamar baya gurin

kawai a zaune take. And I asked myself

again ina Safina take? Ko dai ta koma

gidan Muhammad ne?

Ban samu amsar ba sai da na tafi daki yin

sallar na hadu da Esther sai na tambaye ta

ko taga Safina a gidan? Sai tace "ya da

dare bayan kin taho daki Mustapha yazo

ya dauke ta. Na gyada kai, maybe gidan

Hajiya ta tafi ita ma, Ina yin sallar

maimakon in koma kasa sal na dauki waya

la na kira Muhammad muka sha hira, ya gaya min wai already har sunje da Abba kamfanin da zasu vi musu

Renovating gidan, har sun zabi plan, "kamfanin su Ya

Amen ne fa, they are into construction,

Dama su suka gina gidan tun farko, yanzu

ma kuma su zasu yi aiki a kansa" da ya

fara tsara min yadda suke so ayi wa gidan

sai da naji kana yana neman bugawa "ni

fa ba gane wa nake yi ba wallahi. Ka

barshi kawai in an gama naje sai in gani"

ya dan mararaice "inzo in dauke ki yanzu

muje in nuna miki?" na danyi dariya "me

zaka nuna min tunda ba'a fara komai ba?"

Ya danyi shiru "yeah, right. To wani abu

zan nuna miki daban. Wani abu ne da

nasan kina son gani" nace "dauki hoton

sa a waya ka turo min" yace "it is too big,

ba zai dauku a waya ba. Please inzo

muje?" Nace "ko kazo ma ba zan fito ba.

Wallahi gidan mu a cike yake da iyaye na.

Ba zan wuce su in tafi gurin a ba" yace

"ni fa mijin ki ne.

Maganar wa zaki ji? Tawa ko tasu?" Yadda

ya fadi maganar da authority ya sa na

mararaice "Please Baby, dan ni suka zo

gidan fa, Kuma kawai sai in bika mu fice

mu bar gidan?" Ina maganar Salima ta

bude kofa ta shigo tace min "Fiyya ki zo

ga Hajiya nan tazo" nayi mata alamar ina

zuwa sannan nace masa "kaji ko?" Ya

danyi shiru sannan yace "Hajiya

Maryama?" Nace "yes ita" yayi ajiyar zuciya "hey Piya! How are you coping? I

mean ya kuke ciki da Mommy and her

children?" Na sauke ajjiyar zuciya ina jin

dadin concern dinsa nace "yanzu dai

zanje gurin Hajiya. We will talk about it

later insha Allah" yace "okay. Just take

care of yourself kinji? Kar ki bar komai ya

bata min ranki. And ....... Zan shigo in an

jima da dare idan sun tafi. Kuma babu

zama a falo with the cctv thingy" nayi

dariya "okay. Bye Baby. Love you "

Da sauri na sauka kasa, ban san yadda

Hajiya zata dauki maganar ba kuma tana

daga cikin mutane masu muhimmanci a

rayuwa ta wadanda no matter the

situation ba zan so mu samu sabani ba.

Tana zaune a kan carpet ta mike kafarta,

na sauko reluctantly ina tunanin abinda

zata ce min sai cewa tayi "ina akwatin

kayan ki? Nace wa adamu fa ya gaya miki

ki hada kayan ki tare zamu tafi, wannan

karon ni zanyi gyaran amarya" Aunty Hajjo

tayi saurin cewa "a'a fa. Wannan aikin ai

na iyayen amarya ne ba kakanni ba. Ke dai

zaki iya kawo gudummawar abinda kika

tara" na dan saki raina kadan tare da

karaso wa nace "Adam, Hajiya, ba Adamu

ba" ta jeho min throw pillown da yake

kusa da ita "jaira, Adamu zan ce ba zance

Adam din ba" nace "already ai kin fada". Aka sake yin dariya,

Daga nan suka cigaba da lissafe lissaten

su yayin da ni kuma muka ware da Salima

muke namu. Decisions din mu na kayan

da zan saka ne a event guda daya da

nace zanyi sai kuma na kai amarya. Amma

kuma dai bamu sani ba ko gidan su

Muhammad zasu shirya wani abu. Karshe

dai muka ce zanyi dinkuna na fitar biki set

biyar in case, sai kuma sauran dinkunan

da zanyi. A take na dauko system dina

muka fara neman material, shiga can fita

can da kyar muka samu guda biyu da

suka yi mana, to matsalar kowanne sai an

nemi abun da za'a hada shi da shi. A

karshe dai kawai muka yanke shawarar

neman fashion designer da zata yi mana

komai. A karshe dai Salima kin bin Umma

tayi tace a waje na zata zauna "akwai

abubuwa da yawa da zamuyi kuma bamu

da lokaci" Umma tace "au har kun saka

ranar ne mu bamu sani ba?" Sai akayi

dariya kawal.

Da daddare Muhammad yazo kamar

yadda yace, na san da zuwan na sa dama

dan haka naje nayi wanka na shirya cikin

riga da skirt na atampa na gyara gashina

nayi daurin dankwali mai kyau. Dinkin ya

zsuna das a jikina, na shafa turaruka na

masu dadin kamshi, Salima tana ta

tsokana ta wai sai ta raka ni ta gaya masa ita ta shirya ni ko zai dan miko mata wani

abu. Ban samu lokacin yi masa girki ba

amma na saka Esther tayi masa kuma na

san zata fitar da ni kunya. Amma mutumin

nan yana zuwa sai yayi zaman sa a mota

sannan ya kira ni "ina waje a mota" nace

"waje kuma? Ka shigo mana ga ...." "Not a

chance. Ki same ni a mota" ya katse

kiran.

Na sauke wayar daga kunnena ina hararar

ta. "Kinji


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login