Showing 210001 words to 213000 words out of 375662 words

Chapter 71 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7943

/>
min. She threatened me. Scissors fa ta dauko tace zata yi min illa, kuna jin ta fa a cikin maganganun. I told her what she want to hear dan kar ta illata ni. Amma

karya take yi min Abba. Ni ban san komai

akan abinda ya faru da ita ba. Dan Allah

Abba ka yarda da ni".

Na rufe ido na ina jin zuciya ta tana

tafasa, na bude na kalli Daddy naga yana

zaune ya dafe kansa sai maimaita salati

yake yi shi ya kasa ma magana. Na sake

kallon Mukhtar naga yadda ya dage yana

ta jera wa iyayensa karya da fatan lallai sai

sun yarda da shi. Sai naji Abba yace "biri dai kam yayi kama da mutum. Idan har abinda ya faru da ita

kenan da tuntuni me yasa ba ta fada ba

tun a lokacin sai yanzu tukunna? Me yasa

ba ta ce tana zargin sa ba sai ta amince ta

aure shi dan ta makala masa wannan

sharrin? Me yasa da farko da yace yana

son ta ta ki shi sai daga baya kuma da

kanta tace tana son auren sa, ya kamata

mu duba wannan maganar, Yaya ya

kamata muyi dogon bincike kafin mu

yanke hukunci",

Mommy tace "amma me yasa yayi karya?

In yana da gaskiya me yasa yace bai ma

san sanda ta bar gidan ba bayan gashi munji sai da suka yi maganganu kafin ta fita?"

Suka cigaba da maganganun su yayin da

ni kuma na kwantar da kaina kawai akan

kujera ina jin su, na fahimci iyayen

Mukhtar gabaki daya kokari suke yi sai

sun kare dan su sun ce sharri nayi masa,

ni kuma nawa ban ya kasa cewa ma

komai saboda rashin lafiya sai fuskar sa

da take nuna tsananin damuwa, sai

Mommy ce kawai bakin ta yaki yin shiru

sai kokarin mayar wa da su uncle Ahmad

maganganun su take yi. Na bude ido na

ina kallon su, a raina nace plan C it is.

Sai na jawo jakata ba tare da sun lura ba

na dauki scissor dina na boye a cikin hijab

dina na mike tsaye na fara magana. "okay

shikenan. Yanzu kunce sharri nayi masa.

Gashi kunji da bakinsa ya fada amma

Umma tace "me muka ji ya fada? Dauko

wayar ki sake kunnawa. Ni dai banji inda

ya amsa yayi wanna mummunan abun

ba" nace "ba zaku yarda ba dama. Ni na

san ba zaku yarda ba. Wai kuma a haka

Daddy yana da rai kenan. Idan babu shi

kuma fa? Me zai faru idan babu shi?"

Uncle Ahmad ya mike a zuciye "ke

Safiyya ki shiga hankalin ki, kar ki gaya

mana maganar banza. An gaya miki kudi

hauka ne da zaki saka mu a gaba kina daga mana murya da maganar banza alhalin mu iyayen kine?",

Na girgiza kaina ina jin hawaye yana bin

fuskata "maganar banza. Maganar banza

kake cewa uncle" na juya ina kallon

Mukhtar da dacin rai nace "you took

everything from me. Duk abinda na

mallaka, duk abinda nake takama da shi

sai da ka raba ni da shi, mutunci na a

matsayi na na ya mace, daraja ta a cikin

al'umma, soyayya da amincin iyayena, my

confidence, my good image, saurayina xa

nake so fiye da komai sai da ka raba ni da

shi saboda abinda kayi min, you almost

took my sanity dan sai da na kusa

zaucewa saboda bakin cikin abinda kavi

min and I promised you tun a lokacin

kuma yanzu ma a gaban iyayen mu ina

maimaita maka, i will take away

everything from you too ko da kuwa duk

abinda na mallaka zai kare akan hakan.

Bayan na gama nawa kuma I will make

sure you get the highest sentence da za'a

¡ya yiwa rapist a Nigeria".

Gaba daya duk sunyi shiru suna kallo na,

ni kaina ban san cewa da karfi nake

maganar ba sai da nayi shiru. Hawaye ne

kawai yake bin fuskata ina zagaye su, Sai

na saka hannu na share hawayen fuskata

a dai dai lokacin da na tsaya a saman kan

Mukhtar da yake zaune a kasa a gaban mu.

Ba tare da sun lura da abinda yake faruwa

ba kawai sai na durkusa na damki gashin

kan Mukhtar na yanka da almakashin

hannuna, making sure na dan yanke shi

kadan. Ya zabura saboda zafi ni kuma na

mike da gashin sa a hannuna. Na nuna

masa almakashin hannuna nace "I told

you zanyi amfani da shi dama. Ga abinda

zan yanka nan" na koma inda na ajiye

jakata na bude na dauko ledar da na ajiye

a ciki ta ziplock na saka gashin a ciki

sannan na ajiye ta a tsakanin uncle

Ahmad da Daddy nace "zan kawo muku

na yaron da na haifa. Run a DNA test ku

gani idan ba nashi bane ba. Idan kunyi

baku yarda ba ku sake asibiti ku sake yi

and I assure you ko sau dari zakuyi zaku

ga 100% compatibility. Dan sa ne".

Mukhtar ya mike yana kallona, daga

dukkan alama maganar da da nayi ta

mantar da shi zafin yankar sa da nayi,

yace cikin kidimewa "you told me he is

dead" na daga kafada "I lied" na koma na

zauna, Daddy yayi magana murya can

kasa "wanne irin dead kuma? Yaushe?

Jiya mana ganshi on a video call". Mukhtar ya zame saura kadan ya fadi sai ya zauna akan kujera tare da dafe kansa, cikin karyewar zuciya ya sake cewa "you

told me he is dead" na sake maimaita wa

nima "I lied", Daddy ya saka hannu ya

dauki gashin Mukhtar da na ajiye a gaban

su, sannan ya dago kai yana kallon

Mukhtar din fuskar sa cike da emotions

da ba zan iya kwatantawa ba yace "idan

har ta tabbata kaine Mukhtar. Idan har ta

tabbata kaine, wallahi, wallahi, sai na

tabbatar da cewa kayi nadamar zuwa duniya".

Ya zame daga kan kujerar da yake kai ya

sauko kasa, in ka ganshi zaka dauka

sanarwar cewa Umma ta mutu aka kawo

masa. Ya bude baki ya kai sau biyar amma

ya kasa furta komai. A karshe sai yace

"Daddy..... Abba ..... Dan Allah.…”

Na mike ina kallon sa nace "I will see you

in court" har zan fita kuma sai na juyo na

nuna uncle Ahmad nace "kai kuma ka

dawo min da kudin da ka sata nan da one

week ko kuma ka kawo min resignationletter din ka".

Na juya na fita, Yes, I know that last part

was petty and uncalled for but I didn't

care. I was beyond caring.

Maman Maama✍🏻

[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty Four : Betrayed

Not edited….

Dakina na koma da sauri kamar wadda

ake hankada, ni raina a matukar bace. Yes

na san dama iyaye suna son yayansu and

it is only natural for iyaye to choose yayan

su over every one else, but that should be

on something not as serious as this.

Sanda abin ya faru da ni musamman

sanda maganar cikina ta bayyana every

hand was pointing toward me akan abinda

ni nasan bani da laifi akai amma babu

wanda ya yarda da ni, to me yasa yanzu

ba zasu juya hannun su nuna wanda yake

da laifin ba sai suke neman shield din da

zasu kare shi da shi? Me yasa ni lokaci

daya aka yarda nayi laifin amma shi ba

za'a yarda yayi ba?

But they are all in for a surprise.

Zasu sha mamaki na ba kadan ba.

Dan tabbas Mukhtar sai ya girbi abinda ya shuka sai dai in lahira zasu kai shi su boye shi. In can din ma suka kaishi walakiri yana can yana jiran shi, dan ban yafe masa ba kuma ba zan taba yafe masa ba.

Na shiga dakin na koma na zauna akan

kujerar da na tashi daga kanta ina mayar

da numfashi. Babu wanda zai fahimci

abinda nake ji a zuciya ta sai wanda ya

taba shiga cikin irin halin da nake ciki.

Babu kuwa wanda nake yiwa fatan ya

shiga irin halin da na shiga a rayuwata. Na

sha wahala. Na wahala ba kadan ba. The

pain and trauma of the rape was the

easiest part, sharrin shaye shaye da

Mustapha yayi min, kin yarda da ni da

Daddy yayi da kuma yadda maganar ta

fara kokarin juye wa zuwa kan

Muhammad duk ba sune worst abinda ya

fi bakanta min ba. My life got totally

destroyed lokacin da na fahimci ina da ciki.

. . . . .

11 months ago

Immediately after the night to

remember…..

Ba makaranta ba, a Abuja ma Daddy bai

barni ba ya dauke ni muka koma Kano tare, a lokacin babban tashin hankali na

shine Muhammad, na san yana can cikin

damuwa akan bacewar da nayi na barshi a

ranar da na saka masa rai na kuma yi

masa alkawarin zan kaishi wajen

mahaifina. I tried calling him amma sai na

kasa saboda babu abinda na wuni a ranar

ina yi sai kuka, muryata har dashewa tayi,

kuma yadda muke da fahimtar juna ni da

shi na tabbatar yana jin murya ta zai san

wani abu ya faru da ni, ni ma kuma na san

ina jin muryarsa zan sake wani kukan dan

it will remind me of all the love and the

promises da muka yi wa junan mu. Dan

haka sai na tura masa text, na gaya masa

cewa bayan ya fita aka kira ni cewa Daddy

sun zo amma jikin sa ya tashi, shi yasa na

tafi na barshi dan hankali na ya tashi. And

I forgot my phone in the car shi yasa ban

dauki kiran sa ba. Nace masa kuma da

muka kwana a asilitin jikin baiyi dadi ba

sai muka sake fita dashi da ga kasar, shi

yasa ba zai same ni a waya ba ko ya kira.

Daga nan na rufe dukkan sims dina yadda

ko ya kira ba zai samu ba. But I cried after

that, just the thought of him yana kara

sakani bakin ciki da bacin rai. Tun a

lokacin naji na fara tunanin rabuwa da shi.

A ganina bai yi deserving a used rug like

me ba, Tun kafin muje kano Mommy ta samu

labarin wai na zo gida a buge kuma

bincike ya nuna cewa saurayi ne yaje makarantar mu ya dauke ni ya fita da ni. Na kuma san wanda ya bata labarin....

Abinda ta fara saka ni a gaba da tambaya

muna zuwa gida shine waye saurayin

nawa?

"'Wanda kika ce zai zo gurin Daddyn ku

ne? Dama ba mutumin kirki ba ne ba

Safiyya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun,

abinda kika zama kenan Safiyya?"

And then…..

"Na gaya maka dama baban Mustapha,

yarinyar nan aure za'a yi mata kaki yarda.

Tun da ta nuna auren ta ke so to ai auren

ya kamata ayi mata. Ga Mustapha nan

yace yana son ta amma daga kai har ita

kun nuna ba kwa son abin. Gashi nan ai ta

fara kula wadanda ba mutanen kirki ba.

Bayan ga wannan wanda kai kayi tarbiyyar

sa da kan ka". Naji kamar zuciyata zata kama da wuta,

Wata irin tsanar Mustapha tana kara shiga

ta. A zuciya ta ina kara tabbatar wa da kaina

cewa shi ya aikata min wannan aika aikan dan ya cimma burinsa, dama ya jima yana

nema ya ga tabbas ba zai sa mu ba, ya

shigo da maganar aure ba dam yana so

na da gaske ba sai dan kudin da yaji an

ambata a matsayin nawa, shima kuma ya

ga babu nasara ta wannan bangaren shi

yasa yayi min wannan abun, sannan kuma

ya kala min sharrin shaye shaye, dan a

matsamin dole in aure shi shikenan ya

samu riba biyu. Ni kuma tun a lokacin nayi

rantsuwa a raina cewa ko mazan duniya

zasu kare ba zan aure shi ba. Na kuma

rantsuwa cewa sai na tona mass asiri.

Amma kafin in tona masa asirin ai dole sai

na bayar da labarin abinda ya faru da ni

sannan in shigar da maganar wanda nake

zargi. Amma kuma maganar tayi min

nauyi da yawa a bakina, a zuciya ta. A

cikin first few weeks da faruwar abin na

gwada bude bakina in fada yafi sau a

kirga amma sai dai in mayar da bakin in

rufe ba tare da na fada din ba saboda

maganar taki fitowa, Magan6ce da bazan

iya yin ta da Daddy ba duk kuwa da

shakuwar da take tsakanin mu, ita kuma

Mommy da ya kamata inyi maganar da ita

dan ta nake zargi da aikata min wannan

abun dan haka ita ma sai ma kasa bude

bakina in gaya mata,

Sai dai kuma tun da abin ya faru sai na rasa lafiya. Farko tsananin

ciwon jikin da ma dangantashi da abinda

ya faru, sai kuma ciwon kan da nayi

tunanin tashin hankali ne da bakin ciki ya

saka min shi, daga nan bayan sati biyu sai

abin ya wuce ya zama zazzabi. Mommy ta

kaini asibiti suka yi min gwaje gwaje suka

bani magunguna har da su karin ruwa,

kwana na biyu aka sallame ni na dawo

gida na fara pretending kamar na warke

saboda yadda nake tsoron allura, amma

kuma sam ban warke ba din, tun ina boye

ciwon har na kasa na cigaba da bayyana

shi aka sake mayar da ni asibiti, suke

typhoid suce malaria haka dai muka yi ta

fama. Haka na cigaba da zama a gida ina jinya

ta ina kallon Safina tana zuwa makarantar

ta ni kuwa an rabo ni da tawa makarantar

kuma babu ma zancen komawa ta ko

kuma sake min wata. Daga cikin tashin

hankalin da nake ciki a lokacin shine

maganar Muhammad, ga mamaki na ya

yadda da karyar da nayi masa, da na

samu mukayi online call ma he sounded

so genuinely concerned about jikin Daddy

har yana tambayar in akwai abinda zai iya

yi to help. Sai kawai na saka masa kuka,

ina tausayin sa ina kuma tausayin kaina.

Ina kuma jin haushin kaina akan karyar da

nake ta shirga masa, amma abinda ya faru

da ni abu ne da budurwa ba zata iya bude baki ta gaya wa saurayin ta ba.

Through all these emotional rollercoaster

da nake ciki I missed my period ba tare da

na fahimta ba sai one week after lokacin

da ya kamata in ga period din, ranar da

nayi realizing na shiga toilet ne da niyyar

yin wanka na shire kayana kenan and I

noticed change a kirjina, farko ban yi wani

giving much thoughts to it ba sai daga

baya bayan na fito daga wanda ina shafa

mai sannan na sake fahimtar chanjin and

my first thought was abinda akayi min ne

ya saka naga wanna changing amma

ban kawo ciki ne ba, sai bayan nazo saka

kaya sannan na ga pad a cikin drawer and

it occured to me that ya kamata a ce nayi

period. Na dauko waya ta da sauri na duba app

din da make tracking period dina da shi

and it shows 8 days late. Sai da ma yanke

jiki na fadi. Allah ne kasai ya saka banji

ciwo ba amma na jima ban dawo cikin

hayyacina ba amma tashin hankalin da na

shiga ciki ba xai misaltu ba.

"Allah, Allah, Allah" kawai nake maimaita

wa, na ma rasa me zan roki Allahn, na

rasa me zan ce masa. Kukan ma a ranar

bai zo ba. Hijab dina kawai na saka na

dauki jaka ta tare da key din mota na fita

da sauri, Safina da take falo tana kallon series hankalin ta a kwance tayi ta min

magana amma ni ba ma jinta nake yi ba

na fice da sauri. Abinda nake lissafi kawai

shine inda zan je in tabbatar da zargin da

nake yi sannan kuma in ya tabbata in fitar

da shi. A lissafi na sati biyar kenan dan

haka bai kai matsayin da zai zama laifi in

na zubar da shi ba, sannan kuma na taba

jin waazin da aka ce idan rape case ne irin

nawa malamai sun yi saasauci akan

hukuncin zubar da shi. Sai dai o bayan da na fita daga gidan da mota ban san inda zan dosa ba. Ni dai na

san ba zanje gurin likitan gidan mu da

wannan zancen ba dan idan yaji to kamar

Daddy yaji ya gama ne, ni kuma zan iya

bayar da raina a lokacin dan kar Daddy

yaji wannan maganar.

Haka nayi ta yawo da mota a titinan garin

kano ban san inda zan je ba. Cikin ikon

Allah kawai sai naga signboard din wani

asibiti a bakin titi, I followed the directions

sai gani a kofar asibitin, dan karamin clinic

ne haka, Na shiga na je reception din su

na nemi gain likita suka ce sai na bude

file na bada kudi suka bude min na cike

info din da duka nema amma ko kadan

ban saka addres dina na gaskiya ko

number wayar wani a gidan mu ba.

Daga nan naje na hau layi, babu abinda

nake yi sai salati da istigfari a zuciyata ina

rokon Allah yasa kar zargi na ya tabbata, a

haka layi yazo kaina na shiga gurin likitan

direct na gaya masa pt nake so ayi min.

Ya tambaye ni symptoms dina na fada

masa sai ya rubuta min test din yace inje

lab suyi min, na je lab din suka dauki jini

na, for the first time in my life aka huda jiki

na ban ma san an huda ba dan zafin da

nake ji a raina ya ci uban zafin allurar.

Ina zaune dai har aka gama, zuwa lokacin

na tabbatar an fara nema na a gida dan

dai har lokacin layi na a kashe yake da an

fara kira na. Hankali na idan yayi dubu ya

tashi. A haka aka rubuta min result din

aka ce in mayar wa da Dr. Ban mayar din

ba na samu guri na zauna na bude

takardar da sauri ina bin rubutun da kallon


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login