Showing 135001 words to 138000 words out of 375662 words

Chapter 46 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7982

ya samu

gida ya kama musu rent anan Abuja dan

baya son ya rabata da kasuwancin ta, shima

kuma yanzu yafi mayar da hankali akan

shagon sa na nan Abuja, na kanon mostly

kaninsa Ahmad ne yake handling.

Suma kuma su Hajiya Maryama da Alhaji

Nasir sunyi namijin kokari wajen zubawa

Safiya kayan daki na fitar kunya, yayin da

Sa'adatu ta shiga ta fita ta tabbatar cewa

bikin ya tsaru ya zama very unique and

classy babu wanda zai kushe sai dai idan

hassada ce yake yi.

3

2

9:04 PM

Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta

gata, amma Hajiya Maryama tace babu

abinda zata yi wa kanta "wannan auren da

zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki,

daga wannan karon kin bar hannun mu

kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun

mijin ki, amma still ina son ki sani cewa

muna nan anan gidan babu inda zamuje a

duk sanda kike bukatar wani abu ko wata

sharawa ki zo muna maraba lale da ke".

Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya

Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da

ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk

wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk

inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma

da zata je gidan ambassador Muhammad

Dikko, da ita taje,

Anan gidan Alhaji Nasiru aka daura auren

Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka

kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da

shekaru ashirin da biyar a duniya, A ranar

Safiya tayi kukan da rabon da tayi irinsa tun

kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da

Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta

gata, amma Hajiya Maryama tace babu

abinda zata vi wa kanta "wannan auren da

zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki,

daga wanna karon kin bar hannun mu

kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun

mijin ki, amma still ina son ki sani cewa

muna nan anan gidan babu inda zamuje a

duk sanda kike bukatar wani abu ko wata

sharawa ki zo muna maraba lale da ke".

Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya

Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da

ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk

wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk

inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma

da zata je gidan ambassador Muhammad

Dikko, da ita taje.

Anan gidan Alhaji Nasir aka daura auren

Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka

kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da

shekaru ashirin da biyar a duniya. A ranar

Safiya tayi kukan da rabon da tai irinsa tun

kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da

Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya

kuma adduoin da sai da suka saka ita kanta

hajiyan kuka tare da duk wanda yake gurin,

A haka Hajiya ta rungume ta ta kaita dakin

mijinta tana matukar jin dadi a ranta, ita ta

san Safiya a gurin ta investment ce,

investment din da ba a duniya zata samu

ribar sa ba, a lahira ne,[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: A big sorry to those that waited for

Safiyya yesterday

owner

A big thanks to those that checked up on

me

Some things cannot be explained.

21

6:49 AM

Safiyya

Episode Thirty One: The Legend

Safiya became very emotional tun da aka

kaita gidan miji, tun daga kukan rabuwa

da Hajiya kuma shikenan sai ta zarce

kullum kuka ta bar ango da aikin rarrashi,

amma shi ya fahimci zuwa lokacin ba wai

auren take yiwa kukan ba ko kuma

rabuwa da Hajiya ba, loneliness ne yake

damunta, tana missing din familyn ta

sosai. Ta koma kullum sai ta yi hirar su,

kuma da ta fara sai hawaye, Adam ya

fahimci abin nata har da survivors guilt, a

zuciyarta tana feeling guilt na cewa su

sun mutu ita kuma tana raye, and she is

living the life that idan da ace suna raye

ba lallai ne ta samu wannan rayuwar ba.

One week after the wedding ya tashi da

safe ya neme ta a dakin su ya rasa, yayi ta

zagaya gidan yana neman ta sai can ya

samo ta a backyard dinsu tana zaune a

kasa ita kadai tana kallon flowers din

gurin, ya je ya zauna a kusa da ita ba tare

da yace mata komai ba. Sun jima a haka

sannan ta juyo tana kallon sa da idanunta

da suka kumbura saboda kuka tace "da

kai aka je Kura ko su Baba ne suka je su

kadai?" Yace "da ni aka je" ta juya ta

cigaba da kallon flowers din sannan a

hankali tace "ina so zan je. In ka yarda".

Ya saka hannu ya jawo ta kan kafadarsa

sannan ya zagaye ta da hannunsa guda

daya yace "of cause we will go in kina son

zuwa, just tell me yaushe kike so muje" ta

kara kwanciya a jikinsa tace "jibi" suka

saka yin shiru zuwa wani lokaci sannan

yace "I saw the rooms, na ga dakunan da

suka fadi. Kasar tana nan har yanzu" tace

"I want to see it".

Kwana biyu bayan nan suka dauki hanyar

Zamfara da sassafe, dan tun kafin asuba

tayi suka fita sai a hanya suka tsaya suka

vi sallah. Su kadai kuma babu wanda suka

gaya wa. The drive was joyous as well as

emotional for Safiya saboda tana jin dadin

companion dinta amma kuma tafiyar tana

tuna mata tahowar da tayi zuwa Abuja

over 11years ago, a hanya hirar da kawai

take bashi, ranar har da hirar Baba and

the little she can remember about him musamman irin soyayyar da ya nuna mata

ita da yan'uwan ta. They talked about

yadda irin auren Alhaji Haladu da Baba

Hadiza yake random a cikin al'ummar mu

da kuma yadda irin auren yake affecting

zumunci a tsakanin yan gida daya. It is

halal tabbas, amma wata halal din ana

barin ta ko dan kunya da abinda zata

haifar nan gaba. Wani ma sai yayi retire,

da kudin gratuity dinsa zsi je ya auro yar

karamar yarinya ta zo kuma ta fara

haihuwa bayan sun gama girma matansa

kuma sun manyanta, sai kuma yazo ya

biye mata yayi ta yarinta yana bakanta ran

matansa da yayansa, wannan kuma sai ya

kara hura wutar kiyayyar amaryar da

kuma yayanta a zuciyar wadancan. A

karshe ya mutu ya bar baya da kura.

Su kuma yayan da aka haifa basu da laifi,

amma a karshe sune suke paying price

din abinda ba su suka siya ba.

Karfe 10 na safe a Gusau tayi musu, anan

suka tsaya suka samu wani eatery suka ci

abinci sannan suka dauki hanyar Kura.

Few minutes after that suna garin Kura,

Tun da suka shiga yayi slowing down yana

tafiya a hankali ita kuma tayi shiru tana

karewa garin kallo, nothing much has

changed tun barinta garin, except for few

houses da taga an gina an ld wadansu an

sake musu fasali zuwa na zamani amma babu wani major change a garin, dan haka

tar take gane hanya tiryan tiryan har kofar

gidan su.

Abinda ta fara gani shine tarin kasar da ta

kasance ita ce dakin da tayi spending

most of her childhood in. She could still

feel the moist, dark and suffocating

nature of the rooms, their laughter

together ita da kannnenta da Baba

Hadiza, sheshshekar kukan su idan suna

cikin bakin ciki, ta rufe idonta tana tuno

sound din kukan Khadijah sanda bata da

lafiya "Baba Hadiza ki kaini asibiti bani da

lafiya". Ta bude idonta tana jin echo din

hun Sauda a lokacin da mota ta kade

Baba Hadiza.

Ta juya da sauri ta kalli gurin, a idonta

tana gain gizon sanda motar ta daki

Baba Hadiza ta tashi sama sannan ta fado

kan kwalta. Ta tuna da yadda jini ya ringa

fita daga kan ta, yadda jinin ya jika ta ita

da Sauda. Ta bude tafin hannun ta tana

kallo, kamar mai kokarin gain jinin a jikin

hannun.

Adam ya saka hannun sa cikin nata yana

kallon yadda hawaye yake bin fuskarta

yace "kina so mu koma?" Ta girgiza kan ta

"no" sai ta cire hannun ta daga cikin nasa ta bude kofar ta fita.

Sai a lokacin ta lura da cewa mutanen

unguwar kusan kowa da yake gurin a

lokacin motar ta su yake kalla, irin anga

bakuwar mota ta tsaya kuma ba'a san

waye a cikin ta ba. Ta juya tana kallon inda

suke suyar awarar su ita da Sauda, a kofar

gidan makota, saboda basu isa su yi a

kofar gidan su ba.

Ta taka a hankali zuwa kofar gidan ta

shiga soron, yana nan shima yadda ta

sam shi sai dai ya kara lalacewa, katangar

duk ta tsatstsage, rufin ya taho zai fadi sai

itace aka saka aka tokare shi. Langa

langar da aka saka aka raba soron gida

biyu babu ita, haka jakankunan kayan su

da ta bari a wajan babu su suma. Daga

dukkan alama soron ma ba'a amfani da

shi yanzu dan dakunan su da suka fada

kuma ba'a gyara ba sun saka gidan ya

zama bashi da takamaiman mashiga.

Ta shiga tsakar gida tana bin gidan da

kallo, daga dakin da yake farko, dakin da

nan ne inda yake na Baba Hadiza sanda

Alhaji Haladu yana da rai, dakin da a ciki

aka haife ta taga wata mata da bata sani

ba ta fito ta a kallon ta "'baiwar Allah

lafiya? Daga ina?" Bata amsa mata ba ta cigaba da bin gidan da kallo.

Babban abinda ya ja hankalin ta a

chanjawar da gidan yayi shine bedroom

din Inna Sa'ade da taga ya rushe shima.

Sabon dakin da aka yi mata ginin bulon

siminti aka jingina shi a jikin nasu na kasa

har yayi sanadiyar lalacewar nasun kuma

yayi sanadiyyar rayuwar Sauda, shima ya

fadi, kuma daga alama ya jima shima da

faduwar, amma kuma kamar nasu shima

ba"a gyara gurin ba yana nan a bude, sai

ginin kasa da aka yi aka toshe kofar

tsakanin cikin dakin nata da falon ta.

Safiya ta wuce matar da har yanzu take yi

mata magana ta doshi kofar falon Inna

Sa'aden, kafin ta daga labule taji murya a

bayan ta, muryar yayanta Dauda "ke

wacece ne wai ana ta yi miki magana kinyi

wa mutane shiru?" Ta juyo da sauri ta

sauke rinannun idanun ta akan sa, ya ja da

baya kadan kamar wanda yayi gamo,

"Baba Hadiza?" Ya fada, sai kuma ya

chanja "Safiya?"

Bata amsa masa ba sai ido da take binsa

da shi. Muryar sa tana nan yadda take

bata manta ta ba, ta tuno sanda yace "ina

uwar ta ku? Ko bata dawo daga yawon

karuwancin ba?" Amma kuma kamannin

sa gabaki daya sun chanja, ya rame ya sirance yayi baki, kana ganin sa ka ga

wanda shaye shaye yayi wa kamun mutu

ka raba.

"Lantana! Lami!" Ya fara kwalla kiran

sunan yayyen su wadanda suke yaya ne a

gurin Inna Gaje. Lami ta fito daga dakin

Inna gaje da sauri tana gyara daurin zani.

"Kai lafiya kake min irin wannan kiran

mafarautan? Ba dai zan baka rancen wani

kudin ba dan. .

...." Sai kuma ta tsaya tana

kallon Safiya.

"Safiya" ta kira ta direct

"Safiya ke ce haka? Ke ce a gidan nan?"

Safiya ta tuno ta sanda take zazzagin

Baba Hadiza tana kuma kokarin dukan ta

a dai dai lokacin da aka dauki gawar Alhaji

Haladu. Ta kuma tuno ta sanda suke yi

musu watsi da kaya a waje suna cewa sai

sun bar musu gida, Baba Hadiza tana ta

kuka tana bin su tana rokon su.

Ta juyo sosai tana kallon ta ta kira sunan

ta ita ma "Lami" duk kuwa da cewa Lamin

da haife ta dan tana da yaya sa'annin ta.

Sai kuwa Lami ta rafka salati "jama'a ku

fito. Safiya ce a gidan nan jama'a. Ashe

tana raye. Jama'a ku fito ku ganta dan in

tabbatar ba gamo nayi ba" Dauda yace

"gani nima ina ganin ta kuwa? Wanne irin

gamo? Zamuyi gamo ni mu biyu?" Ta

watsa masa kallon banza "kai dalla can,

kai me idon ka yake gani in banda kwaya?

Ina kiran mutane masu hankali ne su zo su

taya ni gani" nan take sai masifa ta kaure a tsakanin su.

Safiya ta wuce su ta shiga dakin da take

ta hari tun da ta shigo gidan. Sai dai tun

da ta daga labule taji dakin yana wari,

wani wari kamar warin mushe. Ga duhu

tamkar dakin su na da saboda tagogin

dakin duk a rufe suke. Sai da ta dan jima a

tsaye a gurin sannan idon ta ya washe, a

lokacin ne ta ga mutum a kwance a kan

katifa a tsakar daki.

14

6

3

6:52 AM

Sama sama take jin murya tana kiran

sunan ta "Safiya? Safiya ke ce? Safiya" ta

durkusa a gaban halittar da take kwance

a gabanta tana kallon ta. Ta rame ta

motse ta yamushe, Inna Sa'ade ce.

Kafafuwanta duk guda biyun babu su an

yanke su. Daga jikin ta da kuma katifar da

take kwance a kai ne warin yake fitowa.

Sai dai bakin ta yana nan tas, kuma daga

dukkan alamu tana cikin hayyacin ta.

"Safiya daki na ne ya fado min ina kwance

ina bacci, kafafuwana duk duka kakkarye

sai da aka yanke su, Balarabe yayi

hatsarin mota ya mutu, sauran yaya na

duk sun gaji da kulawa da ni suna can

gurin matayen su, Sai Dauda shi kuma

babu abinda yake sai shaye shaye, komai nawa ya sace ya siyar ya sayi kayan shaye

shayen sa..

..." Ta cigaba da magana non

stop, kamar neman wanda zata yiwa

magana da ma take yi, kamar ta jima ba ta

yi magana da kowa ba.

Safiya ta mike tsaye ba tare da ta ce mata

komai ba ta doshi kofa. Sai da taje bakin

kofa sannan inna Sa'ade ta sake kiran

sunan ta "safiya"Safiya ta dakata sannan

ta juyo tana kallon ta, tace "ki godewa

Allah da Sauda mutuwa tayi ba ta zama iri

na ba. A wani lokaci mutuwa rahama ce,

ni yanzu neman ta nake yi taki zuwa".

Har ta koma tsakar gida ana cigaba da

rigima tsakanin Lami da Dauda. Ta wuce

su again ba tare da tace komai ba ta shiga

dakin Inna Gaje. Tana zaune akan

tabarma ita kadai tana ta maganganu

kasa kasa, har Safiya taje gabanta ta

durkusa bata san ta je ba, kuma Safiyan

bata gane me take cewa ba. Maganganu

kawai take yi marasa ma'ana. Ga tsufa ita

ma ta koma kamar tsumma. "Da yazo ya

dauki kazar sai suka tafi cikin ruwan

sama, kuma saniyar bata da ilimi, Allah dai

ya tona asirin takalmi, Amen Ameen"

Safiya ta mike tsaye tana cigaba da kallon

ta sannan ta saka hannu biyu ta share

hawayen fuskarta ta juya ta bar dakin.

Tana fita Lami ta sske kokarin tarar gabanta, ta lura yayan lamin suna zagaye

da ita, da alama zawarci take yi. "Safiya

ina kika je tsahon shekarun nan. Munyi ta

neman ki bamu same ki ba. Mun dauka

ma ba kya duniya" Dauda yace "ina taje

kuwa in banda yawon duniya, namiji ne fa

yanzu ya kawo ta a katuwar mota, a ina

Safiya zata samu shiga irin waccan motar

in dai ba yawon duniya take yi ba?" Lami

tace "dalla yi mana shiru, ka kalle ta mana

ka gani? Ko dan shaye shaye ya toshe

kwakwalwar ka. Bata yi kama da abinda

kake fada ba, kama take yi da matan

masu kudi. Ka sani ko mijinta ne? Ko aure

ta yi? Safiya kiyi min magana mana ina ta

yi miki magana".

Still Safiya bata ce komai ba, ta wuce ta

tsakiyar su taje ta hau ta kan kasar da

shekaru suka saka ta zaizaye ta zama

bata da yawa, ta fita daga gidan ta koma

mota inda ta bar Adam.

Yana tsaye a jikin motar yana kallon cikin

gidan, daga dukkan alamu hankalin sa

ba'a kwance yake ba, yana gain ta fito

yayi ajiyar zuciya sannan ya bude mata

kofa ta shiga ta zauna a dai dai lokacin da

yaya Malam ya kawo kai yana kokarin

shiga gidan, ya tsaya yana kallon motar

daga alama bai gane wacce ta shiga cikin

motar ba, Safiya ta bishi da kallo, yana

nan kamar yadda ta san shi, ssi dai

shekaru da suka karu akan na da, sai

kuma shekarun suka saka taga yayi mata

kama da baban su. Ta rufe ido tana

kokarin tuno wa da fuskar Baba, suna

kama sosai da yaya Malam, ta bude idon

tace da Adam, "Drive, please" ya taka

motar a dai dai lokacin da yaya Malam ya

gane ta yace "Safiya?" Amma bata amsa

masa ba kamar yadda bata amsawa kowa

a gidan ba.

Gidan Hajiya Kyauta tayi masa kwatance

suka je, Hajiya Kyauta tayi murnar ganin

su sosai dan dama bata samu zuwa bikin

nasu ba saboda bata jin dadi sosai. Suka

zauna suka yi hira da ita sannan suka ci

abinci. A lokacin ne take bawa Safiya

labaran abubuwan da suka faru a gidan

su, yayan ta Balarabe wanda Inna Sa'ade

take ji da shi a cikin yayanta ya mutu, ita

kuma kasar da ta kashe Sauda ita ce ta

lalata nata ginin na zamani sannan babu

zato babu tsammani dakin ya fado mata

ita ma cikin dare, abinda yayi sanadiyyar

kafafuwanta biyu duk sai da aka yanke su.

15

8

4

6:52 AM

Ita dama bata da yaya mata, yaya mazan

suka fara jinyarta kamar gaske daga baya

duk kowa ya kama gabansa sai Dauda da

yayi aure yanzu yake zaune a asalin dakin Baba Hadiza. Su sauran yayan daudan

suke aikowa kudi wai ya kula da

mahaifiyar ta su, shi kuma sai ya cinve

kudin. Hatta fitsari da bahaya a lokuta da

dama sai dai tayi su a kwance.

Inna Gaje on the other hand tsufa yazo

mata da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login