Showing 231001 words to 234000 words out of 375662 words

Chapter 78 - SAFIYYA Book Complete Hausa Novels Maman Maama.docx

10 Oct 2025

7994

/>
kulawa sosai. Sannan lokacin da Mukhtar ya fara cewa yana so na ta nuna amincewar ta da maganar dan har irin alkunyar nan ta fara nuna min ta surukai.

Da na ki karbar soyayyar sa, a bar gidan

su, sai dangantakar mu ta ragu sosai and I

did not blame her, babu uwar da zata so

ace ba'a son danta. But I thought she will

get over it with time. Sai kuma gani da

ciki, cikin shege, and sai kuma na zabi

Mukhtar din a matsayin wanda zan aura

to cover the cikin shegen da nayi. I think

kowacce uwa will do abinda Umma tavi ko

ma fiye da haka. Na fahimce ta. Wannan

kuma ya saka bani da grudges

whatsoever on her. And then uncle Ahmad. Uncle Ahmad bayan Daddy bani da wani father figure

kamar sa. Babu kuma wand aya

hidimtawa dukiyar Ammie da Daddy

kamar shi. He spent his entire life yana

aiki a karkashin su though not free tunda

duk abinda ya ke da shi daga gare su ne

but he gave it his best, Ita kuma dukiya

tana da zaki, mutane kadan ne zasu so

rabuwa da ita bayan sun dauki shekaru

suna juya ta. Wannan shi yasa ya nuna

goyon bayan saga aure na da Mukhtar

tun a karon farko, wannan kuma shi yasa

har a last zaman da muka yi ya ke cigaba

da kokarin cusa min Mukhtar din dan yana gain aure na da Mukhtar zai saka ya cigaba da juya dukiyar kuma ko babu ransa to dansa da jikokin sane akan

dukiyar, in babu raina ma sune zasu gaje

ni. Amma kuma bashi da hannu a cikin

abinda Mukhtar din yayi. Nayi kokarin dawo da hankali na kansu, har lokacin suna ta tafka rigima da

Mukhtar, na lura cewa ba karamin maruwa

fuskar Mukhtar tayi a gurin Uncle Ahmad

ba dan fuskar har tayi ja ta fara kumbura,

amma da yake ba shi da kunya still bai yi

shiru ba. Na juyar da kaina gefe na daina kallon su.

Na dauka uncle Ahmad zai cig6da

dagewa a kan abar aurena da Mukhtar, sai

kuma na lura cewa yanzu ya fahimci

hakan ba mai yiyuwa bane ba ya hakura.

And by submitting his resignation letter

yana nufin ya sallama komai ya kuma

hakura da komai. Da gaske uncle Ahmad huce haushin sa yake yi akan Mukhtar, dan bayan marikan

da yake zuba masa har da kafa ya saka ya

ke dukan sa. Ni dai sai na mike tsaye nayi

cikin gida na barsu anan. Na gama kuma

da wannan shafin. Ban yafe wa Mukhtar

ba kuma bana jin zan yafe masa. Amma na bar shi da Allah, na kuma san hukuncin da zai yanke masa yafi wanda alkali zai yanke masa idan na kai shi court.

Maman Maama✍🏻

Ina yan soyayya? Next post zamu tabo

muku Malam Muhammadun ku insha

Allah. Allah ya sa kar ya bada ku kuma😅[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty Seven : The Decision

*Free baking master class*

I'll be sharing delightfully delicious

recipes including how to make soft and

fluffy doughnut for *free* it's completely

free A-Z

Click the link below to join

Females only

https://chat.whatsapp.com/

DN5w2VPGPhE0gf3700F9k0

0704248974

Zan koyarda snacks kala 8 kyauta

acikinsu akwai yadda zakiyi doughnut me

laushi da dadi classes dinnam kyauta ne

daga farko har karshe

Danna wannam link kiyi joining

Mata kawai

Or contact

07042486974

To be added

https://chat.whatsapp.com/

DN5w2VPGPhE0gf3700F9ko

Safiyya.....

Ranar kwana nayi banyi bacci ba ina saka

da warwara, a fahimci abinda Daddy

yake nufi, amma sai dai kuma fahimtar ta

sa ta toshe min hanyar da na biyo kuma

na kasa ganin wata hanyar da zata bulle

da ni xuwa destination dina. Na tashi nayi

sallah na gaya wa Allah bukata ta na roje

shi ya bani mafita tunda dai ni bani da ita.

Sai wajen asuba na kwanta akan sallayar

nayi bacci, bayan anyi sallah na tashi nayi

sallah sannan na koma kan gado na

kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni.

Ban farka ba sai da rana tayi sosai. Na

tashi nayi wanka na shirya ina jin kaina

yana yi min ciwo duk kuwa da cewa nayi

bacci mai nauyi amma na san damuwa ce

ta saka min ciwon kan. Na dauko waya ta

ina dubawa sai na ga sako daga Abdul

yana yi min mitar bana neman su sai in

sun neme ni "munyi fushi" ya turo tare da

hoton Junior ya bata rai ya turo baki, Sai

na samu kaina da yin dariya, He looks so

cute and innocent and doesn't deserve all

this, Na shafa fuskar sa ta cikin wayar sai

nace a hankali "hey you, It is going to be

okay. You are going to be okay, I promise"

Nayi replying Abdul tare da tsokanar sa

ina tambayar sa labarin amarya. Sai kuma na tashi na tafi part din Daddy dan gaishe

shi. Ina shiga na tarar da shi a falon sa

tare da Mustapha suna gwada wani

machine da aka siyo masa da zai taimaka

masa wajen zama da tashi ba tare da an

rike shi ba. Na zauna a gefe ina kallon su.

Mustapha might be a bad person but he

takes care of Daddy and I am greatful to

him for that.

Sai da suka gama sannan na karasa gurin

sa na gaishe shi sannan nace '

"sai yanzu na tashi. I slept in" ya zauna yana haki

saboda movements din da yayi sannan

yace min "maybe baki yi bacci da dare ba

ne ba ko?" Na sunkuya da kai nace "haka

ne Daddy. Ina ta tunani ne. I am still not

sure what I will do" yace "kin ci abinci?"

Na girgiza kai "no, shigowa nayi da ma mu

gaisa sai inje inci abincin" yace "good. Sai

kuma yayi shiru ya kwantar da kansa tare

da rufe idonsa,

Har na fara tunanin tashi ina gain maybe

bacci ya dauke shi sai kuma na ga ya

bude ido yana kallona yace "na taba baki

labarin siblings din Ammien ki?" Na gyara

zama, ina son labarin Ammie ko a gurin

waye ballantana a gurin Daddy, A gurin sa

da sauran mutane na hada labarin ta.

Nace "wanne labarin da ga ciki? Na yadda

suka yi sanadin rasuwar baba Hadiza da su Sauda ko kuma na yadda suka biyo ta

nan suka takurawa rayuwar ta?" Ya girgiza

kai yace "na abinda ya faru da su bayan

rasuwar ta" nace "Daddy you never talk

about anything related to rasuwar Ammie.

Labaran ka duk na sanda tana raye ne ba

ka taba bani labarin lokacin rasuwar ta ko

abinda ya far bayan rasuwar tata ba".

Yayi shiru yana kallon tv amma ba wai tvn

yake kalla ba. Ya dan jima sannan yace

"tabbas yan'uwa Safiya sun tsane ta ita

da yan'uwan ta, tsanar da har ta kaisu ga

aikata abubuwa da dama wadanda suka

zama sanadiyyar da Safiya ta rasa kowa

nata. Sannan kuma sai Allah ya daukaka

ta fiye da yadda bata yi tunani ba, fiye da

yadda suma ba su taba mafarki ba, and

they came back, zuciyoyin su still cike da

tsanar ta, they threatened her life, suka

kira ta da juya, suka kuma bita da

mugayen maganganu na sharri".

"A lokacin a irin daukakar da Safiya take

da shi idan da taga dama zsta iya batar da

su a duniya baki daya, idan da taga dama

zata iya kai su kara ta lissafo irin

abubuwan da suka aikata mata and she

can get a good lawyer da zai iya rufe mata

duk wanda yake da hannu a cikin abinda

ya same ta. But she didn't do that. She said sanda ta shiga gidan su yaga yadda Allah ya mayar da su ita kuma ta ga yadda Allah ya mayar da ita sai ta san

cewa Allah has already fought her battle

for her. Bata bukatar revenge. Ya riga yayi

mata. Amma sai ta ja jikinta daga gare su

dan gujewa sharrin su. Ko sanda suke

zuwa gidan nan. A cikin gidan nan sun

taba gaya mata ido da ido cewa tunda ita

juya ce bata haihuwa suna jira be ta mutu

su ci gadon ta. She could have sue them

a lokacin, but she didn't. She said taga

abinda Allah yay musu wancan karon,

wanna karon ma shi take jira yayi mata

komai. She just took some protective

measures and leave them with God".

"And then she died"

"Washegarin da ta rasu suka zo gidan

nan, Bus guda suka yo shata daga Kura

suka taho mazan su da matan su, yara da

manya, Sanda suka zo aka gaya min sai

nace a barsu su shigo, Na saka aka basu

dakuna biyu, maza aka basu daya a waje

mata kuma aka basu daya a cikin gida,

Amma tun a lokacin sai suka tayar da rigimar su dakunan ta suke so a bude musu a sama su a dakin ta zasu sauka. Lokacin kina ta koke koken ki na neman

mahaifiyar ki Sa'adatu da sauran mutane

suna ta fama da ke amma su ko a kin su.

Hajiya ta san ba alkhairi ne ya kawo su ba

dan haka ta hau saman ta rufe dakunan ta

rike key a hannun ta. Shikenan sai rikici.

Suka kafa maganganu na rashin mutunci

da izgilanci suke yiwa Hajiya, Sa'adatu

kuma da sauran mutane suka shiga ciki,

sai rigima ta tashi a gidan gaisuwa"

"Ni ina can ina cikin matsananciyar

damuwar abinda ya faru naji hayaniya. Ina

ji dama na san sune. Nan take na kira

police suka zo suka kwashe su

gabakidaya suka tafi dasu. Sai da suka

kwana a can. Ahmad ne yayi ta zirga-

zirga sannan daga baya nace a sake su

amma kar su dawo min gida. Su barni inji

da abinda yake damuna".

"Suka tafi din, amma basu hakura ba

ranar sadakar bakwai sai gasu sun dawo,

Mutane sun taru ana yi mata sadaka da

adduoin neman rahamar ubangiji amma

tun daga bakin gate suka fara zage zage,

wai suna so suga uban da zai hana su

shiga gidan, ai gidan ma yanzu nasu ne, ai

ance musu dama gidan tane kuma su ne magadan ta dan haka sun zo karbar gadon su. Har nayi niyyar sake kiran police sai Alhaji Nasir ya hana ni. Ya aika

aka shigo da su ya zaunar da su yace su

zauna avi mata addu'a tare da su sannan

sai a saurari maganar da suka zo da ita".

"Aka gama zaman addu'a aka tashi. Suka

sake zama da Alhaji Nasiru suka gaya

masa sun zone karbar dukiyar da ta mutu

ta bari, har da list din su a hannu na

abubuwan da aka gaya musu ta mallaka.

Alhaji Nasiru ace babu komai dama ai shi

gado Allah ya riga ya raba shi. Su je su

samo malamin da zai raba gadon sai su

zo a raba a basu. Suka ki tafiya, dan

sunce ko kudin motar da zasu koma kura

basu da shi jira suke sai an basu su samu

na mota a ciki, Alhaji Salisu ya sama musu

gurin zama, sannan ya nemo alkalin da zai

raba gado ya kawo ya hada su dashi,

sannan ni kuma aka ce in bayar da abinda

ta bari wanda za'a raba".

"Ban je gurin ba dama nace ba zan je ba,

sai na tura barrister Umar da sauran

lawyers din ta suke managing affairs dinta

suka je, suka gabatar da lissafin

abubuwan da ta mutu ta bari wadanda

suke nata. Wadannan sun hada da

wadansu daga cikin kayan sskawarta, sauran tarkacen irin na mata, da kuma kudin da yake cikin account din ta. Ko mota bata da ita. Nan take sabuwar

rigima ta rikice dan ma Allah yasa na gaya

wa barrister su tafi da security dan babu

abinda ba zai iya faruwa ba. Ai kam dai

ance Dauda wuka ya fitar yace sai ya illata

barrister Umar".

"Nan take suka shigar da kara Court akan

an cinye musu gadon yar'uwar su data

mutu ta bar musu. Zama daya aka yi wa

shari'ar alkali ya kori karar tunda basu da

hujjar cewa wadannan kadarori da suka

lissafa nata ne. Dan ga takardu lawyers

din mu sunje da su da suke nuna duk

kadarorin nan naki ne ba nata bane ba.

Daga nan suka sake kai kara kotun

musulunci. Sunce waccan kotun kafurci

ake yi a ciki. A wannan zaman court din

ne naje, na kuma yiwa alkali bayanin duk

abinda Safiya tayi sanda tana da rai kuma

cikin koshin lafiyar ta. Ta baki kyautar komai da ta mallaka kuma ke ce kadai yar ta a duniya. Na kuma nuna masa abinda ta mutu ta bari a matsayin

nata. Sannan nace ni da ke mun yate

gadon Safiya, abinda ta bari din mun bar

musu su rike"

"A take alkali ya tabbatar musu da cewa

Musulunci ya yarda da abinda Safiya tayi,

dan haka abinda na nuna musu din shine

kawai abinda za'a raba a matsayin gadon

ta, sannan kuma yace ni da ke musulunci

bai bamu damar cewa mun yafe gado ba,

ba'a yafe gado, dole sai an bamu sai dai

in an bamu mu bayar in bama so"

"Still sai suka tayar da rigimar wai ai kayan

sakawa kadai na fito da su banda kayan

daki, su sun san cewa kowacce mace

tana da kayan dakin ta a gidan mijinta dan

haka sai na fito da su gado da kujeru da

sauran su ai suma kayan ta ne. Ni kuma

na san sanda na sayi gidan nan na saka

aka zuba komai a cikin sa, tabbas safiya

ta sai abubuwa itama amma ba ma

zanniya ware abinda ta siya da wanda na

siya ba dan haka nace su zo su dauka.

Ahmad yana ta bala'i nace ya barsu suzo

su dauka. Na zo gida na kwashe duk

abinda na san mai daraja ne kuma ta baki

tun tana da rai, irin su gwala-gwalai da

manyan suturu da designer perfumes din

ta duk na adana a bangare na, Duk abinda

yake bangaren ta kuma nace azo a dauka,

Hatta carpet da labule ba'a bari ba sai da

suka cire, Hatta cutlary set sai da suka

dauke daga kitchen. Cokali basu bari ba,

Har da mugunta, abinda aka ga ba zai

dauku ba sai a fasa shi. Ban ce komai ba

dan ni ta kaina nake yi. Duniyar ma ta fita daga kaina ballantana kayan da suke cikin

ta. Suka kai alkali aka yiwa kaya kudi aka

fitar da nawa da naki sauran aka basu. Ni

dai ban sake komawa court din ba.

Abinda aka bamu ma nace da Ahmad yaje

yayi sadaka da su Allah ya kai mata ladan

kabarin ta. Daga lokacin naji gidan gabaki

daya ya fita daga kaina ba zan iya cigaba

da zama a cikin sa ba. It holds a lot of

good and bad memories for the both of

us dan kema a lokacin kamar kinfi kukan

neman ta in muka shigo gidan. A lokacin

ne na yanke hukunci komawa Kano da

zama to ease the pain for us".

Yayi shiru yana hutawa, idon sa yayi ja,

har yanzu mutuwar Ammie tana damun sa

sosai and I couldn't imagine going

through the pain of loosing her at the

same time kuma da wannan bacin ran na

yan'uwan ta. Ga kuma ni da na saka shi a

gaba da rigima kullum.

Muka cigaba da yin shiru sannan nace

"Daddy to ba ka gaya min ba" yace "ban

gaya miki me ba?" Nace "sanda zaka fara

magana kace zaka bani labarin abinda ya

faru da su bayan rasuwar ta. Menene ya

faru da su?" Ya dan yi gyaran murya yace

"a labarin da aka bani, Tun a gaban alkalin

da ya raba gadon suka fara rigima akan

abinda aka basu, matan suna ta zabar

kayan sakawa daga cikin kayan da suka samu. Sai babban su, Yaya Malam, ya kwace komai daga hannun kowa yace su bari sai sun je gida sai suyi nasu rabon.

Ya dauko shatar motar diban kaya aka

kwashe duk kayan aka zuba a ciki, cash

din kuma ya karba ya rike a hannun sa, su

kuma suka shiga mota suka koma Kura

gabakidayan su"

"Daga baya Jamilu dan marigayiya Hajiya

Kyauta, shi yake bani labarin abinda ya

faru da su. Yace bayan sun je gida suka yi

ta jiran motar kaya tazo shiru shiru mota

bata zo ba. Tun suna tunanin matsala

motar ta samu a hanya har suka fara

tuhumar yaya Malam akan inda kaya suka

makale, da farko yayi ta basu uzurirruka

masu cike da karaiyayi. Daga baya bayan

an debi tsahon lokaci ba tare da kaya sun

zo ba sai suka hada kai suka je gidan sa

suka ritsa shi suka ce lallai sai ya fadi inda

kaya suke, a nan ne yaga babu sarki sai

Allah sai yace musu kaya dai ya siyar da

su, kudin kuma ya biya lawyer din da ya

dauka ya tsaya musu a court, kudin

hannunsa kuma da su ya biya kudin

shatar motar da suke je suka dawo da

kuma motar da aka dauki kayan, Dan haka

babu wani abu da ya rage wanda zai basu”.

"Wannan maganar ta bata musu rai sosai,

a take Dauda ya cire wuka ya soka wa yaya Malam a kahon zuci, a take ya fadi ya mutu, yan sanda kuna suka kama Dauda, bayan anyi shari'ar sa sai aka

yanke masa hukuncin daurin rai da rai". Ya sake yin shiru yana kallon expression din fuska ta. Ban taba tunanin wannan ne abinda ya faru da su Dauda ba ban kuma taba damuwa da lallai sai na san wani abu

a game da su ba. Lallai Allah mai yawan

hikima ma a cikin dukkan al'amuran sa.

Daddy yayi murmushi yana lura da yadda

labarin ya taba ni sai yace "ina fatan kin

gane abinda nake so ki fahimta a cikin

wannan labarin. When you leave all your

battles in God's hand, God will fight all

your battles for you. Za kuma ki samu

justice din da baki taba zata ba,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login