Showing 21001 words to 24000 words out of 72709 words
Chapter 8 - AUREN HADI COMPLETE DOCUMENT WRITING Samira Haruna.txt
zafi a jikinshi, hawayene ke bin fuskanshi a hankali yake fad'in" bazan yafe maki ba har abada, shekara d'aya kenan rabon da naji irin haka, amma gashi yau na kusa mutuwa saboda kin shigo rayuwata, kin kusa tarwatsani."
" Dole na koma gida kafin na aikata ba daidai ba, dole naje gida na samu alhaji na rok'eshi ya auramin nuseiba kafin na mutu, wallahi ke kuma sai kinyi kuka da idonki muguwa marar imani, ba zan saké kallonki ba daga yau harna mutu."
_Salman kuma haka abin ya zama🤔_
*Ummi* na zaune d'aki, number naga tana danna kira tana kashewa, tun tuni haka takeyi kamar wasan yara, d'aga kanta tayi sama tana fadin" miyake damuna, miyasa na damu da tunaninsa, miyasa na kasa mantawa da maganar aurenshi, miyasa nake jin haushinshi dan zai k'ara aure?"
Siraran hawayene suka biyo kuncinta, a hankali ta saké fad'in" ni dai nasan bana son yaya Salman domin kuwa da muguntarshi ya raine ni, haka kuma ba ban tab'a jin koda k'aunarsa ba a zuciyata ba, to miyasa?" kukan da tafe dashi ya jawo hankalin jawahir dake zaune ita da khamis suna hira, tashi tayi ta shiga d'akin ta zauna kusa da ita ta fara magana.
"Ummi sai yanzu ne nagane wani abu, ban tab'a tunanin zaki iya b'oyemin wani abu daya shafeki ba, na d'auka ni da ke d'aya ne zaki fad'amin komai dake damunki, kamar yanda nake fad'a maki abinda ke damuna kuma na nemi shawarar ki, ashe ke ba haka bane a wajenki"
" Ki duba ki gani mana, yaya Salman ya amince da kizo gida na ki zauna, bayan kuma ga k'anwarshi nan khairat, ga hafsat da nadia duka suma yan uwanshi ne amma baice kije can ba,sai yace kizo nan, miyasa yace haka?"
Ci gaba tayi da fad'in" saboda yana ganin munfi kusa da juna shiyasa, yasan kuma babu abinda zai dameki anan inhar muna tare, amma gashi yanzu kina cikin damuwa tsawon kwana uku, ba kicin abinci sosai sai kuka kike amma kin 'ki fad'amin damuwar ki saboda kina ganin ban kai nasani ba."
Kai ta girgiza mata tace" a'a jawahir ba wai baki kai bane, saidai bansan ta yanda zaki fahimce niba, ni kaina bansan miye yake damuna ba, bansan akan mi nake damuwa, saidai nasan za kimin dariya kuma ki fahimceni ba daidai ba idan na fad'a"
05/03/2019 à 17:28 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑
_Samira Harouna_
_My 🅱K *BILKISU Z. YA'U* murnar kammala wannan littafi naki mai sunan *SO MAHA'DIN RAYUWA* ha'ki'ka ya fad'akar ya nishad'antar, musammam ma a wajen mu 'yan soyayya, ina maki fatan alkairi ina rok'on maki Ubangiji da ya yafe maki kurakuran dake cikin wannan littafi, inda ki kayi dai-dai kuma Allah ya baki ladar fad'akarwa_👏👏👏
_Sai mun jiki a novel na gaba mutuniyata 'yar hannu dama na, ina mugun sonki BK ta_
``` daga samirar ki rabin ran bloodynki```😜
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
*Page*
5⃣3⃣-5⃣4⃣
Jawahir tace" haba Ummi, ta yaya zan fahimceki ba daidai ba, ki fad'amin insha Allah zanyi k'ok'ari na fahimta yanda kike nufi" cikin kuka ta fara mata bayanin abinda take tunani.
"Jawahir bansan miyasa nake jin haushin yaya Salman ba tunda yaya Khamis ya fad'amin zai k'ara aure, na rasa dalilin tsanarsa nidai nasan ba kishinsa nake ba domin kuwa bana sonshi kuma bana k'aunarshi, to amma miyasa nake damuwa bansani ba" saida ta goge hawayen da suka zubo mata taci gaba da cewa.
" Jawahir wata'kila wannan itace 'kaddarar rayuwata, har abada bazan samu abinda nake so ba, da farko an min AUREN HA'DI da wanda bana so ba tare dana shirya ba, a bisa d'an k'ank'anin kuskure akamin dukan tsiya aka kawo ni gidan miji babu shiri, to yana iya dole na hak'ura tunda banda yanda zanyi, Jawahir dama bana tsammanin cin amarci ko farin ciki a tare da yaya Salman, saidai ina buk'atar na samu 'yanci kamar kowace mace mai ji da kanta, amma ina na kasa samu azabtar dani kawai yake a gidansa, ya tafi ya barni ko sati banyi a gidansa ba, shine yanzu zai k'ara aure dan yaci mutunci na, shin Jawahir kinsan mai zai faru idan ya k'ara auren nan?"
Kai ta girgiza, ci gaba tayi da cewa" zai kawo min Nuseiba a matsayin amaryarsa, yarinyar da bana jin ta cika shekara shabiyar a duniya, zata fini matsayi da 'yanci a gidanshi saboda ita yana sonta, cikin k'ank'anin lokaci zata fahimci zaman da muke da shi, daga nan saita fara jin ta fini sannan itace mowa a wajen mai gida hakan zaisa ta fara min gani-gani."
"Bayan wani d'an lokaci kuma zata samu ciki, kinga daga nan komai zai k'are, domin kuwa zata fara min gori akan hakan shi kuma zai dinga biye mata, d'awainiyarta hidimarta rainon cikinta zai zama duk nice, idan kuma na'ki nasha duka haka harta haihu daga nan zata fara min gorin haihuwa lokacin shi kuma ya d'auki soyayyar duniyar ya d'ora akan d'anta da ita kanta, zai dinga fita da su duk inda zaije koda barin garine, ni kuma zan zama 'yar gadin gida har lokacin da tawa zata zo k'arshe." kallabinta ta kama ta rufe bakinta da shi taci gaba da rera kuka.
Da k'yar Jawahir ta rarrasheta tayi shiru, kafin ta fara magana" 'yer uwata kiyi hak'uri, insha Allah duk abinda kika fad'a ba zai faru ba, ke da yaya Salman da Nuseiba duka 'yan uwane ku, babu wanda zai cutar da wani, kuma ni bana tunanin auren zaiyiwu, saboda yaya Khamis bayasan maganar gaba d'aya."
Kallonta Ummi tayi tace" dan yaya Khamis baya so, ba shi ke nufin zai fasa abinda yayi niyya ba." kafad'arta ta dafa tace" to naji ma ace ya aureta, miye Nuseiba keda shi da har zaki tashi hankalinki? ni kaina k'anwa take gareni, bare kuma ke da kika ban shekara d'aya, kinga kenan k'anwarki ce kema." wani murmushin kan labb'a tayi tace"Jawahir bakisan kishiya bane shiyasa, bata kad'an kuma bata k'arama"
Dariya jawahir tayi tace" yanzu ke harkin fara kallon nuseiba a kishiyarki? ai 'yer uwarki ce" hararanta tayi tace" lokacin da zata shiga tsakanina da mijina ba baki sani ba"kallon mamaki ta bita dashi tace" Ummi kece kike kiran yaya Salman mijinki, to inaga fa kamar anjima da kashe boss" da gudu tabar d'akin saboda dukan da Ummi takai mata.
Kwance ta koma tare da d'aukar pillow dake gefenta ta rumgume, a hankali take tariyar rayuwarta a gidan Salman da tayi.
_Tambayoyi ne ta jero ma kanta" miyasa nake damuwa, miyasa nake jin haushin shi dana Nuseiba, miyasa nake jin zafi a zuciyata, miyasa nake so naji muryarsa, kuma miyasa na kasa kiranshi?"_
😜😜😜 ```in bata amsa, koko cikin ku akwai wanda zata bata?```
_Ma chérie ta Hakima fito mucashe, lokaci ya kusa yan bak'in cikin Salman saidai a mutu😉😜_
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑
_Samira Harouna_
_My seeya fatan alkairi da godiya tare da addu'ar ya fiyar Ubangiji a bisa kurakuran da ki kayi, daidai kuma Allah ya baki ladar fad'akarwa da ki kayi, *BAMU DACE DA JUNA BA,* darasi nishad'antarwa tare da ilimi da fad'akarwa ne a cikin shi._
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜_ 🤛
*Page*
5⃣5⃣-5⃣6⃣
Tunda safe haka Ummi ta tashi sukuku jiki babu k'wari, Jawahir ce ta fad'ama Khamis halin da take ciki, kiranta yayi tana zuwa da kanshi ya zuba mata abinci a plate ya aje mata tare da fad'in" maza cinye ki bani plate d'in"
Kallonshi tayi tace" yaya Khamis ko zanci ba zan iya cinye wannan ba" yanda ya had'e rai yace" Ummi ina wasa dake?" kai ta girgiza tace" kayi hak'uri yaya Khamis wallahi yamin yawa"
"Ke, ina wasa dake ne, za kici ko saina takaki?" tsawar daya mata ce tasa tayi saurin jan plate d'in a gabanta ta fara kai loma baki, Jawahir ma 'yan cikinta ne suka kad'a, haka nima saida na saki alk'alamin.
Tana ci tana kuka tana rok'onshi ya isa haka, amma ya tsareta saida ta cinyeshi duka ta bashi plate d'in, tunda uwar Ummi ta haifeta bata tab'a cin abinci mai yawan haka, shiyasa Khamis na fita Ummi ta fara tsula amai, abin ya d'aga hankalin Jawahir dan da farko tayi tunanin idan ta amaye abinci zata daina, amma sai taci gaba da shek'ashi.
Cikin tashin hankali ta fara kiran Khamis ta fad'a mashi halin da ake ciki, cikin tashin hankali yace da ita "gani nan zuwa saimu kaita asibiti"
suna jiranshi Salman ya kiran Jawahir dan tunda ya tashi bai fita ba, gab'a d'aya hankalinshi ya koma gida, hakan yasa ya kira iyaye maza da mata da kakannin amma saiya ji baibar kewa da damuwa na gidan ba, dole ya kira Jawahir ya tambayeta Ummi.
Tana d'auka cikin damuwa tace "assalama alaikum, ina kwana yaya Salman?" gabanshi yaji ya fad'i, da k'yar ya daure yace "lafiya lau, kun tashi lafiya?"
Kamar zata fashe da kuka murya na rawa tace "yaya Salman da sauk'i dai, kaga Ummi nan tana ta amai wallahi, nifa na fara jin tsoro" cikin d'aga sauti yace "amai kuma, miyasa meta to?"
Cikin kuka tace "yaya Salman daga taci abinci fa shine take amai "innalillahi wa'inna illaihir raju'un, kinga bata wayar" ya fad'a tare da nuna tsantsar damuwarshi a fili.
Mik'a mata wayar tayi, wata harara ta wurga mata tare da kau da kai, maida wayar tayi a kunne cikin sanyin murya tace "yaya tak'i karbar wayar" abun mamaki na d'auka Salman zaiji haushine, amma sai naji yace "Jawahir karki min k'arya, ki fad'amin abinda ke damunta?"
"Yaya Salman nima bansan miyake damunta ba, amma dai jiya ta fad'amin wani abu wanda nake tunanin kaine silar shigarta wannan halin" cikin rashin fahimta yace "bangane ni nasa taba?"
"E yaya Salman amma kayi hak'uri nima zato ne nake, amma banda tabbaci" cikin jin haushi Salman yace "naji ni fad'amin me ta fad'a maki?"
Duk da tana d'ard'ar dashi haka ta daure ta fad'a masa duk abinda Ummi ta fad'a mata jiya, dariya yayi yace "Jawahir lallai yarinya ce ke, waya fad'a maki ana kishin wanda ba'a so?"
Saida ta sauke ajiyar zuciya tace "yaya Salman ai macen kenan, tsamar dake tsakaninku ba zata hana zuciyoyinku fallasa sirrin dake cikin taba, ko bata sonka zata iya kishinka saboda akwai aure tsakaninku, kamar yanda da zaka ganta da wani namiji za kaji zafi a zuciyarka, amma idan aka fahimci hakan zaka iya wayancewa ta hanyar cewa kana san kare martabar aurenka ne dake kanta, kaga kenan dan tayi kishinka ba abun mamaki bane."
Shiru yayi yana tunanin abinda ta fad'a, murmushi yayi kamar yana gabanta yace "Jawahir ban tab'a jin alamun haka a raina ba, ko zanyi soyayya zanyine da wata daban amma ba Ummi ba, yarinyar da idan naganta sai gabana ya fad'i saboda tunanin abinda zata min musammam idan ina cikin mutane"
Dariya tayi cike da jin k'arfin gwiwa tace "Yaya Salman ai fad'uwar gaba alamune na so" dariya yayi yace " ke Jawahir banasan sharri, ke har kinsan alamomin so?"
Dariya tace "na san wasu yaya Salman wanda nake ji a duk lokacin da naga yaya Khamis" cewa yayi "to fad'amin uku daga ciki, kuma idan ki kayi ba daidai ba to idan nadawo dole kisha rank'wasa a kai"
Hannu ta d'ora a kanta dan bâ zata manta rank'wasan daya tab'a mata ba har saida tayi ciwon kai, cewa tayi " yaya Salman duk lokacin da kaji gabanka ya yanke ya fad'i a lokacin da gaka wata 'ya mace, to alamune na zuk'atanku suna shirin k'ulla wata alak'a koda ku baku shirya hakan ba.
"Sannan lokacin da kaji komai na wata 'ya mace yana burgeka, komai yana nufin dariyarta, murmushinta, fara'arta, kai dama kukanta to shima akwai yiwuwar ka kamu da sonta ko kana shirin kamuwa."
"Yaya Salman akwai jin tausayinta duk lokacin da wani abu ya sameta na rashin jin dad'i, haka kuma akwai son ganinta a cikin farin ciki tare da mata fatan farin ciki mai d'orewa, son jin sautin muryarta a koda yaushe, son ganinta a kusa da kai a kullum."
"Yaya Salman duk lokacin da kayi nesa da ita tunaninta zai iya hanaka sukuni, zaka kasa komai burinka bai wuce ka dawo ka ganta ba, zaka ji kewarta na yawan damunka kana buk'atar kasancewa da ita, sannan yaya Salman duk wacce kake so za kaga murmushin da kake mata ma na dabanne, haka kallon da kukewa junanku ma zuk'atanku ne kad'ai zasu iya fassarashi, don ko mai kallonku ba zai iya fassara maku shi ba."
"Ke" ya daka mata tsawa yana fad'in" nawa na tambayeki ni uku fa nace, waike sarauniyar soyayya ko?" kai ta girgiza alamar a'a, tace " yaya nadai fad'a maka abinda na sani ne kawai, amma ina so ka sani kai da Ummi koda baku son junanku, to ku sani akwai jinin 'yan uwantaka da yake yawo a sassan jikinku wanda baku isa ku cireshi ba, ko babu so a tsakaninku akwai k'auna, yaya Salman abune mai sauk'i samun masoyi, amma samun wanda yake k'aunarka da gaskiya shine mai wahala, mafiyawancin soyayya tana farawane daga k'iyayya sannan ta koma so wannan shine."
Kashe wayar yayi ba tare da sunyi sallama ba, maida kallonta tayi ga Ummi dake kwance tana bacci, Khamis na zuwa Ummi tace taji sauk'i, dan babu abinda ta tsana kamar shan magani da allura, dole suka k'yaleta da sukaga jikin yayi sauk'i ta daina aman.
_Wato dai 'yarta bakin Salman baki son shan magani sai abun dad'i_😂
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑
_Samira Harouna_
*MEELAT*_(my meelat)_
*HEENAT*_(my heenat)_
*CHOUKRA*_(habibaty)_
*FATIMA*_(mom dady)_
*HALIMA*_(kakale ta)_
*SAFIYA*_(ma chérie)_
*AZEEMA*_(k'awata)_
*RAMATOU*_(rammess)_
*MAMAN LABYB*_(momy na)_
*MOMYN SULTAN*_(aunty)_
*MOMYN DEEJA*_(ma belle)_
*HAWA JAMIL*_(aunty na)_
*HAKEEMA*_(ma chérie)_
```WANNAN PAGE SADAUKARWA CE GAREKU, DAN HAKA KUYI YANDA KUKE SO DA ITA TAKU CE KYAUTACE DAGA GARENI```
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
*Page*
5⃣7⃣-5⃣8⃣
Yanda Salman yaga rana haka yaga dare ba tare daya rintsa ba, kalaman Jawahir sun gigita tunaninshi sosai ya kasa fayyace gaskiya da k'arya, indai har fad'uwar gaba yana d'aya daga cikin alamun so, to kenan tun Ummi na matashiya yake sonta, domin ko duk lokacin daya ganta sai gabanshi ya fad'i sannan baya jurar kallon idanunta, suna sashi yaji wani yanayi a tare dashi, hakan ma yasa yake kiranta da mai idon aljanu kona mage wani lokacin.
Ya yanke shawarar komawa gida jibi, dan haka ya ciro ticket haka ya k'agu safiya ta waye ko ya kama hanyar gida,yayi niyyar bankad'o gaskiyar abinda Jawahir ta fad'a masa zaiyi k'ok'arin gano gaskiya ta hanyar lalubo kishin Ummi sannan yasan dalilin kishin nata.
08:00 na safe suka kamo hanyar zuwa niamey, banda kallon pic d'in Ummi babu abinda yake, ko abinci baisa a bakinshi har suka sauka, duk da gobe zai wuce amma yayi niyyar bazai fad'ama kowa ba yana so ya masu bazata, sannan yaga yanda Ummi zatayi.
Bayan ya huta sosai abu d'aya yake da buk'ata yayi wato bacci, amma ina ya kasa samuwa duk da cewar baiyi bacci daren jiya ba, wayarshi ya d'auka yana so ya kira Ummi amma yana tuna ya fad'i bazai k'ara kiranta ba, haka ya daure ya kirata amma abun haushin wayar kashe, haka ya k'urama pic d'inta ido yana kallo har bacci b'arawo ya d'aukeshi.
*Washe gari* da safe Ummi ce ta fito farfajiyar gidan dan tasha iska, sanye take da doguwar riga mai colour ja da bak'i da fari, sama a matse sai k'asa daya bud'e ba tada dan kwalli dan haka ta d'ora na abaya ba'ka, zaune tayi akan 'yar gajerar katangar da aka kewaye rabin harabar gidan da ita, jingina bayanta tayi ta rumgume hannayenta a k'irji tayi shiru tana kallon 'yar k'aramar bishiyar mangaro, a hankali ta tuna ranar da suka fito tare da Salman ta rakoshi zai fita, da kuma ranar da ta fad'i saboda jiri ya d'auketa sannan ya kawo mata madara tasha.
Rayuwarsu take tunani tana murmushi ajiyar zuciya ta sauke tana mai k'ara fad'ad'a murmushinta tace "ina ma kadawo yau, da zan zauna da kai ko dukana ne kaci gaba dayi da wannan tattausan hannun naka"
Jawahir dake zaune gefe ita da Khamis ta kalleshi tace "mijina dubi mutuniyar murmushi take ita kad'ai, ina ga fa tunanin yaya Mane take"
Dariya suka saka gaba d'ayansu hakan ya janyo hankalinta, mamakine ya bayyana a fuskarta dan batayi tunanin suna nanba suma, saidai kallonsu kawai take saboda ganin k'afar Khamis a cinyar Jawahir tana masa wankin k'afa, take ta tuna da ranar da tama Salman yankan akaifu, wani murmushin ta koma saki tare da jin wani sanyi na lullub'eta, gaba d'aya taji kawai tana son ganin Salman ko fad'ane ma su dinga yi zata ji dad'i.
Jawahir ce data lura ba tada niyyar magana tace "Hajia Abu tunanin me ake ne haka?" kallonta Ummi tayi tace "ba komai"
Tab'e baki tayi tace "to naji ba komai, amma ya kamata ki shirya gobe muje muyi kitso" cikin farin ciki tace "yawwa dama nima ina so nayi kitso"
Cewa tayi "amma ai da kin bari har yaya Salman zai dawo sai kiyi" hararanta kawai tayi ba tace komai ba, Khamis kam cewa yayi "to nidai kamar kullum ne, indai har kina so kije to ki tabbatar kin kira mijinki kin fad'a masa."
Ba tada zab'in daya wuce ta kira ta fad'a masa dan haka tace "to yaya Khamis zan kira, na lura kaidai kana jin tsoron mutuminan sosai"
Hararan ta yayi yace "ke kuma baki tsoronsa ko jaruma?" dariya kawai tayi ba tace komai ba.
Ummi bata kira Salman ba saida safe sannan ta d'auki wayar ta kuna, ta danna numbershi tana fara k'ara taji gabanta ya fara dukan uku-uku, da k'yar ta iya daurewa tana sauraran ya d'aga.
Tana jin ya d'aga taji cikinta ya d'uri ruwa take taji tana buk'atar kewayawa, amma haka ta dake ba tare da tace komai ba, Salman dake saman hanyar dawowa yana ganin kiranta yaji farin ciki ya mamayeshi, ba tare daya kula ba ya samu kansa yana mai kasaitancen murmushi amma daya tuna wacece Ummi da kuma kashe wayar da tayi, kawai sai ya b'ata rai sannan ya d'aga.
"Oui je t'ecoute" ( na'am ina jinki) ya fad'a a tak'aice, cikin sanyanyen murya tace "haba ba ko sallama?"
Cikin dakakkiyar murya yace "ki fad'i abinda yasa kika kirani da gaggawa inada abinyi?" tab'e baki tayi tace "dama na kira ne dan na fad'a maka za muje wajen kitso nida Jawahir yanzu, kuma yaya khamis yace dole saina fad'ama