Showing 129001 words to 132000 words out of 375662 words

Chapter 44 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7920

kira Safiya.

Safiya ta shigo kanta a kasa tana kallon

yadda kafafuwanta suke nutsewa a cikin

carpet din falon da ta kasa tantance da me

aka yi shi. Kamar da katifa kamar kuma da

gashin rago.

Ta durkusa daga nesa da su ta gaishe da

Hajiya, Hajiya tace mata "ya sunan ki?" Tace

"Safiya" Hajiya ta kalli ciwon da yake kafar

Safiya tace "ya akayi kika ji ciwo haka

Safiya?" Safiya ta dago kanta tana kallon ta

tace "kusa na taka guda biyu, lokacin da

nake kokarin tono yaruwata da katangar

dakin mu ta fada mata".

Duk hajiyoyin biyu suka bude baki, thinking

about the trauma, dan itama Hajiya Kyauta

bata san yadda mutuwar Sauda ta kasance

ba, Hajiya Maryama tace "ina yar'uwar taki

take to yanzu? An fito da ita?" Safiya tace

"ta mutu. An fito da gawarta daga karkashin kasa, sal aka sake mayar da ita aka binne a

kasan wata kasar a makabarta" suka sake

yin shiru baki daya, sai kuma Hajiya ta sake

tambaya "mamanki fa? Me ya faru da ita?"

Safiya tace "Baba Hadiza, Mota ce ta kade

ta, sanda take gudu zata cecemu ni da

Sauda daga hannun Dauda" suka sake yin

shiru, safiya ta kara cewa "Dauda din yayan

mu ne" ba tare da sun tambaye ta ba,

Sai Hajiya Maryama taji tana son jin cikakken

labarin Safiya, ta tambaye ta, ita kuma ta

bata labari tiryan tiryan a yadda rayuwar ta

ta kasance tun daga kan abinda ta sani na

labarin auren iyayen ta har zuwa rasuwar

Alhaji Haladu da kuma tragedies din da suka

biyo baya.

16

1:15 AM

Bata san tana kuka a labarin nata ba sai da

ta gama taga audience din nata suna share

hawaye sannan ta share nata ita ma. Ta

cigaba da magana "so nake in samu hanyar

da san zamu jari in fara sana'"a, shine naje

grin Hajiya Kyauta ita kuma tace min zata

kawo ni nan in yi aikatau sai in tara kudin da

zan yi jari dasu, Hajiya dan Allah ki dauke ni

aiki, zanyi miki aiki sosai kuma zan ringa

girmama mutane yadda ba zaki kore ni ba, in

na tara kudi sai in gina wa Baba Hadiza

masallaci in roki Allah ya gina mata gida a

aljanna da ladan masallacin". Hajiya ta sauko daga kan kujerar da take ta

durkusa a gaban Safiya tace "zan dauke ki

aiki kinji? Kuma ba zan kore ki ba ko da kinyi

laifi, in kinyi laifi zanyi miki fada in baki

tarbiyya kamar yadda uwa ya kamata ta

bawa yar ta tarbiyya. Kin zama yata daga

yau kinji? Ina fatan nima Allah zai gina min

katon gida a aljanna da ladan rikon da zanvi

miki"

Hajiya Kyauta ta share nata hawayen tace

"Amen Hajiya. Dama nasan zaki karbe ta.

Banyi tunanin kowa ba sai ke. Allah ya dubi

niyyar ki ya baki ikon sauke wannan babban

nauyin da kika dauka" Hajiya tace "Ameen.

Ke ma Allah ya baki ladan taimakon da kika

yi mata da zuciya daya. Da baki dauko ta ba

da yadda zuciyar ta ta bushe din nan

gudawar zata yi ko da kuwa an daura mata

auren ne, kuma kinga da ba'a san hannun

wanda zata fada ba".

Ta juya gurin Safiya tace "zan dauke ki aiki,

zan ke baki albashi kamar yadda bake bawa

sauran yan aikin gidan nan, zanyi hakan ne

saboda ki samu ki cika burin ki na gina wa

mahaifiyarki masallaci da gumin ki, amma ba

zan rike ki a matsayin yar aiki ba, zan rike ki

a matsayin yata, Kuma ina so ki saki jikin ki,

duk wata magana da kika san zaki iyayi da

Baba Hadiza ki zo kivi da ni, in wata shawara

kike nema ki zo gurina, duk wani abinda ya

shige miki duhu ki tambaye ni, duk wani abu da kike bukata ki tambaye ni. Kinji?" Safiya

ta gyada kai tana share hawayen ta, rabon

da ayi mata magana with motherly concern

irin haka tun Baba Hadiza tana da rai, hakan

yasa ta tuna irin yadda take missing

mahaifiyar tata.

Daga nan sai Hajiya ta dauki wayarta ta yi

kira, "Sa'adatu zo ina neman ki". Jimawa

kadan sai ga daya daga cikin yaran da aka

kora dazu ta fito daga ciki ta zauna a kusa

da Hajiya tace "Hajiya ganj" Hajiya tace

"ga

yar'uwa kun samu ke da A'isha, ta zama

kanwar u daga yau" Sa'adatu ta kalli Safiya

ta a yatsina fuska tace

"Hajiya yar'uwar mu

kuma? Ji nake sabuwar yar aikin da aka

kawo miki ce?" Hajiya tace "shi dan aiki ba

mutum bane ba kenan? Ba zai zama dan

uwa ba? So nake kuje ku samar mata kayan

sawan da suka yi muku kadan a cikin kayan

ku, da duk sauran kayan da kuka san zata

bukata kafin in fita in siyo mata. A dakin ku

zata zauna tare da ku saboda ina son ku

kula min da ita, duk abinda tayi ba dai-dai

ba ku gyara mata har ta gane ta saba da irin

rayuwar nan. Kin gane?"

Sa'adatu ta ce "eh" amma daga ganin

fuskarta kasan bata ji dadin maganar ba,

Hajiya ta kara sa da cewa "saura kuma kije

kiyi tayi mata wannan fadan naki da baya

karewa". Ta juya kan Safiya tace "wannan kanwata ce

uban mu daya sunan ta Sa'adatu, daga

yanzu ta zama yayarki. Zata ke kula dake

kamar yadda yaya zata kula da kanwarta. Sai

dai tana da fada" ta karashe maganar cikin

tsokanar Sa'adatu da har lokacin take zaune

fuskar ta a bace. Hajiya tace "ku je ki nuna

mata dakin ku.

Ta juya gurin Hajiya Kyauta tace "to sai

kuma a bani yar aikin"

Sa'adatu ta mike Safiya ta bi bayanta

hannunta rike da ledar da hotan su yake ciki,

wannan ledar ita kadai ce abinda Safiya ta

shiga da shi gidan Hajiya.

Wani dan corridor suka bi sannan suka yi

kwana, sai suka tarar da kofofin dakuna

guda biyu da kuma toilet a tsakiya. Sa'adatu

ta bude kofa daya ta shiga sai Safiya ta bita

amma sai ta tsaya a bakin kofa kanta a kasa.

Babu abinda bata so a rayuwar ta irin a

wulakanta ta, ta kuma lura kamar yammatan

suna da wulakanci. Kallon dai suke cigaba

da yi a dakin a tvn dakin. Daya yarinyar tana

zaune a kan gado, Lawisa tana zaune a

kasa,

6

3

1:15 AM

Sa'adatu ta zauna akan kujerar dakin tace

"Fati ga bakuwa nan inji Hajiya, tace zata

zauna anan a wajen mu. Kuma zata zama kanwar mu" wadda aka kira da Fati ta kalli

Safiya sannan tace "yar'uwar ku ce?"

Sa'adatu tace "ni dai ban san ta ba, ban san

a ina ta samo ta ba, tace kuma mu bata

kayan sawa da abubuwan bukata" Lawisa da

take zaune a kasa tace "yar aiki ce fa, na

ganta tare da wannan matar da tazo"

Sa'adatu tace "ina ruwan ki? Bana hanaki

muna magana kina saka mana baki ba?

Tashi ki fita?"

Lawisa ta taso saura kadan ta bangaje

Safiya sai ta bata guri ta wuce. Tana nan dai

a tsaye Sa'adatu ta bude wardrobe din dakin

ta fara debo kaya tana ajiyewa akan dago,

sai data bata kaya sunfi set goma, har da

mayafai da hijabs, sannan ta bude drawer ta

bata sabulun wanka, tooth brush da paste,

da kuma man shafawa da roll on da turare.

Ta tsaya tana kallon ta sai ta kalli Fati tace

"kuma fa kyakkyawa ce. Gyara kawai take

bukata" Fati ta kalle ta ta tabe baki tace

"fatan dai ba nan dakin zaki ajiye ta ba. Sai

dai ki kata can dayan dakin" Sa'adatu bata

ce komai ba ta saka hannu ta kwashi kayan

tace "debo sauran mu tafi" Safiya ta debi

sauran kayan suka fita suka shiga dayan

dakin. Ta lura kamar dakin ba'a amfani da

shi kamar wancan, amma kuma shima

exactly kamar wancan din yake, Sa'adatu ta

ajiye kayan akan dago tace "ga kaya nan na

baki, ki zuba a cikin wardrobe din nan ki ki zuba a cikin wardrobe din nan ki

ringa sakawa, ga kuma kayan gyaran jiki

suma na baki, kin iya amfani da su?" Safiya

bata ce komai ba sai Sa'adatu ta nuna mata

yadda zata yi amfani da komai, sannan ta

nuna mata yadda zata kunna kayan

electronics din dakin, sai kuma suka fita ta

nuna mata yadda zata yi amfani da toilet,

daga nan ta mayar da ita falo.

Sanda ta koma falo already Hajiya sun gama

maganganun du da Hajiya Kyauta, Safiya ta

fahimci Hajiya ta dauki Jamila aiki itama a

gidan, amma instead of cikin gida da aka

shiga da ita sai aka hada Jamila da Dije,

matar da suka gani a waje, ta tafi da ita

bangaren yan aiki mata.

Hajjya ta tambayi Safiya in ta samu duk

abinda take bukata, Safiya tace "ta bani

kaya masu yawa, Nagode sosai Allah ya kara

arziki" Hajiya tace "Ameen. Tana da kirki ai

da kyauta, sai fada fal cikinta" Sa'adatu ta

tura baki tana kunkuni.

Daga nan suka yi sallama da Kyauta da

sauran yaran, Kyauta tayi mata alkawarin

duk sanda ta shigo Abuja zata je zuwa tana

ganin ta, Ta tsaya tana kallon su har suka

fita daga gate sannan ta juya ta koma ciki, A

lokacin Safiya tana da shekaru goma sha

hudu a duniya, dai dai da shekarun Baba

Hadiza sanda aka aura mata Alhaji Haladu. A hankali Safiya ta fara adjusting to rayuwar

gidan duk da dai ba xata ce babu challenges

ba amma tana jin dadin changes din sosai.

Ita kadai take kwana a dakin da Sa'adatu ta

kai ta, and all the nights she misses her

mother and siblings, wishing suma rayuwa

ta basu irin wanna damar ta kwanciya a irin

wannan gadon da kwana cikin ac a

lafiyayyen dakin da baya zuba ballantana ya

fada a kansu. Kullum ita take fara tashi a

gidan, kafin kuma mutan gidan su tashi ta

gyara duk inda take da access to, tun daga

dakin da take kwana har falo har kitchen da

duk wani daki da ya ke bude ko da kuwa

babu kowa a ciki. So take ta nuna wa Hajiya

irin gwanintar ta dan Hajiyar ta san bata yi

kuskuren daukan ta aiki ba. Satin ta daya a

gidan Hajiya ta dinka musu sababbin kaya

ita da Jamila, sai dai na Safiya yafi na Jamila

yawa.

Ta lura su Sa'adatu suna zuwa makaranta,

kullum da safe zasu tashi su shirya, Dije zata

hada musu breakfast su ci tare da wasu

samari biyu suma data fahimci rikon su ake

yi a gidan, in sun gama driver zai kai su

school, ita kuma zata je ta gyara musu dakin

da suka kwana a ciki sannan ta wanke toilet

din da suka yi amfani da shi,

Farko ta samu challenges kafin ta iya aikin gidan, sai da Dije ta zauna tayi mata bayanin

yadda ake yin amfani da komai sannan ta

iya, a hankali kuma har ta kware. Ta fahimci

cewa Fati yar kanwar mai gidan ce, ita kuma

Sa'adatu kanwar matar gidan.

9

4

1:15 AM

Ta kuma fahimci cewa daga mai gidan har

matar gidan yan kasuwa ne kwararru dan

har sunayin muamala sosai da kamfanonin

kasashen waje.

And she wished that one day she will be like

them....

Jinin su yafi haduwa da Sa'adatu akan Fati,

saboda Sa'adatu tafi fada amma tafi son

mutane, Fati tana da rainuwa musamman da

ta kara fahimtar cewa da gaske Safiya ba

yar uwar Hajiya bace ba.

A gurin Hajiya ma kuma tana samun kulawa

ta musamman dan ko da yaushe in dai suka

hadu sai ta tambaye ta "kin ci abinci? Akwai

abinda kike so? Ki ringa yin bacci sosai kina

hutawa ko kya samu ki dan yi kiba, ga

Sa'adatu nan sai hawa take kamar fulawar

da aka saka wa yeast". In Sa'adatu taji haka

sai ta kara kumbura,

Ranar nan tana dakin da su Sa'adatu suke

tana yi mata tsifa, sun kulla kallo a tv suna yi

ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana

shirya irin hidimar da za'a yi a birthday din

wata kawar su da yake zuwa soon. Hajiya ta

shigo ta tsaya a bakin kofa tana kallon su

tana kuma jin irin hirar da suke yi ba tare da

sun ga shigowar ta ba. Sai da suka gama

sann6ta karasa shigowa ta kuma kama fada.

"Kun ganku yaran nan sai kunyi wa kanku

fada fa. Rayuwa ba zata tafi muku yadda

kuke so a haka ba. Ku baku da tunanin

komai sai na jin dadin duniya? Ya kamata

ace zuwa yanzu kun fara tunanin yadda

zaku ke juya biyar tana komawa goma.

Rayuwa bata da tabbas. Kamata yayi ace

kun fara tunanin wata sana'ar hannu ko wani

kasuwanci da zaku iya fara wa tun kafin ku

gama secondary school. Hausawa sunce da

zafi zafi ake dukan karfe"

Sai duk su biyun suka kwashe da dariya

"haba Hajiya, wacce sana'a ce zamuyi ne

wai? Sai kace wasu maza" "mu kam ai sai

dai a nemo a kawo mana. Soft life kawai"

Hajiya ta bude baki "soft life? Kawai dai

kuce min cima zaune na tara a gida na. To

Allah ya sawake muku. Amma dai sai kun

sake tunani tun kafin lokaci ya kure muku,

Ko irin dan cin cin din nan ne da zobo ku

ringa yi mana kuna tafiya da shi makaranta

kuna siyarwa" Sa'adatu tace "cin cin fa kika

ce Hajiya? Haba dai! Wuce nan mana""Safiya dai bata ce komai ba har Hajiya ta

fita, sai data gama tsefewa Sa'adatu kitson

ta sannan ta fita tana neman inda Hajiya

tayi, a falon ta na sama ta same ta waya da

dealer din da zai kawo mata abayas. "A

sabon shagona zan saka su, kaga kuma

zuwa nan da two weeks nake son bude shi.

Dan Allah kar saba min alkawari".

Safiya ta zauna a kasa sai da ta gama wayar

sannan ta kalle ta cikin kulawa tace "Safiya?

Kina bukatar wan abu ne" Safiya ta gyara

zama tace "maganar sana'a da naji kina

yiwa su Sa'adatu. Kina gain nima zan iya

yi?" Hajiya ta gyara zamanta tace "ba su

Sa'adatu nake yiwa maganar sana'a ba, har

da ke kema, gabaki dayan ku nake yiwa. Da

akwai sana'ar da kike gain zaki iya farawa

yanzu?"

Safiya tayi shiru tana tunani sannan tace

"a

garin mu dai tun bayan rasuwar Baba ni da

Baba Hadiza muna yin awara da kuma wake

da shinkafa muna siyarwa, ban sani ba ko

anan zasu siya?" Hajiya ta dan yi shiru tana

tunani sai tace "gaskiya bani da tabbas din

zaki yi cinikin wake da shinkafa anan, Amma

ina saka ran zaki vi na awara tunda abin

sha'awa ce." Ta sake yin shiru sai kuma tayi

murmushi tace "kin san wani abu. I have a

plan for you. Ki rubuta min duk abinda kike bukata na yin sana'ar awara ni kuma zan

siyo miki. Zaki iya yin aikin dahuwar awarar a

can filin baya, sai mu aika duk makota zan

kuma yi miki talla a gun customers dina, sai

a ringa sakawa a robobi ana aikawa ko'ina"

Safiya tayi murmushi tana jin dadi "Nagode

Hajiya, Nagode sosai " hajiya tace "and that

is not all, zan bude sabon shagon da zan

ringa siyar da fabrics na mata, da sauran

ado na mata, zan dauke ki aiki a matsayin

sales girl din shagon, zan hada ki da

yarinyar da already na riga na dauka sai kuyi

akin tare ki koyi harkar yadda ake gudanar

da business" Safiya tayi shiru tana kallon ta

tace "amma Hajiya already kin riga kin

dauke ni aiki anan gidan ai, ko kora ta kika yi

daga akin gidan?" Hajiya tace "ban kore ki

ba kuma ba zan kore ki ba, ko baki san ana

yin aiki biyu a lokaci daya ba? And also

concerning aikin gidan nan, Dije tace min

kusan komai ke kike

14

1:15 AM

yi, maybe shi yasa har yanzu kika gagara yin

kiba, daga yau na ware miki aikin ki,

bedroom dina da nan falon su kadai ne naki.

In kika yi kika gama sai ki tafi zaman shagon

ki, in kin dawo da yamma sai ki dafa awarar

ki, are you up to the task?" Safiya tayi shiru

dan bata gane karshen ba, Hajiya ta

maimaita mata "zaki iya yin hakan?" Da sauri ta gyada kai "zan iya Hajiya, sosai ma".

And that was how it began.

Ana bude shagon Safiya ta fara aikin zaman

shago, kullum da assuba tana tashi zata hau

saman Hajiya, dama kuma Hajiya ba'a dakin

ta take kwana ba tana dakin Alhaji. Dan haka

dakin nata bashi da datti gyaran sa babu

wahala, cikin kankanin lokaci Safiya take

gamawa sannan ta sauko ta gyara nata

dakin tayi wanka ta shirya taci abinci ta debi

na rana ta tafi shago. A can take wuni sai

la'asar take dawowa gida sannan tazo ta

dora dahuwar awarar ta. Ta kan dafa da

yawa wani lokacin ta yi freezing sai take

daukowa tana soyawa ana zuwa ana siya

daga gida gida. Yadda take cinikin awarar

har mamaki yake bata. Tana kuma diyar da

danya, idan mutum yafi so ya soya da kansa

a gida. Har a shago idan customers sunzo

takan yi musu tallan awarar ta, daga baya

sai ta fara soyawa tana tafiya da ita shagon

ma tana siyarwa a can.

Da lokacin albashi yayi Hajiya ta lissafa

kudin albashin ta na aikin gida ta bata a

hannunta, Sannan ta sake lissafa kudin

albashin zaman shago ta sake bata, Sai ta

tsaya tana kallon kudin kawai dan dai ita

bata taba gain kudi masu yawan wadannan

ba. A garin su ko masu aikin gwamnati jin suna daukan wanna kudin. Ta tashi ta je ta

dauko kudin ribar awarar ta da take tarawa

ta kara su akan albashin nata. And the first

thing that came to her mind was wacce

hanya zata bi ta juya wadannan kudaden su

kawo mata wasu?

Maman


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login