Showing 237001 words to 240000 words out of 375662 words

Chapter 80 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7977

da motar yace

"welcome back to Nija" gidado yayi ajiyar

zuciya yace "home sweet home" sai dai

kuma a ransa bashi da tabbas din how

sweet the home will really be for him.

Al'ameen ya dan kalle shi yace "you look

good, you look really good, har wata kiba

naga kayi fa, and with that skin dole ka

nuna baka san rana ba" gidado ya dan

daga hannunsa yana kallon skin din

sannan ya tabe baki yace "change of

weather, just take me home kaji? Ka kaini

inga rabin rai na ko na san na dawo

Nigeria" Al'ameen yace cikin tsokana

"kaga angon Safina wanna doki haka?

ana ta missing amarya ko? Tunda ka bata

rabin ran ka mu babu komai zamu raba

the other half din" Gidado ya jefa masa

wata harara yace "Safina kuma? a'a ba

Safina ba Sa'adatu" Alameen yace

"wacece kuma saadatu? Kar dai kace min

new catch kayi" Muhammad yayi dariya sosai sannan yace "uwar safina nake nufi, sunanta Sa'adatu" Al'ameen yayi dariya shima yace "wallahi baka da kirki

Muhammad, warta fa kace, yanzu sunan

sirikar taka kake ambata kanka tsaye?"

Muhammad ya daga kafada yace "kai ka

jawo mata, why will you say she is my

rabin rai?" Alameen yace "then who is

your rabin rai? Am sure you are not

talking about that married girl k0? Ko har

yanzu bamu wuce gurin ba?" Muhammad

yace "I was talking about Mama. Mama is

my rabin rai please. And don't mention

that girl's name. let the sleeping dog lay"

Muhammad Alameen bai ja maganar ba

kamar yadda gidado ya bukata, sai suka

koma hirar humaira da sauran family

members, daga nan kuma suka yi maganar various businesses din su da yadda suke adjusting to their

responsibilities.

Ana bude musu gate mama ta bude kofa

ta tsaya tana kallon su har suka yi packing

suka fito a tare, Gidado yana fadada

murmushin sa yace "Mamana" sannan ya

karasa inda take da sauri ya rungume ta,

gabaki dayanta iya kirjinsa ta tsaya.

Alameen ya karaso sai ta saki Muhammad

tana amsa masa gaisuwar sa tare da

tambayar sa lafiyar Humairah, bai amsa

ba ya sunkuyar da kai yana shafa keya

cikin nuna jin kunya, mama tace "Allah dai

ya sauke ta lafiya, Allah ya sauke su lafiya baki daya" Alameen ya amsa a hankali sannan yayi musu sallama yace zai koma office, Mama tayi kokarin ya shigo yayi

lunch amma yaki yace sauri yake yi.

Suna shiga ciki Muhammad ya zauna

akan kujera cikin nuna gajiya tare da fara

unbuttoning shirt din jikinsa, "akwai zafi

mama" mama ta karo karfin ac sannan ta

zo ta zauna tana kallonsa fuskarta cike da

farin cikin yanayin da ta ganshi a ciki "you

look good Muhammad. I was worried ko

baka samun abinci kana ci sosai" yayi

murmushi "ba sosai nake cin abincin ba

fa, ina ta missing abincinki, kawai dai ina

samun bacci ne sosai and the weather

there is good. Shine kawai. Ina abba?"

tace "yana office shi da Haidar" ta kalli

agogo "but they will soon be on their way".

Yaran gidan suka fara hidimar ajiye masa

kayan ciye ciyen da mama ta tanadar

masa. Ya zuba drink a cup yana tasting

sanyin sa sai yace da daya daga cikin

yaran "get me ice, saurj" mama tace "kai

dai kana son sanyi, ka sha ruwan sanyi ka

sha kankara kayi wanka da ruwan sany"

ya danyi murmushi bai ce komai ba. He

sometimes feels as if his blood is too hot

shi yasa yake cooling din sa down. Abu

mai sanyi yana calming dinsa kuma baya

saka shi ciwo.

Aka ajiye bowl of ice din a gabansa tare

da diba aka zuba a cikin drink din da

already ya riga ya zuba a cikin cup, ya

dago kansa suka hada ido da mai zuba

masa ice din. Ta sha kwalliya kamar ranar

ne zaa kai ta gidan miji. Jikinta sanye da

doguwar riga ta shadda da ta sha aikin

stones sai kyalli take yi, fuskarta with all

the make up possible, daga dukkan alamu

ma gidan kyalliya taje musamman aka yi

mata kwalliyar aka kuma daura mata

dankwalin kanta, hannayenta sun sha

both bakin lalle da ja. Fuskarta dauke da

murmushi.

Ta miko masa kofin tare da cewa "sannu

da zuwa" ya karba, amma maimakon ya

sha sai ya ajiye akan table din gabansa

tare da cewa "yauwa, sannunki". Ya juya

gurin Mama "Mama bara inje inyi sallah

tukunna" tace "gaskiya kam, kar ka ci

abinci jikin ka yayi nauyi ka kasa tashi.

Jiya na saka aka gyara maka dakin ka

dama. Yana bude" ya wuce da sauri zuwa

dakin nasa.

A can ya shiga toilet ya watsa ruwa ya

chanja kaya zuwa jallabiyya da wando

sannan yayi sallah azahar da laasar din da

yaji already an fara yi. Sai kuma ya dawo

falo, mama bata nan sai safina a zaune ta

dasa wa hanyar da zai fito ido, yayin mata kallo daya ya dauke kai yana jin gabansa yana faduwa, ta chanja, she looked a bit like abinda baya son ya ambata ko da

kuwa a zuciyarsa ne, she cannot be. It is not possible. Amma shi ya san cewa it is very possible kawai yana so yay denying ne to protect his heart. Ya dauki wani cup din, ignoring wancan da safina ta taba, ya sake zuba ice sannan ya zuba drink a kai ya zauna yana

jujjuyawa a hannunsa har sai da yayi masa

sanyin da yake so sannan ya daga ya

shanye ya kuma hada wani ya ajiye. Ta

sauko daga kan kujerar da take kai zuwa

gabansa tace "me za'a zuba maka?

Akwai.... " Ya katse ta "I know menene

akwai, so just shut your hole please. And

please get out of my site ina son zama da

family na" ta gyara zaman ta a gabansa

tace "I am your family" ta shafa marar ta a

hankali tace "we are your family" ya mike

tsaye yana jin kamar yayi ball da kayan da

suke gabansa. "goddammit" ya fada a

hankali, almost inaudible dan yasan ko da

wasa mama taji yana yin zagi sai ransa ya

baci.

A lokacin abba ya shigo, haidar yana

binsa a baya da briefcase a hannunsa,

duk su biyun suka saki murmushin ganin Muhammad, ya juya gurinsu shima yana

kirkirar murmushi duk kuwa da yadda

hankalinsa gabaki daya yake a tashe. Ya

je ya rungume abba sannan kuma ya

russuna ya gaishe shi, ya rungume haidar

shima, haidar yana kare masa kallo yace

"amma bread kake ci a can ko? Naga

kamar wanda aka saka maka yeast?

Mama da ta fito daga sashen ta da charbi

a hannunta jikinta sanye da hijab, daga

alama sallah tayi tace "tubarkallah". Abba

yayi dariya shima yana jin dadin ganin dan

nasa yace "zai zazzage ne ai, akwai aiki

da nake ta tara masa yana nan yana jiran

sa"

Safina da take zaune a gefe ta gaishe da

abba ya amsa mata tare da tambayar ta

jikin ta, bata ce komai ba ta sunkuyar da

kai tana murmushi, Haidar ya fara

tsokanar ta "yau da ya dawo, tagumi ya

kare. Nace wannan ciwon nata har da

rashin yaya" ta dan harare shi cikin wasa

amma bata ce komai ba sai mama tace

"kinyi sallah kuwa safina? Dan miji ya

dawo kuma sai ki zauna ki saka shi a gaba

kina kallo ba zaki je kiyi sallah ba?" safina

ta mike da sauri ta shiga wani daki da

yake cikin falon.

Suna zama sai ga mufida ta shigo gidan

da gudunta, tazo ta rungume Muhammad tana dariya, ya daga ta daga jikinsa hana murmushi, yana kin dadi a zuciyarsa "yar autar Mama, ke da nace miki zan zo har gida ina same ki?" Ta bata rai "da zaka

tafi ma cewa kayi zaka je muyi sallama

kuma ba ka je ba. Shi yasa naki jiran ka

yanzu" yace "ayi hakuri, nayi niyyar zuwa

wallahi sai abubuwa suka duke min

hankali, sai da na shiga jirgi na tuna" tace

"zanyi hakurin but I need one more

squeeze" ta fada tana kara rungume shi.

Bayan Mufida ta gaishe da kowa sai suka

hadu gabaki daya suka tafi dining suka

fara zuba abinci, tun kafin su fara ci sai ga

Safina ta dawo, fuskarta tana nan da

kwalliyar ta, tana shiga gurin Mufida tace

"hey in law! I was about to ask about you

sai na manta" Safina tace "nayi fushi ai.

Tunda kinga yayanki ai dole ki manta da

ni'" Mama ta juyo tana kallon Safina tace

"Safina wannan fuskar kuwa kin wanke

ta? Ta yaya kika yi alwala da wannan

kwalliyar?" Safina ta dan yi murmushi

nervously "Mama nayi, ai ba zata fita ba

dama" Mama ta girgiza kai "ai kuwa dai in

bata fita ba alwala ba tayi ba. Ki koma ki

wanke ta tas ki sake alwala ki sake Sallah.

Ai ya ga kwalliyar taki" Safina ta dan bata

rai "Mama nayi alwala kafin inje kwalliyar

fa" Mama tace "tun safe kenan? Alwala

tun safe har la'asar ai ya kamata a hakura da ita ko?" Safina ta juya ta koma ciki,

Mama ta gyara zaman ta tana cigaba da

zuba wa Abba abinci. Haidar yayi dariya,

Mufida tace "Mama kin ba da Safina a

gaban Haidar, a gaban kuma mijinta"

Mama tace"ga Abban ku nan a zaune

shima ai. Dole mu gyara mata mata

tarbiyyar ta ai, ko mijin nata ne yayi ba dai

dai ba dole a gyara masa ballantana ita,

she will soon become a mother, idan babu

tarbiyya ai mun shiga uku baki daya".

Muhammad ya kware da abincin da yake

ci. Abba ya zuba masa ruwa ya mika

masa, ya karba ya sha amma still yaji

abincin ya tsaya masa a makogwaronsa

ya ki wucewa, wani zafi yaji jikinsa ya

dauka. Ya fara panning fuskarsa da

hannayensa sai ya lura kowa na gurin shi

yake kallo. Abba yace "lafiyar ka kuwa?"

Muhammad ya sake daukan cokalin ya

debi abincin yace "lafiya lau.

I am not feeling good ne kawaj" Mama

tace "kace lafiya lau kuma kace you are

not feeling good, Wanne ne kenan? Kar fa

mu je ko heat stroke zaka samu dan tun

dazu kake complain din zafi" Haidar ya

mike tare da kara karfin ac sannan shima

ya tambaye shi "are you okay Yaya?" Muhammad ya kirkiri murmushi tare da gyada kai, yana jin babu dadin yadda duk suka shiga damuwa lokaci daya saboda

shi.

"It is okay. I am okay yanzu" ya fada yana

sake kai lomar abinci bakinsa duk da

waccan lomar har lokacin bata wuce ba. A

zuciyarsa ya san abinda duk wadannan

maganganun suke nufi amma ya kasa

barin kwakwalwarsa ta yarda. Mama tace

"'in ka cigaba da jin zafin dai kayi magana

aje asibiti, tun kafin abun ya zama babba"

ya gyada kai kawai tare da kokarin cigaba

da cin abincin da yake gabansa.

Sunanan zaune Safina ta sake dawowa, ta

wanke fuskar tas yanzu, daurin dankwalin

ma daga dukkan alama an kwance shi an

sake, Mama tace "yauwa, ko ke fa, yanzu

har kinfi kyau ma" ta danyi murmushi tana

sunkuyar da kanta kasa, Mama ta nuna

mata kujerar kusa da Mufida daga right

dinta tace "zauna to ke ma kici abinci, tun

safe banga kinci komai ba kina ta

kwalliya" sai ta zagaya ta zauna a left din

Mufida, kujerar da take kusa da

Muhammad. Ta zuba abinci ta fara ci,

yana jin idanunta a kansa amma bai ko

kalli inda take ba, he tried as much as he

can to not ruin the moment for his family.

Suka yi ta hirar su suna bashi labarin gida

yana basu labarin can. Bayan sun gama

kuma sai suka sake dawowa falo ya zauna

yana ta yiwa Abba bayanin tarukan da

yayi attending da matsayar da aka samu a

tarukan and what they mean to their business.

Suna nan tare har magrib, suka je suka yi

sallar suka sake dawowa suka cigaba da

hirar su, zuwa lokacin Muhammad ya dan

ware, trying not to look at side din da

Safina take zaune duk kuwa da cewa yana

jin yadda ta zuba masa ido a jikin sa.

Daga baya sai ga mijin Mufida yazo

daukan ta, shima ya shigo yayi joining

hirar ta su, sai kuma suka yi dinner tare

sannan Abba yace kowa ya zo ya tafi

gidan sa. Mufida ta fara tsokanar Safina

"Safina ki kara wa Mama ko sati biyu ne

mana" Mama tace "ina fa, ta tafi gidan

mijinta ya cigaba da jinyar a can. Tun dazu

dama na saka an kai yan aikinta gidan dan

su gyara musu kafin su tafi"

Babu kunya sai ga Safina ta jawo akwatin

kaya ta fita da su waje, tana ganin

Muhammad ya tashi kuwa tayi wa Mama

sallama, dama Abba ya riga ya shiga ciki,

ya fita ta riga Muhammad din shiga motar

ta zauna, maybe tana tsoron kar yayi

mata irin na ranar nan. Ya tsaya yana kallon ta kawai a ransa yana tunanin da ace daya motar tana nan da ita zai je ya shiga yayi tafiyar sa ya barta anan ya ga

yadda zata yi. Amma kuma Mama tana

tsaye a bakin kofa tana kallon su, yayi

sallama da su Mufida ya zo ya shiga

motar yana bata wuta Mama ta leko tace

"ka tafi a hankali fa, ban da gudu, kai a

guje dama kake driving dinka sai kace dan

tsere" yayi murmushi "to Mama, ba zanyi

gudu ba" tace "Allah ya sa" ya ja motar a

hankali suka fita daga gidan, amma ana

rute gate ya fige ta a guje saura kadan

Safina ta hantsula, tayi sauri ta gyara

zamanta tare da saka seat belt.

Suka fara tafiya da farko in silent, Allah

Allah yake yi suje gida ba tare da tayi

magana ba ballantana tayi confirming

abinda yake suspecting. Har ya fara

murnar ba zata yi ba sai kuma tayi din "ya

hanya?" Yayi kamar bai ji ta ba ya kara

gudun motar sa, sai kuma tace "you run

away, gashi kuma ka dawo" ya dan daga

kafarsa ya juyo yana kallon ta yace

"excuse me? Me kika ce?" Ta maimaita

"cewa nayi ka gudu, gashi kuma ka dawo"

yace "ban gane na gudu ba? Gudun me

zanyi? Run away from what?" Tace "you

run away from me" yace "and why will I

do that?" Tace "because you found out

that you cannot resist me. Shi yasa ka gudu"

Sai da ya danyi karamar dariya "you are

delusional. You and I know that that thing

that you think happened…….." Ta katse shi

"that I think happened? Kana nufin bai

faru kenan ba. Kana nufin I imagined it?

Okay wanne bangaren nay imagining the

first round or the second" yaji kamar yaje

ya jefa su a rami gabakidaya su mutu

kowa ya huta. Yana girgiza kansa cikin dacin rai yace "I wanted to not talk about it now, amma

tunda kin kawo topic din let me spell it out

for you. Na farko I did not run away from

you or from anything, na riga nayi

planning tafiya ta before that thing you

think is something happened. So idan

kina tunanin it means something to me ki

daina, it means nothing, you mean

nothing and will never be anything to me.

Abu na biyu kuma mafi muhimmanci

shine ni da ke gabakidaya mun san cewa

what happened that day wasn't natural,

you did something to me, I don't know

what amma ke kin sani kuma you are

going to tell me one way or another. Me

kika yi min?" Ya fada almost shouting.

Tayi kokarin matsawa daga kusa da shi

yadda ransa ya baci gani take kamar zai

kai mata duka.

"'Ba zaki fada ba?" Ya sake yi mata tsawa.

Ta rufe fuskarta da hannayenta da suka

sha lalle tace "ni banyi maka komai ba. Ni

babu abinda nayi maka". Yayi horn a bakin

gate mai gadi ya bude masa kofa ya shiga

da motar yaje yayi packing ya juyo yana

kallon ta "Ke munafuka ce Safina. Baki da

gaskiya ko kadan. Kin aikata abinda kika

aikata and you have the guts to spill out

trash from that hole in your face kina gaya

min maganar banza? You did something

to me ke ma kin sani, you thought idan

naje gadon ki I will fall in love with you ko?

Haka kike tunani? To abinda baki sani ba

shine what you did made me hate you the

more, made me despise you the more,

your gutter behavior and your trash of a

body disgust me. I am going to find out

what you did and I am going to use it as a

pass to my freedom from you". Ya bude

motar ya fita sannan ya buga kofar motar

da karfi.

Part din sa ya wuce, sai daya bude ya

shiga sannan ya tuna bai fito da kayansa

daga mota ba, ya juya ya fita ya tarar har

lokacin tana zaune a mota tana kuka. Ya

fito da kayansa ya ajiye ya bar mata nata a

ciki. Mai gadi yazo da sauri ya gaishe shi

ya dauki kayan ya wuce ciki. Sai a lokacin ta fito daga motar, ta tsaya tana kallon sa suna magana da mai gadin, yan aikin ta biyu da cousin dinta da suke gidan suka fito ta bude booth ta basu kayan ta suka

shiga da shi cikin gida.

Sai da ya gama yiwa mai gadi magana ya

juya zai tafi sannan ta kira sunansa

"Muhammad" ya dakata amma bai juyo

ba. Ta karasa bayan sa ta tsaya sannan

tace "I am pregnant" still bai motsa ba

ballantana ya juyo ya kalle ta. Ta cigaba "I

wanted to tell you tun kana can, amma ba

ka daukan waya ta ba ka duba messages

dina. At least idan banci albarkacin

soyayyar da nake yi maka ba ai ya kamata

yanzu in ci albarkacin abinda yake ciki na"

Ya yi gaba, pretending kamar bai ji abinda

ta fada ba amma ransa tafasa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login